Saturday 9 February 2013

Rubuce-rubucen Shehu [an Fodio a kan Imam Mahdi AF


Watan sha’aban da muka fita,kamar yadda aka sani,a cikinsa ne aka haifi Imam Mahdi [AF],saboda haka ne mabiya Ahlulbayt [AS] a sassan duniya daban daban ke gabatar da tarurruka,domin tunatar da juna dangane da ~angarori daban daban da suke da ala}a da Imam Mahdi [AF].misali,wiladarsa,gaiba ]insa,shaksiyya ]insa,alamomin bayyanarsa,bayanai da rubuce rubuce na malaman madrasah ]in Ahlus sunna dangane dashi,da dai sauransu
.Akan asasin haka ya zama zai yi kyau da kuma muhimmanci kawo wasu daga cikin bayanai da kuma rubuce rubuce wa]anda shehu usman ]an fodio yayi dangane da Imam Mahdi [AF].                                                                                                                                                                                   Shehu usman ]an fodio [da yake yadda sunan ya kamata ya kasance shine,shaikh bn fudi,amma kasantuwar galibi haka ake fa]i ko rubutawa] ya rubuta littafai masu yawa dangane da Imam Mahdi ]         1.AL-KABARUL HADI ILA AMRIL IMAMIL MAHDI.                                                                                                               2.TAHZIRUL IKHWA’AN MIN IDDI’AA’IL MAHDIYYATIL MAU’UDATI,AKHIRAZ ZAMAN.                                    3.ALAMATI KHURUJUL MAHDI.                                                                                                                                                 4.ULLUW SHA’ANI MAHDI.                                                                                                                                                          5.TANBIHUL-FAHIM da dai sauran wasu littafai da ba za’a iya kawowa ba,saboda gudun tsawaitawa.                                                                                                                                                                                                        Haka nan ]an sa Shaikh Muhammad Bello ya rubuta littafai hu]u da suka shafi Imam Mahdi [AS].Ga biyu daga ciki:                                                                                                                                                                                               1.KASHFUL KAFIYYI FI AK-BARIL IMAM MAHDI.                                                                                                                                2.AL {AUL MUK TASAR FI AK-BARIL MAHDI AL-MUNTAZAR.                                                                                      Haka nan ‘yarsa mai suna Maryam,ita ma ta rubuta littafi [aya,da ya shafi Imam Mahdi [AS] mai suna               DARI{UL HI JRATI ILA MAHDI.Haka nan jikansa mai suna Sa’id ]an Muhammad Bello,shima ya rubuta littafan da suka shafi Imam Mahdi [AF].Misali,daya ]aga ciki shine SAHIHUL KHABAR FI AMRIL MAHDI AL-MUNTAZAR.                                                                                                                                                                                                Wannan kuma banda wa]anda almajiransa suka rubuta da kuma ]an uwansa Shaikh Abdullahi.Wanda im mutum yayi zuzzurfan bincike zai ga cewa samun nahiya a duniyar sunna,wa]anda malamanta suka yi littafai da suka shafi Imam  Mahdi [AF] kamar wannan nahiyar da wahala.Mutum ya ]an bincika wasu }asashen musulmi na duniyar sunna ya gani.                                                                                                        Kuma wani abun mamaki shine,idan mutum ya bibiyi  wa]annan littafai da shehu ]an fodio ya rubuta dangane da Imam Mahdi [AF],zai ga cewa sun yi muwafa}a da yadda suka zo a madrasah ]in Ahlulbayt[AS],misali kamar yadda ya kawo shekara da watan haihuwar Imam Mahdi [AF] da nasabarsa da alamomin bayyanarsa da dai sauransu.kamar yadda za muga hakan insha Allah nan gaba cikin rubutun.Saboda haka ne ma aka samu wasu a wannan zamanin, nan da can,a bayanansu da rubuce rubucensu,da su kayi }o}arin kawo tawili a wa]annan rubuce rubucen na shehu ]an fodio,domin ganin sun yi kama da yadda shi’a suka tafi akai.Wa]anda kuma basu iya tawilantar dasu ba.sun nuna cewa shehu usman ]an fodio ya dawo daga wadannan ra’ayoyin }arshen rayuwarsa ne,domin idan mutum ya dubi malaman Ahlus sunnah da suka yi littafai dangane da Imam Mahdi [AF] zai iya kasa su gida uku.                        1.Akwai wa]anda abin da suka rubuta yayi muwafa}a da abinda  shi’a  suka tafi akai.                                        2.Akwai wa]anda abin da suka rubuta yana kusa da abinda shi’a suka tafi akai.                                                        3.Akwai wa]anda abin da suka rubuta yayi karo da abinda shi’a suka tafi akai,misali kamar yadda wasu daga malaman Ahlus sunna suka tafi akai na cewa Imam Mahdi, ba’a haife shi ba,ko kuma an haife shi yayi zamani ya wuce,da dai sauransu.                                                                                                                                         Amma idan muka duba shehu ]an fodio,ya fuskanci jarabawa daban daban a zamaninsa,musamman bayan tabbatuwar addini,na cewa shine Mahdi,domin an samu jama’a da dama a lokacin da suka tafi akan cewa shine Mahdi.kuma babban abinda daya da]a karfafa wa masu wannan ra’ayi,baya ga tabbatuwar addini }ar}ashin jagorancinsa,shine abinda yazo a cikin wani littafi na Jalaluddin As-suyu]i mai suna “AL-IR{UL WARDIY FI AKHBAARIL IMAMIL MAHDI”.Na cewa Imam Mahdi zai bayyana ne a shekara ta 1200 hijiriyya,ko kuma a shekara ta 1204 hijiriyyah.Ga shehu ]an fodio kuma ya rayu ne a dai dai wancan lokacin ga kuma Allah [T] bisa ikonsa ya tabbatar da addini }ar}ashin jagorancinsa,ga kuma wannan hasashe na suyu]i.Saboda haka akan asasin wa]annan dalilai aka samu jama’a da dama suka ce ai shine Mahdin.Amma nan take shehu yayi inkarin wannan abu da tsananin gaske,kuma ya rubuta littafai don gamsar da mutane cewa bashi bane Imam Mahdi [AF],kamar yadda zamu ga haka a nan gaba.Saboda haka bayan wannan shimfi]ar insha Allah rubutun zai gudana ta fuskoki guda uku.                                                                                                                                                                                                   1.Bayanan shehu ]an fodio dangane da Imam Al-Mahdi [AF].                                                                                     2.Inkarinsa na cewa shine Mahdi.                                                                                                                                             3.Ala}arsa da Imam Mahdi [AF].                                                                                                                                                              1.BAYANAN SHEHU [AN FODIO DANGANE DA IMAM MAHDI [AF].
Idan aka duba littafinsa mai suna NASIHATU AHLIZ ZAMAN.Mutum ya duba fasali na bakwai a cikin littafin,wanda shine fasali na }arshe a littafin;taken fasalin shine,fasali na bakwai cikin ambaton al’amarin Imam Al-mahdi,wanda shine halifa na }arshe”.A cikin fasalin shehu usman ]an fodio yana cewa, “ku sani yaku yan uwana,bayyanar Imam mahdi [RA] wani al’amari ne wanda yake yankakke [wato tabbatacce],domin hadisai akan haka sun kai haddin tawatur.kuma kasancewarsa daga zuriyar fa]imatu ‘yar Manzon Allah [S],shima abune yankakke domin hadisai akan haka sun kai haddin tawatur”.A wani sashe na fasalin yana cewa, “Ku sani ba makawa daga bayyanar Mahdi [AS],amma bazai bayyana ba har sai }asa ta cika da zalunci da danniya,sannan ya cika duniya  da adalci,kuma koda ba abin daya rage a kwanukan duniya sai yini ]aya,to Allah [T] zai tsawaita yinin,har wannan khalifa ya ji~ince ta.kuma yana daga itrar Manzon Allah [S] ne,daga ‘ya’yan fatima [RA], kuma mahaifinsa shine Al-hassan Al-askari ]an Imam Aliy An na}iy,]an Imam Muhammad At-ta}iy,]an Imam Aliy Arrida,]an Imam Musa Al-kazeem,]an Imam Jafar As-sadi},]an Imam Muhammad Al-ba}ir,]an Imam Zainul Abidin Ali,]an imam Hussain,]an Aliy ]an Abi Talib [AS]”.                                     Haka nan kuma a wani sashe na fasalin da yake bayani dangane da haihuwar Imam Mahdi [AF] yake cewa, “Haihuwarsa [AS] ta kasance daren 15 ga sha’aban shekara ta 255,kuma yana wanzuwa [raye] har zuwa lokacin da zasu ha]u da Isa ]an maryam [AS]”.                                                                                           Idan muka duba,ko da daga wa]annan abubuwa da aka kawo,dukkansu sunyi muwafa}a da yadda suka zo a madrasah ]in Ahlulbayt [AS].Misali,yadda ya kawo nasabar Imam Mahdi [AS],da kuma wata da shekarar haihuwarsa,da kuma cewa ba zai bayyana ba har sai duniya ta cika da zalunci da danniya,da kuma bayyana shi a matsayin khalifan Manzon Allah [S] na }arshe.                                              Akwai ma in da yake cewa a cikin fasalin, “shi Imam Al-mahdi yana daga cikin wanda wajibi ne abi sunnarsa,domin shi yana daga cikin khulafa’ur Rashiduna Almahdiyyin,shine ma na }arshensu”.                                                                    Haka nan ma awani sashe na fasalin yana cewa, “amma ayyana lokacin bayyanarsa,ace sa’a kaza ko rana kaza ko shekara kaza,ba wanda yasan haka in ba Allah [T] ba”.                                                                                                                                    Idan kuma muka ajiye wannan littafin muka ]auko littafinsa mai suna AL-KHABARUL-HADI ILA AMRIL IMAMIL MAHDI,a cikinsa ya kawo al’amura daban daban guda 10 wa]anda suke da ala}a da Imam Mahdi [AF].Misali,inda yake cewa, “al’amari na shida sanin cewa lalle Mahdi [RA] yana raye”.                            Shehu ]an fodio ba kawai ya tafi akan Imam Mahdi yana raye bane,wuce nan.ya tafi akan akwai yiwuwar a sadu dashi.mutum ya duba a cikin littafin,al’amari na 10, ya kawo }issar wani bawan Allah [T] daga madrasah ]in Ahlus sunna,wanda ya ha]u da Imam Mahdi [AS],ga mai bu}ata yana iya duba littafin da yake }issar na da tsawo,kuma a }arshe shi wannan littafi in mutum ya duba zai ga yadda shehu ya kammala wannan littafin da addu’ar cewa,  “ya Allah ka }addara mana saduwa dashi,da kuma ha]uwa dashi ta ‘hissi’,wadda take tabbatuwa da gangar jiki,kamar yadda ka }addara mana ha]uwa dashi ta ma’anawiy”.                                                                                                             Wanda wannan shima bai sa~a wa yadda malaman madrasah ]in Ahlulbayt [AS] suka tafi akai ba,wato na yiwuwar ha]uwa da Imam Mahdi [AF].Ba domin saboda gudun fita cikin maudu’in ba,da an kawo wani misali na wasu bayin Allah [T] daga madrasah ]in Ahlulbayt [AS] da suka samu baiwar ha]uwa da Imam Mahdi [AS].                                                                                                                  Wannan kenan dangane da bayanan da shehu ]an fodio yayi game da Imam Mahdi [AF].Mutum ya kwatanta su da yadda suka zo a shi’a zai ga duk sun yi muwafa}a.                                                                                                                                           2.INKARINSA NA CEWA SHI NE IMAM MAHDI [AS]:
Kamar yadda ya gabata cewa wannan ya kasance babbar jarabawa ga shehu a lokacin,domin a lokacin in mutum ya bibiyi tarihinsa zai ga yayi iya iyawarsa ta hanyan rubuce rubuce,jawabai  kai har ma da wake,domin  a lokacin su mutane ne masu zau}in wa}e,domin ya gamsar dasu cewa shi ba shi ne Imam Mahdi ba.misalin littafi daya rubuta akan haka shine mai suna TAHZIRUL IKHWAAN MIN IDDI’AA’IL MAHDIYYATIL MAU’UDAH AKHIRAZ ZAMAN.In mutum ya duba littafin akwai in da yake cewa, “kusani yaku yan uwa cewa bani ne Imam Mahdi [AS] ba,kuma ban ta~a da’awar cewa ni Imam Mahdi ne ba,na kan ji haka a bakunan mutane,kuma na yi iyakar }o}ari na domin yi musu kashedi akan haka,kuma na bayyana raddina akan haka a wallafe wallafena na Arabiyya da kuma Fulatanci”.                                                               A wani waje a littafin yana cewa, “yaya zan yi da’awar ni Mahdi ne? alhali an haife ni a Biladus Sudan a wani wuri da ake cewa ‘Marad’ kuma yaya zan yi da’awar cewa ni Mahdi ne,alhali sunana bai dace da sunan Annabi [S] ba,domin sunana Usman,kuma sunan mahaifina bai dace da sunan mahaifinsa ba,domin sunan mahaifi na muhammad.kuma an riga an sani a cikin hadisan Annabi cewa Al-mahdi sunansa ya dace da sunan Annabi” a wani waje kuma yana cewa “Imam Mahdi yana da siffofi da kuma asrar,wanda ni bani dasu.”da dai sauran bayanai wanda saboda gudun tsawaitawa baza a iya kawo su ba,wanda shehu ]an fodio yayi domin raddi ga masu irin wannan tunanin a lokacin.                                                                                                                                                            3.ALA{ARSA DA IMAM MAHDI [AF]:
Tabbas idan mutum ya bibiyi tarihi da kuma rayuwar shehu usman ]an fodio zai ga yana da ala}a babba kuma ta musamman da Imam Mahdi [AS].Akwai ma in da yake cewa, “Allah [T] yayi mani  baiwa da sanin Imam Mahdi da koyi dashi”.idan mutum ya duba tarihinsa zai ga ya kasance mai gayar tawali’u ga Imam Mahdi [AS].kuma ya kasance mai gayar shau}i gare shi,akwai }asidodi na wa}e da yayi da harshen fulatanci na yabo da kuma bayanin darajojin Imam Mahdi [AS].kuma akwai in da yake cewa, “wannan jihadin da nayi da izinin Allah har sai ya dangana da zuwan Imam mahdi”.kuma yana cewa wannan abu da yayi shimfida ne ga zuwan imam Mahdi [AS],kuma shehu usman ]an fodio ya bar wasiyya ga ‘ya’yansa da jikokinsa da zuriyarsa baki ]aya da sauran jama’a, a lokacin cewa idan Mahdi ya bayyana su kasance tare da shi, su kuma taimake shi,da kuma yin hijira zuwa gare shi.Wannan wasiyya ta shehu ita ta san ya jikansa mai suna Hayatu ]an sa’id ]an muhammad Bello,lokacin da wani a Sudan ya bayyana yayi da’awar cewa shine Mahdi [wato wanda ake cewa mahdin sudan,wannan ya faru shekaru 50 bayan rasuwar shehu ]an fodio],sai shi wannan jikan shehu ]an fodio ya bar sakkwato zuwa sudan da nufin taimaka masa,har ma da ya sadu dashi yake ce masa “lalle na yi maka bai’a ni da ‘ya’yana da dukkan wa]anda suke tare dani”.Ya ci gaba da ce masa, “ha}i}a shehu usman ]an fodio yayi mana wasiyya da hijira zuwa gareka,da taimakon ka da kasantuwa tare da kai idan ka bayyana”.                                                                                                                                    Duk da an samu malamai a sakkwato a lokacin da suka yi inkarin haka,na cewa abin ba gaskiya bane,amma wannan abin da yake nunawa shine irin yadda shehu ya gina ‘ya’yansa da jama’arsa, na su taimaka wa Mahdi [AS] idan ya bayyana.kuma mu duba yadda shehu ]an fodio yayi tsayin daka wajen inkarin masu cewa shine Mahdi,,misali akwai in da yake cewa “wanda yake riyawar ni ne Mahdi da sannu zata bayyana ba haka bane,don na bayyana siffofin Imam Mahdi [AS]”.wannan a wasu baitocin wa}e yake fa]in haka,a wani wuri a wa}en yana cewa, “ina garga]inku,kuma ina ro}onku don Allah mai girma, ku kame daga fa]in cewa ni ne Mahdi”da dai sauran bayanansa wa]anda ba za’a iya kawowa ba,saboda gudun tsawaitawa.da suka nuna ala}arsa da Imam Mahdi [AS].Daga }arshe akwai darasi babba da zamu koya daga wa]annan rubuce rubucen na shehu usman ]an fodio dangane da Imam Mahdi [AS],shine zuzzurfin bincike da yayi kan wanna abu,domin idan mutum ya bibiyi wadannan littafai da aka ambata a sama wa]anda ya rubuta dangane da Imam mMahdi [AS],zai ga ya dogara ne da masdarorin Ahlus sunna,domin kaiwa ga wannan sakamako.wato bincike yayi mai zurfi,duk ko da }arancin wasa’il na ilimi da ake dashi a zamanin da kuma rashin hanyoyin sadarwa,to, ina ga wannan zamanin da muke ciki mai cike da wasa’il daban daban na ilimi da kuma hanyoyin sadarwa,saboda haka yana da muhimmanci mu tashi tsaye domin amfanuwa da wa]annan wasa’il daban daban na ilimi,domin kai wa ga irin wa]annan natijoji,da fatan Allah [T] ya amfanar damu da abubuwan da aka karanta amin.

No comments:

Post a Comment