Alhamdulillah, kasantuwar wannan wata da muke ciki, wato
na Zulhijjah cikinsa ne 18 gare shi wato Ranar Ghadir Manzon Allah (S) ya
bayyana wa wannan al’umma wa]anda za su kasance Imamai, wato Khalifofi a
bayansa, bayyanawa wadda za a siffata ta a matsayin bayyanawa RASMIYYAN, wato
OFFICIALY. Saboda haka mabiya Ahlul Baiti (AS) a sassan duniya daban-daban suke
gabatar da tarurruka da kuma rubuce-rubuce domin tunatar da juna dangane da
wannan rana ta Ghadir.
Ko kuma abubuwan da suka faru kafin ranar Ghadir da kuma
ranar da abin da ya biyo bayan ranar. Ko kuma tunatar da juna dangane da
ayyukan da ake aikatawa a ranar Ghadir ]in da dai sauran mas’aloli da suke da
ala}a da wannan ranar ta Ghadir, kamar al’amarin Imamanci.
A kan wannan asasin ne rubutun zai
gudana insha Allah, wato Imama a mahangar Madrasa ]in Ahlul Bait (AS) da kuma
Madrasa ]in Ahlus Sunna. Domin Mas’ala na Imamanci ko Khalifanci shi ne asasul-asas
na sa~ani tsakanin Shi’a da Sunnah. Wato duk wani sa~ani da kuma rarraba da ya
auku a wannan al’umma ta Manzon Allah (S) ya gangaro ne daga wannan asalin.
Haka nan kuma duk wani musgunawa
da cutarwa da aka yi wa Ahlul Baiti (AS) da kuma mabiyansu na kisa na ]auri,
kora daga }asa zubar da jininsu, ~arnatar da dukiyoyinsu, wannan shi ne sabab.
Hatta cutarwa ta farko da aka soma
yi wa Ahlul Baiti (AS) da kuma mabiyansu bayan wafatin Manzon Allah (S) kan dai
wannan al’amari ne. Mutum ya karanci tarihi na wa]annan makarantu guda biyu zai
ga haka na abubuwan da suka faru a Sa}ifa da kuma abin da ya biyo bayan nan na
kai hujumi gidan Sayyida Fatima(AS) da nufin cewa Imam Ali (AS) da wa]anda suke
tare da shi a gidan dole su fito su yi bai’a. Abubuwan da suka faru a gidan
mutum ya tambayi tarihi, me ya faru a gidan ya gani.
Bayan haka Imaman nan ]aya bayan
]aya baki ]ayansu, babu wanda ba a cutar da shi ba kan wannan al’amari. Mu duba inda aka haife su da kuma inda suka rasu. Idan
mutum ya bibiyi tarihin A’imma (AS) 12 zai ga in ka ]ebe Imam Ali (AS) da aka
haifa a Makka da kuma Imam Mahdi(AF) da aka haifa a Samarra da ke }asar Ira}i,
to sauran iImamai 10 duka a Madina aka haife su, ko kuma kusa da Madina kamar
Imam Kazim (AS) da aka haifa a wani waje mai suna Abwa kusa da Madina. Amma mu
duba mu gani mafi yawan wa]annan Imaman }aburburansu na Madina ne, ko kuma nesa
da Madina? Wannan ka]ai ya isa ya nuna wa mutum cewa lallai wasu al’amura sun
faru da ya kai ga faruwar haka.
Kuma
mu duba inda aka haifi Imam Mahdi (AS) a waje ne nesa da Makka da kuma Madina.
Dalilin haka kuwa kamar yadda ya zo a tarihi shi ne; masu tafi da iko a lokacin
suna da masaniyar cewa Imam Hasan Al-Askari shi ne Imami na 11, kuma shi zai
haifi Imami na 12, wanda zai kau da zalunci da kuma azzalumai, ya shimfi]a
adalci a bayan }asa baki ]aya. A kan asasin haka ne aka ]auko shi daga Madina
zuwa Ira}i aka aje shi a Samarra a wani sansani na maya}a (barikin soja). Daga
nan ne wannan la}abi nasa ya samo asali.
Ba su
tsaya nan ba, Khalifan Abbasawa na lokacin ya sa aka samu mata wa]anda suka
}ware wajen sanin cikin ’ya mace ya sa su lokaci bayan lokaci su dinga bibiyar
iyalin Imam Askari (AS) su ga wacce ce take da ciki a shaida masa. Amma ta
Allah ba tasu ba, a irin wannan yanayi ne aka haifi Imam Mahdi (AS). Allah (T)
ya kare shi har ya shekara biyar kafin rasuwar Mahaifinsa da dai sauran abubuwa
masu yawa da suka faru marasa kyau ga Ahlul Baiti (AS) da kuma mabiyansu,
saboda al’amarin Imama ko Khalifanci. Wannan kenan dai a ta}aice.
Dangane
da Imama a mahangar Ahlul Baiti (S) da kuma Ahlul Sunnah, a dun}ule wannan
mahanga ]in guda biyar ne, kamr yadda suka zo a littafin A}a’id sune:
1. Imama, Usulul-Deen ce ko Furu’ud-deen?
2. Imama, Nassi ce ko shura?
3. Dawamul-Imama
4. Mas’uliyyar Imam.
5. Shuru] na Imam.
Ga
mahangar kowanne ga wa]annan abubuwan guda biyar da aka ambata.
Na ]aya
Imama Usul ce ko Furu’u? Shi’a sun tafi a kan cewa Imama tana cikin Usuld-din
ne, shi ya sa in mutum ya duba littafi na A}ida na Madrasa ]in Ahlul Baiti (AS)
zai ga bayan bayani kan Nubuwa, abin da yake biyowa baya mubasharatan shi ne
bayani dangane da Imama.
Su kuma Ahlus Sunna suka tafi a kan
cewa Imama tana cikin Furu’ud-din ne, wato Fi}hu. Ga zantukan wasu daga cikin
Malaman Ahlus sunna a kai. Gazzali ya ce “Mas’alar Imama ba ya cikin A}a’id,
yana cikin Fi}hu ne”. Wani Malami mai suna
Amudi ya ce; “Ka sani bayani dangane da Imama ba ya cikin Usulud-din”. Haka nan
wani Malami ya ce; “Bahasin Imama a wurinmu yana cikin Furu’ud-din ne”. Ibn
Kaldun ya ce; “Al’amarin Imama mas’ala ce ijtima’iyya bai cancanci ya zama
cikin babin A}ida ba”. Wani kuma Malami mai suna Taf-tazani ya ce; “Babu
jayayya a kan cewa mas’alar Imama ya fi dacewa da ilimin Furu’ud-din”. Da dai
sauran zantuka na Malaman Ahlus Sunnah dangane da haka.
Na
biyu: Imama nassice ko Shura, wato ayyanawa ne daga wajen Allah (T), ko ko an
bar wa mutane su tattauna tsakaninsu su za~a? Shi’a suka tafi a kan cewa
al’amarin Imama Nassice daga wajen Allah
(T), wato kamar yadda Allah (T) shi ya za~i Annabawa, to, haka nan Imamai shi
ya za~e su. Kamar yadda babu wani Annabi daga cikin Annabawa da mutanen
zamaninsa suka tattaru suka za~e shi, sannan suka ce sun mai da shi Annabi. To haka
nan al’amarin Imama yake a Madrasa ]in Ahlul Bait(AS). Ba mutane ne suke ha]uwa su za~i Imam ba, (amma nan a lura, Imam nan ana
nufin da ma’anarsa ta Is]ilahi ba ta lugga ba. Wato ana nufin Khalifa na Manzon
Allah (S)). Saboda haka Shi’a suka tafi a kan cewa, Manzon Allah (S) kafin ya
bar duniya ya bayyana wa]anda za su kasance Khalifofi a bayansa. Ya bayyana a
dadinsu, wato su 12 ne, ya kuma bayyana sunayensu, na farkon su shi ne Imam Ali
(AS), na }arshensu shi ne Imam Mahdi (AS). Ya bayyana haka RASMIYYAN a ranar
Ghadir da kuma wasu munasabobi a tarihin rayuwarsa, ta hanyar ishara, ko kuma
kai tsaye, kamar yadda ya auku tun farkon da’awarsa wato a Makka a muhadarar da
aka fi sani da Yaumud Dar.
Su
kuma Ahlus Sunni suka tafi a kan cewa a’a, Manzon Allah (S) ya bar duniya ne ba
tare da ya bayyana Khalifa ba. Alal misali, mutum na iya duba littafin Tarikhul
Khulafah na Suyu]i, ya duba fasali na farko a littafin , zai ga yana bayani ne
a kan cewa; “Manzon Allah (S) bai khalifantar da wani ba, da kuma sirrin
hakan”.
To
amma da mutum zai ]ebe ta’asubanci da kuma tunanin abin da ya gada, wato abin
da ya taso a kai, kuma ya bu]i ido a kai, ya yi bincike kan hujjojin wa]annan
~angarori na Musulmi guda biyu (watau Shi’a da Sunna), bayan ya gama binciken
sai ya zo ya yi mu}arana, wato ya kwatanta hujjojin ya gani, na wa ya fi }arfi,
kuma abin rinjayarwa? Sai ya yanke wa kansa hukunci.
A bisa
gaskiya in da mutum zai yi wannan bincike, daga }arshe zai ga cewa hujjojin da
Shi’a suka kawo kan wannan al’amarin hujjojin ne masu }arfi wa]anda kuma za su
iya tabbatar da wa]annan hujjoji ba wai a littafansu kawai ba, a’a, hatta ma a
littafan Ahlus Sunnah.
Misali
guda ]aya a nan shi ne abin da su Shi’a suka tafi a kai na cewa Khalifofin
Manzon Allah su 12 ne, wannan yana nan a littafan Hadisai na Ahlus Sunna, wato
Bukhari, Muslim Nisa’i, Tirmizi da kuma Musnad na Ahmad, wato Shugaban Mazhaban
Hanbaliyya. Duka
sun fitar da wannan Hadisin, wato wanda yake bayani da kuma nuni ga Khalifofi 12.
Nassin Hadisin shi ne; Manzon Allah (S) ya ce: “Alkhulafa’u min ba’adi isna
Ashr”. Wato Khalifofi a bayana 12 ne. Abin tambaya a nan su waye wa]annan sha biyun?
Zai yi kyau mutum ya samu littafin da aka ambata a baya wato Tarikhul Khulafah
na Suyu]i ya ga yadda ya kawo zantukan fitattun Malaman Ahlus Sunnah dangane da
shi wannan Hadisin. A duba fasali na uku a littafin.
Daga }arshe in mutum ya duba zai
ga cewa, babu matsaya ]aya ko fahimta ]aya na Malaman Ahlus Sunnah kan wannan
Hadisin, kamar yadda Suyu]i ]in ya kawo a littafin. Ga bayanan da ya kawo na
wasu daga cikin fitattun Malamai na Ahlus Sunnah yadda su suka fahimci Hadisin
ga abin da yake cewa; “{hadi Iyad (watau wanda ya yi littafin Asshifa) ya ce }ila
abun da ake nufi da 12 a wa]annan hadisan da wa]anda suka yi kama da su, shi ne
wa]annan Khalifofi za su kasance a zamanin izzar Khalifanci da }arfin Musulunci
da kuma ijma’i akan wanda ya tsayu da khalifanci.
Ibn Hajar a sharhin Sahihul Bukhari ya }arfafa wannan magana ta Khadi Iyad,
inda yake cewa maganar Khadi Iyad, ita ce mafi kyawun abin da aka fa]i a wannan
Hadisi, kuma abin rinjayarwa”.
Ya ci gaba da cewa; “Abin da ake
nufi da ijma’i shi ne wanda mutane suka ha]u a bai’arsa. A ta}aice idan an fahimci
bayanin Khadi Iyad da kuma Ibn Hajar kan wannan Hadisin na Khaliffofi 12 cewa
ana nufin wa]anda mutane suka ha]u a bisa yarda da khalifancinsu ba wa]anda ba a
ha]u a kan khalifancinsu ba. Shi ne Ibn Hajar ya zano sunayensu kamar haka. 1.
Abubakar. 2. Umar. 3. Usman. 4. Ali. 5. Mu’awiyyah. 6. Yazid. 7. Abdulmalik. 8.
Walid. 9. Sulaiman. 10. Yazid (watau [an Abdulmalik). 11. Hisham. 12. Walid [an
yazid”.
A nan zai yi kayau mutum ya nemi
wannan littafi na Tarikhul Khulafa na Suyu]i ya karanci tarihi da kuma rayuwar
wa]annan da Ibn Hajar ya kawo a matsayin Khalifofi, ya samo daga Khalifa na shidda
wato Yazid [an Mu’awiyya zuwa na 12 wato Walid [an Yazid. In ba zai iya
karantawa duka ba, to a}alla ya karanta na shida da na 12. Bayan ya karanta ya
auna da hankalinsa. Anya kamar Yazid ko Walid su ne Khalifofin Manzon Allah
(S)? Wal’iyazubillah.
Ga wanda }ila ba zai iya samun
littafin domin ya karanta ba, ko kuma ba zai iya karantawa ba. To ga ka]an daga
cikin abubuwan da Suyu]i ya kawo a cikin littafin kan abin da ya shafi Yazid [an
Mu’awiyya. Ya soma banayanan nasa ne dangane da yadda aka yi ya zamo Khalifah
da abin da ya soma yi bayan da aka na]a shi, sannan ya kawo }issar wa}i’ar
Karbala da kuma kashe Imam Husain (AS), har yake cewa kisansa }isa ce mai tsawo,
wanda zuciya ba ta iya jurewa da ambaton }issar.
A nan sai ya kawo Inna Lillahi Wa
Inna Ilaihi Raji’un. Ya kuma kawo bayani dangane da canje-canjen da aka gani a
sama da kuma }asa da duwatsu da dai sauran halittu bayan kashe Imam Husain (AS).
Wannan ya faru ne a shekarar farko ta hawan Yazid.
A shekararsa ta biyu ya sa aka kai
hari Madina. An kashe mutane da dama. Daga ciki akwai ma Sahabban Manzon Allah (S),
aka kuma yi wa mata da yawan fya]e! Aka }wace dukiyoyi da kuma kayayyakin
mutane. A nan ma Suyu]i ya sake kawo Inna Lillahi Wa Inna Ilahi Raji’un. Har ma
ya kawo wani Hadisi wanda Musulim ya ruwaito cewa Manzon Allah (S) ya ce; “Duk
wanda ya tsoratar da mutanen Madina, Allah zai tsoratar da shi, kuma la’antar
Allah da Mala’ikunsa da kuma mutane baki ]aya ta tabbata a gare shi”. A takaice
wa]annan sojojin nasa sai da suka }wace Madina na tsawon kwanaku uku suna
wannan ta’asa.
A kuma shekararsa ta uku ya aika
da maya}a zuwa Makka domin ya}ar Abdullah [an Zubair, wanda haka ya yi
sanadiyyar }onewar Ka’aba da kuma muhimman abubuwan da ke kusa da ita. To fa
wannan shi ne Yazid [an Mu’awiyya a ta}aice kamar yadda Suyu]i ya kawo.
Akwai ma inda Suyu]in ya kawo cewa;
“Akwai wani da aka ce wa Naufal [an Abu Furat, ya ce na kasance wajen Umar [an
Abdul’aziz, sai wani mutum ya ambaci Yazid ya ce Amirul Muminin Yazid [an
Mu’awiya, ya ce sai Umar [an Abdul’aziz ya ce ka ce Amirul Muminin? Ya ba da
umurni a yi masa bulala 20”. Mutum ya duba cikin wannan littafin na Suyu]i
shafi na 114. Amma abin mamaki a ’yan wa]annan shekaru sai ga gwamnatin
Saudiyya ta buga wani littafi wanda a ciki aka yi }o}arin wanke Yazid ga duk
abubuwan da ya yi, alhali suna nan a rubuce a littafan tarihi na Ahlus Sunna. Abin
ma da aka rubuuta a bangon littafin shi ne Amirul Muminin, Yazid Ibn
Mu’awiyyah. Wannan ke nan a ta}aice kann shi Yazid.
Sai kuma wai Khalifah na 12, wato
Walid, shi ma ka]an daga cikin rayuwarsa kamar yadda Suyu]i ya kawo a wannan
littafi nasa na Tarikhul Khulafa cewa ya yi; Walid Khalifah ne fasi}i, ya
kasance fasi}i, mashayin giya mai keta hurumin Allah (T). Ya ci gaba da cewa
akwai lokacin da ya yi niyyar zuwa Hajji domin ya sha giya a saman Ka’abah.
Ya ce Shams-Suddin Azzahabi, ya
siffanta shi da cewa Walid ya shahara wajen shan giya da kuma luwa]i. Kai akwai
ma lokacin da ya kekketa Al}ur’ani ya ce in ya je wajen Allah ya ce Walid ne ya
kekketa shi. Wannan ke nan a ta}aice.
Mu duba mu gani wannan littafin ba
wai Malamin Shi’a ya rubuta shi ba, ballantana mutum ya sa shakku, ko kuma
ta’asubanci a kai, wanda ya rubuta shi wato Suyu]i yana ]aya daga cikin
manya-manyan Malaman Ahlus Sunnah, wanda kuma ya yi rubuce-rubuce a fannoni
daban-daban, wanda ya san tarihinsa zai fahimci haka.
Dawowa ga wannan Hadisi da yake
bayani dangane da Khalifofi 12. Suyu]i ya ci gaba da cewa wa]ansu Malamai sun ce
abin da ake nufi shi ne samuwar Khalifofi 12 tsawon muddan Musulunci har zuwa tashin
}iyama, wa]anda suke aiki da gaskiya ko da ba su kasance suna biye da juna ba.
A kan wannan ra’ayi da fahimta Suyu]i ya tafi ya kuma }arfafa a kan haka, inda yake
cewa (wato a }arshen fasalin); “Na ce a kan wannan (wato fassara) an samu daga
cikin wa]annnan Khalifofi 12, Abubakar, Umar, Usamn, Ali, sai Hasan ]an Ali dai
Mu’awiyya, sai Ibn Zubair, sai Umar [an Abdul’aziz”. In ka yi lissafi za ka ga
su ne ya ci gaba da cewa za a iya ha]uwa da Muhta]i na Abbasawa. Shi ne ya }ar}are da cewa sauran ana jira su. [ayan su
Mahdi ne, domin yana daga cikin Ahllul Bait (AS). Wannan ita ce nassin maganar
Suyu]i.
To a
nan mutum zai ga yadda Suyu]i ya fahimci Hadisin, wato a kan cewa wa]annan
Khalifofi 12 ana nufin Khalifofin da suka kasance mutanen }warai suka kuma
tsaya kan gaskiya da kuma aikata adalci ko da ba a biye suke da juna ba. Wato
za su kasance jefi-jefi a cikin tarihi, kamar yadda ya kawo sunayen 10 ya ce
saura biyu.
Sai
kuma tafsiri na uku da Malaman Ahlus Sunna suka kawo dangane da wannan Hadisin
shi ne wanda Ibnul Arabi ya ce a sharhin Sunan na Tirmizi, inda ya ce; “Idan
muka lissafa bayan Manzon Allah (S) Khalifofi 12 muka same su kamar haka,
Abubakar, Umar, Usman, Ali, Hasan, Mu’awiyya, Yazid, Mu’awiyat [an Yazid, Marwan,
Abdulmalik [an Marwan, Walid Sulaiman, Umar ]an AbdulAziz…”. Haka dai ya dinga
zana su har zuwa zamaninsa. Shi ne sai ya ce; “Idan muka lissafa 12 daga
cikinsu, za mu ga adadi 12 ya tu}e ne ga Sulaiman”. Shi ne daga }arshe ya ce;
“Ni dai ban san ma’anar wannan Hadisi ba”.
Akwai
zantuka na Malaman Ahlus Sunna kan yadda suka fahimci wannan Hadisin saboda
gudun tsawaitawa ba za a iya kawo su ba sai dai ga mai bu}atar ganin zantukan
yana iya samun littafi mai suna Ma’alimul Madrasatain, mujalladi na 1, wato na
Sayyid Murtadha Al-Askari domin ya duba.
Amma
idan mutum zai juya ya duba a littafin Shi’a zai ga sun kawo sunayen wa]anann
Khalifofin kamar haka: 1. Imam Ali (AS), 2. Imam Hasan (AS), 3. Imam
Husain (AS), 4. Imam Ali-Zainul-Abidin (AS), 5. Imam Muhammad Ba}ir (AS), 6.
Imam Jafar Sadi} (AS), 7. Imam Musa Kazim (AS), 8. Imam Ali Arridah (AS), 9.
Imam Muhammar Jawad (AS), 10. Imam Ali Alhadi (AS), 11 Imam Hasan Askari (AS),
12 Imam Mahdi (AS). A nan babu abin cewa face Alhamdulillahil lazi hadana li haza,
wama kunna linahtadiya laula an hadanallah. Mutum ya je ya binciki tarihin wa]annan bayin
Allah (T) dukkaninsu jinin Manzon Allah ne, dukkansu daga {uraish ne, kuma
cikin Bani Hashim. Mutum ya karanci tarihinsu ]aya bayan ]aya ya ga irin shaida
da Malaman Ahlus Sunnah suka yi masu na zamanin kowanne ]aya daga cikinsu.
Ba don gudun tsawaitawa ba, da an
kawo shaida da Malamai na zamaninsu suka yi masu. Da mutum zai bincika zai ga
cewa dukkansu 12 babu wanda ba a yi wa shaida cewa a zamaninsa ya fi kowa ilimi,
ya fi kowa ibada, ya fi kowa akla} da duka janibobun addini ba. Ga misali na
ilimin guda ]aya daga A’imma 12, shi ne Imam Jafar Sadik (AS), wanda Limaman
Mazahib guda biyu na Ahlus Sunna suka yi zamani da shi, wanda ba wai kawai sun
yi zamanin da shi ba ne, a’a, sun yi ma karatu a wajensa su ne; Abu Hanifa, wato
Shugaban Mazhabar Hannafiya, ga shaidar da ya bayar ga Imam Sadi} (AS). Abu Hanifa
ya ce; “Ban ta~a ganin wanda ya kai ilimin Imam Jafar Sadi}(AS) ba”. Wani waje
kuma yana cewa; “Ba domin shekaru biyu ba da Nu’uman ya halaka”. Wato yana nufin
shekaru biyun da ya yi wajen Imam Sadi} yana karatu.
Sai kuma abin da Malik [an Hasan,
wato Shugaban Mazhabar Malikiyya yake cewa, wato na shaida ga Imam Sadi}(AS); “Ban
ta~a ganin wani ba ko jin wani ba a zamanina wanda ya fi Jafar [an Muhammad
ilimi ko ibada ko kuma tsantsani ba”. Ya ci gaba da cewa; “Na yi kai-komo wajen
Jafar [an Muhammad lokuta daban-daban, duk lokacin da na je sai in same shi ko
yana Salla ko Azumi ko kuma kararun Al}ur’ani”.
Haka nan Ahmad Ibn Hambal, Shugaban
Mazhabar Hambaliyya ya yi karatu gun Imam Musa Kazim (AS). Akwai wani abin
mamaki da ya ta~a gani wajen Imam Kazim (AS) shi ne ya yi masa bayani.
Akwai kuma wani tambihi a nan shi ne;
Ahmad Ibn Hambal shi ya riskar da Imam Ali (AS) a cikin Khalifofi guda hu]u wa]anda
Ahlus Sunna suka tafi a kai, domin tsawon mulkin Banu Ummayya Khalifofi uku ne
suke lissafawa. Kuma wannan ko a hankali mutum ya auna ya gani, wanda ake zagi
a masallatai, ya za a saka shi cikin Khalifofi? Saboda haka a lokacin Abbasawa
ne Ahmad Ibn Hambal ya riskar da shi, shi ya sa ba wani Hadisi da muutum zai
iya kawowa ko da ko dha’ifi ne, wanda ya ce Manzon Allah (S) ya ce Khalifofi a
bayan guda hu]u ne.
Saboda haka a nan yana da gayar
muhimmanci musamman ga ’yan uwanmu Musulmi na Madrasa ]in Ahlus Sunna da su
rin}a yin bincike a kan abubuwan da aka samu sa~ani a kai, tsakanin Shi’a da
Sunna, domin mutum ya ga hujjojin kowa, sannan ya kwatanta, domin yin haka insha
Allah zai taimaka wajen rage gaba da kuma }iyayya da take gudana tsakanin juna.
Wanda wannan ba ana nufin mutum ya bar na shi ya zo na wani ba ne, a’a, a}alla
ana son ka fahimci hujjojin da shi ma ]an uwanka Musulmi yake a kai.
Insha
Allah sauran mahanga guda uku wani lokaci za a ]ora a kai.
No comments:
Post a Comment