Monday 4 February 2013

Alamomin Bayyanan Imam Mahdi[AF] da kuma Ladubban Zamanin Gaiba.


Alamomin bayyanar Imam Al-mahdi [AF] za’a iya kasa su kashi uku.Na farko akwai alamomin da zasu gudana kafin bayyanarsa,Na biyu akwai abubuwan da zasu gudana  gaf da bayyanarsa,misali shekarar da zai bayyana.Na ukku akwai alamomin da zasu gudana lokacin da ya bayyana.Kuma duk bayanan wa]annan alamomin sun gangaro ne daga Manzon Allah [S] da kuma A’imma na Ahlul-bayt [AS].
Saboda haka da mutum zai bibiyi littafan Hadisai na wa]annan makarantu guda biyu,wato na madrasah ]in shi’a,da kuma madrasah ]in sunna,zai ci karo da Hadisan da suke bayani dangane da alamomin bayyanar Imam Al-mahdi [AF].                                                                                                                                                                  Har ila yau kuma da mutum zai bibiyi littafan tarihi,musamman littafan da malaman imamiyyah suka rubuta,zai ga cewa a tarihin Imam Mahdi [AF] galibi sukan kawo alamomin bayyanarsa.kyakkyawan misali anan shine littafan tarihi na Muntahal A’mal na shaikh Abbas Al-}ummiy. Littafin A’immatuna da kuma littafin Siratu Rasul wa Ahlulbayt [AS];dukkan wa]annan littafan guda uku,a juzu’insu na biyu,malaman da suka rubuta su, sun fitar da fasali ko babi da ke bayanin alamomin bayyanar Imam Mahdi [AS].                                                                                                                                                                                                        Baya ga haka ma akwai malamai na wa]annan makarantu guda biyu da suka rubuta littafai khususan kan alamomin bayyanar, Imam Mahdi [AS] Misali anan shine wanda shaikh Usman [an Fodio ya rubuta mai suna “ Alamatu Khurujul Mahdi”.Akwai kuma wanda ]ansa shaikh Ahmad Rufai ya rubuta mai wannan taken.Saboda haka anan insha Allah za’a kawo bayanin wa]annan alamomin a ta}aice akan tar-tibin da aka ambata a sama,wato  guda uku.                                                                                                                                              Na farko,alamomin da zasu gudana kafin bayyanarsa,Akwai alamomi da dama,amma anan za’a kawo guda 10 domin gudun tsawaitawa.                                                                                              
1.Yawaitar zalunci da kuma danniya a duniya,kamar yadda yazo daga Imam Ba}ir [AS] yace, “Imam Mahdi [AS] ba zai bayyana ba har sai zalunci ya kai tsororowarsa”. A kuma wani hadisi wanda aka samo daga Manzon Allah [S] yace, “ko da duniya ta kasance saura yini ]aya ne,to Allah [T] zai tsawaita yinin domin Mahdi, ya cika ta da adalci kamar yadda aka ci kata da zalunci da kuma danniya”.Wanda wannan bayyane yake a wannan zamanin,wato yadda zalunci da kuma danniya suka cika duniya.                                                                  2.Yawai tuwar kashe-kashe da mutuwa da kuma musibobi a bayan }asa.An samo daga Imam Aliy[AS] yace, “Mahdi ba zai bayyana ba har sai an kashe ]aya bisa uku na mutanen duniya”.wannan magana ta Imam Aliy [AS] tazo acikin littafin nan mai suna Al-burhan fi Alamati Mahdi  Akhiraz-zaman,wanda malami ne na Ahlus Sunna ya rubuta,Wannan shima a bayyane yake a wannan zamanin.Mu duba yadda kashe-kashe ya yawaita a bayan }asa da mace-mace na fuj’a da musibobi na ambaliya,girgizar }asa,da dai sauransu.                                                                                                                                                        
3.Yawaitar fasadi da kuma sa~o a bayan }asa.Mu duba yadda ~arna da sa~on Allah[T] suka yawaita a duniya,wa]ansu ma sun mai da fasadi da Zunubi a matsayin ado da kuma sana’a.                      
4.Ci gaban ilimin kimiyya da kuma fasaha.Wannan shima a bayyane yake a wannan zamanin,mu duba yadda ilimin kimiyya da fasaha ya kai matsayi mai girma,kuma kullum ci gaba ake samu a wannan fagen,wanda in mutum ya duba wasu zantuka na Aimma na Ahlulbayt [AS] da suka fa]a wa mabiyansu dangane da ilimin kimiyya da fasaha a wancan lokacin,da yawansu zai yi masu wahalan fahimta,amma mutumin wannan zamanin zai ga abin a bayyane.ga misali guda biyu, acikin littafin hadisi na Al-kafi akwai hadisi da aka samu daga Imam sadi} [AS],wanda abinda hadisin ya }unsa shine cewa idan Imam Mahdi [AS] ya bayyana zai kasance yana magana a waje ]aya ne,amma sauran mutane na sassan duniya daban-daban zai kasance suna jinsa kuma suna ganinsa,alhali kuma yana waje ]aya ne,[misali a ce yana Makka yana jawabi,amma mutanen dake Iran,yaman,misra,madina da dai sauran sassan duniya, a lokaci guda suna kallonsa,kuma suna jinsa],fahimtar haka a wancan lokacin tana da wahala,amma ga mutumin wannan zamanin mai sau}i ne,mutum yana magana a talabijin a waje ]aya na duniya,amma sauran mutane na sassan duniya daban-daban suna kallonsa,kuma suna jinsa.                                                                                       Har ila yau kuma a wani hadisi da aka samo daga Imam sadi} [AS] yana cewa, “Mumini a zamanin }a’im[wato Imam Mahdi [AF] yana gabashin duniya,zai kasance yana ganin ]an uwansa da yake yammacin duniya.Haka kuma wanda yake yammacin duniya zai kasance yana ganin wanda yake gabashin duniya;.Wanda wannan dai yana nuni ne da irin ci gaban da ilimin kimiyya da fasaha zai kai.
5.Ta~ar~arewar tattalin arziki na duniya da kuma tsadar kayayyaki.shima wannan yana daga cikin alamomin bayyanar Imam Mahdi [AF],kamar yadda yazo a littafai.Wanda shima wannan bayyane yake a wannan zamanin.Mu dubi yadda tattalin arzikin duniya, yake ta ta~ar~arewa da kuma yadda tsadar kayayyaki suke a yanzu a kasuwannin duniya.Wanda wannan kawai ya isa ya nuna mana matsayin da A’imma na Ahlulbayt [AS] suke dashi,wanda kuma dama sune wa]anda Manzon Allah [S] ya bar ma wannan al’ummar da su yi ri}o dasu a bayansa.Zantukan da suka fa]i a zamaninsu, sama da shekaru dubu da wani abu da suka wuce,amma yau gashi suna gudana a aikace a wannan zamanin namu.                             
6.Nisantar koyarwar addinin musulunci da kuma }e}ashewar zukata,shima wannan bayyane yake a wannan zamanin.Mu dubi yadda addini ya zama ba}o,haka nan ma wanda ya siffanta dashi.har ma  suka }e}ashe,idanuwa suka bushe.                                                                                           
7.Yawaitar rarraba da kuma sa~ani tsakanin musulmi da kuma samuwar sa~ani da rarraba tsakanin mabiya Ahlul Baiti [AS].shima wannan yana daga cikin alamomin bayyanarsa.Kamar yadda yazo a wasu hadisai daga Ma’asumai [AS].Mai bu}atar ganin wa]annan hadisai yana iya duba littafi mai suna “Imam Al-mahdi- fil Ahadis- mush-taraka –Bainas- Sunna was-shi’a”.ko kuma littafin muntahal Amal,juzu’I na biyu na shaikh Abbas Al-}ummy,wato mawallafin littafin mafatihul jinan.                    
8.Yawaitar bayyanar ayoyi daban-daban a halittun Allah[T].shima wannan a bayyane yake a wannan zamanin,musamman ma a ‘yan shekarunnan,sai ka ga an samu wani ganye ko itaciya ko wuri ko kuma wani abu dai da sunan Allah [T] a jiki,ko sunan Manzon Allah [S],ko wata aya ta Al-}ur’ani mai girma,ko kuma abinda yayi kama da haka,duk wa]annan suna daga cikin alamomin bayyanarsa [AF].
9.Samun yun}urin neman sauyi da kuma gwagwarmaya a sassan duniya daban-daban.Shima wannan a bayyane yake awannan zamanin,mutum ya duba musamman a }asashen musulmi,zai ga cewa akwai yun}uri da kuma gwagwarmaya ta neman sauyi,wanda ire-iren wa]annan yun}uri da kuma gwagwarmayar kamar shinfi]a ce ga zuwan Imam Mahdi [AS] kamar yadda bayanai suka zo a littafai.Akwai ma wa]anda har ha}arsu ta neman sauyi da gwagwarmaya ta cimma ruwa.Misali,kafuwar jamhuriyar musulunci ta iran.                                                                                                                          
10.Ya]uwar ilimin Ahlulbayt [AS] a bayan }asa.shima wannan bayyane yake a wannan zamanin,mutum ya dubi yadda wilaya da ilimin Ahlulbayt [AS] suke ta ya]uwa a sassan duniya daban-daban,in ma mutum bai san wani waje ba,to ya duba nan in da yake,wannan ma yana daga cikin alamomin bayyanarsa kamar yadda yazo,da dai sauran alamomin wa]anda ba za’a iya kawo su ba saboda gudun tsawaitawa.                                   Sai kuma kashi na biyu wato alamomin da zasu guda na gaf da bayyanarsa.Saboda gudun tsawaitawa za’a kawo guda biyar:                                                                                                  1.Bayyanar Dajjal:Yazo akan cewa dajjal zai kasance gaf da bayyanarsa.Bayannan shi dajjal ]in da irin ~arna da kuma ta’asar da zai yi mutum sai ya koma a littafai,musamman na hadisai domin samun bayanai akai.in mutum ya bincika zai ga akwai adduo’in da aka samo daga Manzon Allah  da kuma Ahlulbayt  daban-daban na neman tsari daga sharrin shi Dajjalda kuma fitinarsa.                                      2.khusufin rana a tsakiyan watan ramadan da kuma }arshen watan ramadan ]in,wato sa~anin yadda ya saba gudana na cewa khusufin wata,ya kan kasance a tsakiyar wata, na rana kuma }arshen wata.Akan wannan ma akwai hadisi da yazo daga Imam Ba}ir [AS] yace, “Ayoyi guda biyu zasu kasance gabanin tsayawar }a’im,wa]anda basu ta~a kasancewa a doron }asa ba.sune khusufin rana a tsakiyar watan ramadan,da kuma khusufin wata }arshensa.                                                                                                                      3.Kashe Nafsuz-zakiyyah:yana daga cikin jikokin Manzon Allah [S],za’a kashe shi a makka ne tsakanin ruknu da ma}amu Ibrahim [AS],sunansa shine muhammad ibn Hassan,ya mazo a hadisi cewa tsakanin kashe shi da kuma bayyanar Imam Mahdi [AF] kwana 15 ne.                                                                                     4.Jin kira daga sama,hadisai da dama sunzo da bayani akan haka,cewa gaf da Imam Mahdi [AF] zai bayyana,a daren 23 a watan ramadan, za’ayi kira da sauti daga sama,wanda yazo akan cewa duk wanda yake doron }asa ko’ina yake zai ji wannan kira,abinda kiran yake cewa shine; “yaku taron halitta!Ga Mahdi na Ahlulbaitin Muhammad, kuyi masa bai’a,ku shirya,kada ku sa~a wa al’amarinsa ku ~ace!”.                                                                                                                                                                                                                        5.Bayyanar tafin hannu a sama,A wata ruwaya fuska da }irji da kuma tafin hannu zasu bayyana a tsakiyar }wallon rana.wannan kenan a ta}aice.                                                                                                                                  Sai kuma alamominsa da zasu kasance a lokacin daya bayyana; shima saboda gudun tsawaitawa za a kawo guda uku:                                                                                                                                                    
1.Yazo akan cewa zai bayyana a makka,ranar Ashura wato ranar shahadar Imam Husain [AS],duk da akwai ruwayoyi dabam dabam kan wannan al’amari.Haka nan yazo akan cewa zai bayyana ranar jumma’ce,a wani zan ce kuma ranar Asabar.Haka nan  kuma shekarar da zai bayyana zata kasance  akan witri,wato ko dai shekarar ta kasance da1,Ko da3,ko da5,ko da7,ko da 9.wannan shima yazo a hadisi,gamai bu}atar ganin wa]annan hadisai da suka zo da wannan,yana iya duba littafi mai suna,Mun takhabul- asri fil- Imamis-sani- Ashra’’ na Ayyatullahi Golfeganiy.
Sai dai tambihi a nan kada mutum ya samu ish-kal a nan cewa hadisai ba sun ayyana lokaci ba ne, wato  ba su yi karo da hadisan da suka zo na ayyana lokacin bayyanar Imam Mahadi (AF) ba, domin wace Ashura ce ba a ayyana ba, wace juma’a ce ko asabar, ba a ayyana ba. Haka nan wace ta 1, 3, 5, 7, 9, ba a bayyana ba. A ita ruwayar da ta zo cewa zai bayyana a makkah, yazo akan idan ya bayyana ]in, farkon abun da zai fara furuci da shi, shi ne wannan ayar ‘Ba}iyyatullahi khairun-lakum in kuntum muminin`.
2. Ha]uwar mataimakansa su 313 a lokaci guda, wato za su ha]u, za su kuma kasance ne daga sassan duniya daban-daban, amma kuma bisa ikon Allah (T) yana bayyana wa]annan matamaika nasa 313, za su ha]u tare da shi. Kamar yadda Allah (T) ya ke fa]i a cikin al-kur’ani mai girma “Duk inda kuke Allah zai zo da ku baki ]aya, kuma Allah mai iko ne akan komai.
3. Saukar Annabi Isah (AS). Shi ma wannan zai kasance idan ya bayyana. Kuma hadisai na shi’a da sunna sun zo da bayani akan haka. Wannan ke nan baki daya a ta}aice dangane da alamomin bayyanar Imam Mahdi (AF).
Sai kuma abin da ya shafi ladubban gaiba, wato fakuwarsa. Da yake zamuna a wannan al’umman sun kasu kashi hu]u, wato wa]anda suke da ala}a da Ma’asumin (AS) na farko akwai asrun-nubbuwa, wato zamanin da Manzon Allah (S) yake a raye. Na biyu akwai asrul-Imama, wato zamanin da Imaman Ahlul bait  12  suke raye. Na uku, asrul-gaiba, wato zamanin da Imam Mahadi (AF) ya ke ba a bayyane ba. Shine wannan zamanin da muke a ciki, na hu]u. Akwai asruz-zuhur, wato zamanin da Imam Mahdi (AF) ya ke a bayyane.
To wannan zamani da muke ciki, wato zamanin gaiba, akwai wasu ladubba da ake son ko wane mutum mace da namiji musamman ma mabiya ahlul baiti (AS) da su lizimta, wato ta hanyar aikata wa]annan ladubban da siffantuwa da su. A kan haka ne malamai da dama a madarasah ]in ahlul baiti (AS) sun yi wallafe wallafe na littafai da suke bayanin wa]annan ladubban, da ake son lizimtar su a zamanin gaiba. Alal misali akwai littafi mai suna “adabu asril gaiba”, na sheikh Hussain  khoraniy  da kuma littafi mai suna “wazifatul –anami- fi- zamani- gaibatil- Imam (AS), na Ayatullahi Mirza Muhammad At-ta}iy al-musawiy, wanda wa]annan littafai guda biyu babu komai a cikin su, face bayanan wa]annan ladubba. Amma saboda gudun tsawaitawa za a kawo 17 daga cikin su.
1.       SANINSA: Wato mutum ya san Imam Mahadi (AF) sani a dun}ule ko a war-ware. Wato ya san shi ta fuskoki daban-daban. Misali sani ta fuskacin matsayin sa,nasabar sa, shaksiyyar sa, wiladar sa, gaiba ]in sa, zuhur ]in sa, da dai sauran su. Akwai ma hadisai da suka zo suna nuni ga muhinmancin kowane musulmi ya san Imamin zamanin sa. Alal misali akwai hadisin da ya zo a cikin littafi mai suna « kamaluddin wa tamamun ni’ima » na shaikh sadu}, yana cewa “Duk wanda ya mutu amma bai san Imam ]in zamaninsa ba, to yayi mutuwar jahiliyya”. Har ila yau wani hadisi wanda shaikh [usi ya ruwaito a littafin sa mai suna ‘gaiba` hadisin yana cewa «  wanda ya san Imamin sa, sannan ya mutu gabanin bayyanarsa, to yana da lada kamar wanda ya kasance tare da shi lokacin bayyanar sa ».
2.       ADDU’A: Na farko wadda ake yiwa Imam Mahadi (AF), akwai wadda aka ruwaito daga Imam Ridah (AS) ya yi umarni da a karanta wa Imam Mahdi (AF). Ga mai bu}ata yana iya duba mafatihul jinan, tana kusa da dua’un nudba. Akwai kuma wata addu’an da ake son, adun ga karantawa bayan kowace sallah. Addu’ar  tana farawa ne da “Allahumma- Kun-liwaliyyika - hujjatu bin Hassan………”. Da kuma yawaita addu’ar , Allah ya gaggauta bayyanarsa. Domin ya zo akan cewa bayin Allah da dama da suka sadu da shi, cikin abun da yake ce masu shine,Su yawaita addu’ar  Allah ya gaggauta bayyanarsa. Na biyu :daga cikin addu’ar da ake son mutum ya  yawaita  biyata. Akwai addu’a wadda aka samo daga Imam Sadi} (AS) ana son ya biyata, da lizimtar ta a zamanin  gaiba itace, “YA ALLAH YA RAHMAN YA RAHEEM YA MU{ALLIBUL {ULUB SABBIT {ALBIY ALA DINIK” Ana cema wannan addu’ar du’a’ul gari}. Akwai kuma wata addu’a wadda itama ana son lizamtar tana soma wa da “Allahumma  arrifni naf.                         
3.       3. YIN ZIYARA GARE SHI:Shaikh kaf’ami yace a  cikin littafinsa mai suna  baladul Amin,mustahabbi ne ziyartar Imam Mahdi[AF] a kowane waje a kuma kowane lokaci.kuma ziyarar tasa tazo da sigogi dabam dabam.A}alla Akwai ziyara da ake yi gare shi ta ranar juma’a, yana da kyau mutum ya lizimce ta.Ga mai bu}atar ganin wa]annan ziyarori yana iya duba littafin mafatihu,babi na ]aya,fasali na biyar,da kuma babi na ukku,fasali na goma.
4.GIRMAMASHI: Tashi tsaye domin girmamawa gare shi,lokacin da mutum yaji an an baci la}abinsa na Al}a’im.  kuma wannan abu ya samo asali ne daga A’imma na Ahlul baiti [AS], misali yazo akan cewa Imam Sadi} [AS] ya kasance a wani majalisi sai aka ambaci wannan lakabin,  sai aka gan shi ya mi}e tsaye, kuma  an samo makamancin hakan daga Imam Ridah [AS] yana zaune da aka ambaci  wannan la}abin  sai aka ga ya Tashi tsaye ya ]an sun kuyar da kansa mai albarka ya kuma ]ora hannun daman sa a kansa yace, “Allah ka gaggauta bayyanarsa”.
5.YIN BAI’A GARE SHI:Mustahabbi ne kamar yadda yazo yin bai’a ga Imam Mahdi [AS] ko wace rana,ko mako musamman ran juma’a, ko wata,ko  shekara.Sigar bai’a ]in itace kamar yadda yazo a addu’a wadda ake cewa, Du’a’ul Ahad ta nan cikin Mafatihu  gaban Du’a’ul Nudba.In son samu ne duk bayan sallar asuba mutum ya dun ga biya ta.
6.JIRANSA: Wato intizar,jira anan ba yana nufin mutum ya kame hannunsa bai yin komai a fagen addini ba.A’a zai zamanto da farko shi }ashin kansa ya siffanta da addini.Na biyu kuma ya zamanto yana bada gudummuwa a fagen addinin da irin bai war da Allah [T] yayi masa.Na uku ya zamo mutum  yana da ruhi na jihadi da kuma mujahada.Akwai hadisai masu yawa da suka zo da bayanan falalar intizar.Ga guda biyu daga ciki.An samo daga Imam Sadik [AS] yace, “Duk wanda ya rasu yana intizarin wannan al’amarin zai kasance kamar wanda yake a zamanin bayyanarsa.” An samo daga Manzon Allah [S] yana cewa, “Mafificin ayyukan al’ummata shine intizarin  far’j” wato bayyanar Imam Mahdi [AF].
7.SHAU{I GARE SHI:Wato mutum ya zamanto mai yawan begen Imam Mahdi [AS],mutum ya gina kansa a haka har ya kai matsayin da zai dunga kuka, saboda shau}insa gare shi.Lizimtar Du’a’ul Nudba zata taimaka wa mutum akan haka.Domin akwai fa}arori a cikin Addu’ar da suke gina mutum ga shau}insa.
8.NUNA DAMUWA GARE SHI:Damuwa da ba}in ciki na rashin ganinsa da kuma saduwa dashi.Shima wannan mutum ya gina kansa akan haka har ya kai matsayin da zai zubar da hawaye saboda haka.Wannan kuwa zai kasance ne idan mutum yana yawan tunanin Imam Mahdi [AS].
9.{ASKANTAR DA KAI GARE SHI:Wato mutum ya zamanto mai yawan girmama wa ga Imam Mahdi [AS] ya kuma kasance mai yawan {askantar da kai gare shi.Misalin da aka bayar abaya  na cewa Imam Sadi} [AS] da kuma Imam Ridah [AS] da aka ambaci la}abin na Al’}aim sai da suka mi}e tsaye saboda girmama shi.Akwai ma fa]in Imam Sadik [AS]  yana cewa, “Da ya riski Imam Mahdi [AS],to da yayi masa hidima tsawon rayuwar sa…..”.
10.YI MASA TA’AZIYYA GARE SHI:Yi masa ta’aziyya da kuma taya shi murna duk lokacin wafatin [rasuwar] ko wiladar [haihuwar] wani daga cikin Ma’asumai ta zaga yo,wato Manzon Allah [S] da kuma Ahlulbaiti [AS].Misali ace yau ranar wafatin Imam Ali ce,to sai kayi masa ta’aziyya a wannan ranar,ko kuma ace yau ranar wiladar Imam Ali ce to sai ka taya shi murna a ranar,ta hanyar yi masa sallama sai ka mika ta’aziyyar ka ko murnan ka.
11.RASHIN AMBATON SUNANSA:An yi hani ga ambaton sunansa, sai dai ambaton sa da la}ubbansa kamar Mahdi,Sahibuz zaman,Muntazar da dai makamantansu.Kuma kamar yadda muka sani sunan sa,yayi muwafa}a da na Manzon Allah [S] ne.
12.SANIN ALAMOMIN BAYYANARSA:Muhimmancin haka kamar yadda Malamai suka yi bayani shine:                                     i.Tsare kai daga fa]awa tarkon masu i}i-rarin Mahadawiyya.Domin in mutum ya bibiyi tarihin wannan al’umma,zai ga an samu wa]anda sukayi iki-rarin cewa sune Mahdi.Misali,wanda aka yi a Sudan shekaru 50 bayan rasuwar Sheikh [an Fodio.                                                                                                                  ii.Shiga cikin rundunar sa.Ga wanda Allah yayi wa muwafa]a,yana raye ya bayyana.Wato kasantuwar ya san alamomin bayyanarsa cikin sau}i zai iya gane shine ko bashi bane.
13.TAWASSULI DA KUMA ISTIGASA DA SHI:Mutum ya dunga yin tawassuli dashi  ga dukkan al’amuransa na  duniya da na addini da kuma na lahira .Yana da kyau mutum ya saba wa kansa da haka.Domin yin haka zai taimaka wajen samun ala}a }albiyyah [wato damfaruwa da shi a zuciya] 
14.HADDIYA GARE SHI:Wato mutum yayi wani aiki na ibada ko ]a’a da nufin Allah [T] ya kai ladar ga Imam Mahdi [AF] shima wannan ya nada kyau mutum ya saba da shi.
15.TSAYAWA DA BADA HU{U{-MALIYYA:Ga wanda ya kai matsayin ya bayar,misali khumusi da makamantansu,domin kamar yadda aka sani a cikin khumusi, akwai abinda ake cewa Sahmul-Imam [AS] da kuma Sahmus Sadat,wannan bayaninsu sai a koma Risala Amaliyyah.
16.TA{ALIDI DA [AYA DAGA CIKIN NUWWAB [INSA NA AMMA:A FAGEH FI{IHU. wannan wajibi ne ba ma mustahabbi ba.Kamar yadda yazo akan cewa idan mutum shi ba mujtahidi bane ko muhta]i ba,to, dole  ne ya samu wani daga cikin mujtahidai, domin yayi Ta}lid da shi ga ayyukansa na ibadat da kuma mu’amalat.Wannan shi ma sai a koma ga Risala Amaliyyah domin }arin bayani.
17.RAYA AL’AMURUNSA TSAKANIN MUTANE:Wannan shi ma ta fuskoki daban daban,misali kiyaye ranar haihuwarsa ,yin tarurruka domin }ara wa juna ilimi dangane da shi,yin rubuce-rubuce dangane da shi da dai sauransu.Ya ma zo daga Imam Sadi} [AS] yace Allah Ta’ala yayi rahama ga wanda ya rayar da al’amarinmu.A wani hadisi kuma yace, “Allah Ta’ala yayi rahama ga bawan da ya sanya sonmu a zukatan  mutane”.                                                                                                                                                  Wannan kenan baki ]aya a ta}aice da fatan Allah [T] ya amfanar da mu abubuwan da muka karanta ya kuma bamu ikon aiki da su.   

No comments:

Post a Comment