Imam Sadi}[AS],kamar
yadda aka sani shine imam na 6 a jerin I mamai
12.kuma wannnan munasaba ce ta wafatinsa,domin
ya koma ga Allah [T] ne ranar 25 ga wannnan wata da muke ciki na
shawwal,a shekara ta 148 bayan hijra.Ya rasu sakamakon guba da aka sa mishi a
inabi,kuma ya rasu ya nada shekara 65, a wata ruwaya shekara 68
.Kuma wannnan
yana ]aya daga
cikin khususiyar Imam Sadi}
[AS] wato na tsawon shekaru.Domin in mutum ya bincika zai ga cewa in ka ]ebe Imam Mahdi [AS],to
duk Imamai da suka gabace shi da kuma wa]anda
suka biyo bayansa, basu kai wa]annan
shekarun ba.Alal misali ga shekarun da kowane yayi a duniya.Imam Ali [AS]
63,Imam Hasan [AS] 48,Imam Husain [AS] 57,Imam Zainul Abidin 57,Imam Ba}ir [AS] 57,Imam
Sadi} [AS] 65,
ko 68 a wata ruwaya,Imam Musa Alkazim [AS] 55,Imam Ridah [AS] 51,Imam Jawad
[AS] 25,shine mafi }arancin
shekaru a raye,in an kwatanta da sauran A’imma [AS].Imam Hadi [AS] 41,Imam
Askari [AS] 28,Imam Mahdi [AS] shi yana nan a raye har yanzu,Allah [T] ya
gaggautar da bayyanarsa.Haka kuma
shekaru na Manzon Allah [S] a duniya 63,na kuma Sayyida Fatima [AS] 18.To anan
in mutum ya duba,in ka ]ebe
Imam Mahdi [AS] ka dubi shekarun
da wa]annan
Ma’asumai su kayi a duniya ka kwatan ta dana Imam Sadi} [AS] za kaga ya fisu tsawon shekaru a
duniya shi ake nufi da waccen khususiyyar
da aka ambata a sama. Haka
nan khususiyya ta biyu,wadda Imam Sadi}
[AS] ya ke~anta
da ita in ka kwatanta da Imaman da suka gabace shi da kuma wa]anda suka biyo
bayansa shine,samun dama da kuma yana yi na koyar da ‘ulum’ na Ahlulbayt
[AS],saboda a lokacin a madina kawai
yana da masu ]aukar
karatu a wurinsa sama da mutum 4,000.Wanda dukkansu shi’arsa ne,wato banda wa]anda suke kan
wasu a}idoji
da kuma mazhabobi,wa]anda
su ma suke karatu a wurinsa kamar yadda zamu ga haka nan gaba a wajen bayanin
iliminsa. Khususiyya
ta uku,a lokacin Imamancinsa ne daular Bani umayya ta fa]i da kuma hawan daular
Abbasiyawa.Kabarinsa na madina ne a ma}abartar Ba}i’a.Kusa
da shi akwai kabarin Imam Hasan [AS],da na Imam Zainul abidin [AS],da kuma na
Imam Ba}ir
[AS],Imamai 6 kuma kabarinsu na Ira}i
ne.Sune Imam Ali [AS],Imam Husain [AS],Imam Kazim [AS],Imam Jawad [AS],Imam
Hadi [AS],da kuma Imam Askari [AS],sai kuma Imam Ridah [AS] shi kuma nasa yana
Iran ne.Wannan kenan a ta}aice
dangane da abin da yake da ala}a
da wafatinsa. Sai
kuma bayani a ta}aice
dangane da wasu ~angarori
na rayuwarsa da nufin su zama darasi gare mu,wanda insha Allah in muka ]abbaka su a
rayuwarmu,zasu kasance masu amfani gare mu duniyarmu da kuma lahirarmu. 1-AKHLA{-[INSA:
A-AFUWARSA,Imam
sadi}[AS] ya kasance mai yawan
afuwa,ba wai kawai ya kan yi afuwa ga wanda yayi masa laifi bane,a’a yak an ma
nema masa afuwa a wajen Allah[T],misali;akwai wani mutum da yaje wajen sa sai
yace ma Imam Sadi}[AS],wane,ko yace kaza da kaza gare ka,wato marasa kyau,ciki
har da zaki,kamar yadda yazo a
ruwayar.Sai Imam Sadi}[AS] yace ma kuyangar
sa[baiwarsa] kawo min abin al-wala,data kawo sai yayi alwala,bayan haka yai
sallah raka’a biyu.Bayan haka yai addu’a yace, “Ya ubangiji wannan mutumin ya ta~a ha}}ina,to,na yafe
masa,kai ne mafificin yafewa,ka yafe masa kada ka kama shi,ko kayi masa hisabi
saboda ni.”Shi wanda ya kawo wannan Maganar,sai
yai tsammani,Imam Sadi}[AS] zai ma mutumin mummunar addu’a ne,amma
sai yaga akasin haka,wannan babban darasi ne,gare mu.Haka nan an ruwaito cewa wani
mutum cikin mahajjata sai jakar ku]insa ta fa]i,ya dudduba bai gani ba,sai ya
ga Imam Sadi} [AS] yana sallah a masallacin Manzon Allah [S].To da yake bai san
ko waye ba,kawai wal’iyazubillah sai yace shi ya ]aukar masa jaka.Sai Imam Sadi} [AS] yace
masa cikin lausasawa,mene ne cikin jakar? Yace dirhami dubu ke ciki.Sai Imam
Sadi} [AS] ya bashi dirhami dubun.Mutumin
ya wuce kenan beyi nisa ba,sai ya ga jakar ku]in nasa,sai ya dawo wajen Imam Sadi} [AS] yana cewa ya yafe masa ,ya mi}a masa dirhami dubun,sai Imam Sadi} [AS] yace ba zai amsa ba.Ya tafi ya bashi.Yace masa, “Duk abinda ya
fita hannuna ,to ba zai dawo ba”.Shine wannan mutum abin ya bashi mamaki ,sai
yaje ya tambaya,wai waye wannan? Sai aka ce masa Ja’afar Sadi} ne.Shine ya tafi yana cewa haba,shi ya san
wannan aiki sai shi! Shine Imam Sadi} [AS] ya na yawan cewa, “Mu Ahlul Baitin manzon Allah,]abi’unmu shine yin afuwa ga wanda ya
zalunce mu”.Mu duba wannan }issa mu
gani,zamu ga cewa A’imma [AS] ba wai kawai sun fuskanci jarabawowi wajen masu
tafi da iko na zamunansu bane,a’a har da jarabawowi daga mutanen gari,in ba
haka ba.Don ba kaga kayanka ba,mutum na
sallah sai kace shi ya ]aukar maka.
B:KYAUTAR SA [AS]:Imam Sadi} [AS] ya
kasance mai yawan kyauta,wani daga cikin sahabbansa,ya shiga wajensa yace masa
yana cikin matsala ta rayuwar,saboda haka yana son Imam Sadi} ya taimaka masa da addu’a,sai Imam Sadi} [AS] ya aika akawo masa wata jaka da
aka kawo ya mi}a masa,yace
wannan jaka akwai dirhami ]ari hu]u,kaje ka biya bu}atarka da shi, sai Imam Sadi} [AS] yace ka tafi da shi zan yi maka
addu’ar. Haka
nan wani fa}iri ya ta~a zuwa neman taimako wajensa,sai ya
bashi dirhami 400,sai fa}irin ya amsa
ya tafi yana godiya.Sai Imam Sadi} [AS] yace
wa khadiminsa je kace wa mutumin ya dawo .Sai wannan khadimin yace masa, baya
tambaye ka ba,ka kuma bashi? Sai Imam Sadi} [AS] ya
amsa masa da cewa ; “Manzon Allah [S]
yace mafificiyar sadaka itace wadda ta wanzar da wadata,sai Imam Sadi} [AS] ya mi}a masa zobe mai tsada.Kamar yadda yazo
a ruwaya,yace masa duk lokacin da aka shiga cikin matsala ka sayar da zoben. Kuma
Imam Sadi} [AS] ya
kasance yakan aika da kyauta ga wani ko ga wasu ba da sanin cewa daga wajensa
bane.Misali,akwai wani ]an uwansa
na jini lokaci bayan lokaci yakan aika da kyautar ku]i mutumin ya tambayi ]an sakon wannan da yake aiko wa da
wannan sa}on lokaci
bayan lokaci wa nene? Sai ]an sa}on yace masa bai son a bayyana ko wanene,kawai sai wannan mutumin ya
kada baki yace kai wannan mutumi na taimaka mana,amma ga Ja’afar ]an uwana ne,ga shi da ku]i amma ko dirhami ]aya bai taimake ni da shi ba.Mu duba
kuma irin wannan jarabawa daga ‘yan uwa na
jini,shi yana }ule da
Imam Sadi}
[AS],alhali shi yake aika masa da wannan taimako. Haka
nan kuma yazo akan cewa Imam Sadi} [AS],idan
dare yayi, lokacin da duhu yayi duhu yakan ]auki kayayyaki na
abinci,nama da ku]I, ya ]auka da kansa yana bin gidajen
matalauta yana raba musu,basu san ko waye ba,sai bayan rasuwar Imam Sadi} [AS] suka ga abubuwan da aka saba
basu na agaji ya yanke,suka fahimci ashe
Imam Sadi}[AS] ne,
ke kai masu wa]annan
kayayyakin.
C:TAUSAYINSA:Imam Sadi} [AS] ya
kasance mai yawan tausayi.Akwai wani daya shiga wajen Imam Sadi} [AS] sai ya gan shi launinsa ya
canza,kuma cikin damuwa,sai mutumin yace masa lafiya? Sai Imam Sadi} [AS] yace masa; “na hana hawa saman daki ,sai na shiga cikin gida na ga ]aya daga
cikin kuyangina ta hau ]auke da ]aya daga cikin yara na da take reno,ganina sai ta firgita ta ]imauta har wannan yaron ya fa]o ya kuma rasu.Wannan damuwa da
kaganni a ciki ba wai saboda rasuwar
wannan yaron nawa bane, a’a yadda na ga ta firgita hankalinta ya tashi shine tausayinta ya kama
ni”.Daga }arshe Imam
Sadi} [AS] yace mata ba komai har sau
biyu.Yace kuma ta tafi ya ‘yanta ta saboda Allah [T].
2.GIRMAMAWARSA GA MANZON ALLAH [S]:An ruwaito cewa akwai wani daga
cikin sahabban Imam sadi} [AS] ya
kasance ya kan je majalisin Imam Sadi} [AS],sai
aka kwana biyu bai je ba.Ran da yaje sai Imam Sadik [AS] yace masa,kayi kwana
ki bangan ka ba.Sai yace masa haihuwa aka yimin,an sami da namiji,sai Imam Sadi} [AS] yace Allah yayi masa albarka,ya
tambaye shi wane suna kasa mishi? Sai yace nasa masa Muhammad,jin haka sai Imam
Sadi} [AS] ya sunkuyar da kansa }asa yana cewa har sau uku, Muhammad!
Muhammad! Muhammad!!! Sannan yace; kaina da na iyali na da wa]anda suke a doron kasa baki ]aya,su kasance fansa gareka ya Manzon
Allah [S]”.Daga }arshe yace
masa. “Tunda kasa masa suna Muhammad,to kada ka zage shi,kada ka dake shi,kada
ka munana masa”.Yace kuma ka sani babu wani gida a doron }asa wanda akwai mai suna Muhammad a
ciki face mala’iku zasu dinga tasbihi kowace rana a gidan.Akwai
ma Hadisi da yazo cewa talauci baya shiga gidan da akwai mai suna Muhammad.Mu
duba ta’azimin sa ga Manzon Allah [S] na sun kuyar da kai,da yaji sunan Manzon
Allah [S],da kuma abinda ya fa]a ma wannan
mutum daya sa ma ]ansa sunan Manzon
Allah [S],yace kada kayi masa kaza da kaza,wato wannan yana alamta gayar
girmamawar sa ga Manzon Allah [S].
3.IBADARSA:Imam Sadi} [AS] ya
kasance mai yawan ibada,yazo akan cewa a zamaninsa baki ]aya babu wanda ya kai shi yawan
ibada,akwai ma fa]in Malik ]an Anas,wato shugaban mazhabar malikiyyah
yace; “Na jajje wajen Ja’afar ]an
Muhammad lokuta da yawa,amma duk lokacin
da naje sai in samu yana ]ayan uku;
ko yana sallah,ko karatun Al}ur’ani,ko kuma
yana Azumi”.Akwai kuma wani da ya ga Imam Sadi} [AS] ya yi sujuda a masallacin
Manzon Allah [S],mutumin yana zaune yana jin Imam Sadi} [AS] ya na tasbihi a cikin
sujudar,sai wannan mutumin ya ]aukar wa
kansa cewa,ko zai dinga }idaya wannan
tasbihi da yake yi,yana ta }idayawa,sai
da Imam Sadi} [AS] ya yi
tasbihi 360 sannan ya ]ago daga sujudar.Akwai kuma wata rana
Imam Sadi} [AS] yana
karanta Al}ur’ani a cikin
sallah sai aka ga yana yinsa ya canza,bayan da ya gama sai aka tambaye shi akan
haka sai yace; “Ban gushe ba ina karanta wa]annan ayoyi na Al}ur’ani ba, har na kai matsayin da kamar ina
jinsu mubasharatan daga wanda ya saukar dasu”.Haka ma Imam Sadi} [AS] ya ta~a kasancewa a wani wata na Ramadan ba
shi da lafiya,amma duk da haka a daren 23 na watan yace akai shi masallacin Manzon
Allah [S],haka ya dinga ibada duk da halin da yake ciki na rashin lafiya har
wayewar gari. Akwai wata rana suna tafiya da
wani mutum akan dabba kawai sai yaga Imam Sadi}[AS] ya sauko yayi sujuda,kuma ya tsawaita a sujudar,shine da ya ]aga kai daga sujudar sai shi wannan mutumin ya tambayi Imam Sadi} [AS] dalilin haka.Sai Imam Sadi} [AS] yace masa yayi ne saboda godiya
ga Allah [T] kan wata ni’ima da yayi masa,watau sujudu shukru.Kuma ita wannan
sujuda ta godiya ana son mutum ya saba da yin ta a duk lokacin da Allah [T]
yayi masa wata ni’ima,ko kuma ya tun ku]e masa wata
musiba.Domin yin haka hanya ce ta da]a samun abinda
Allah ya ba ka ko kuma da]a tsare ka
daga abin da ya tsare ka,wato kamar yadda Allah Ta’ala yake cewa idan kuka gode
zan }ara maku. Haka nan yazo akan cewa duk lokacin daya tsaya
zai yi sallah akan ga launin sa ya canza,kuma jikinsa na makyarkyata ba don
komai ba sai saboda tsoron Allah [T] da kuma ta’azimin wanda zai tsaya gaba
gare shi,wato Allah [T]. Haka
nan kuma ya kasance mai yawan addu’oi,an samo addu’oi da yawa daga
wajensa.Akwai ma wani malami daya tattaro addu’oin da aka samo daga wajen Imam
Sadi} [AS] ya mai she shi littafi,yasa masa
suna Sahifatu-Sadi}iyya.Ana samun
littafin.Haka nan kuma Imam Sadi} [AS] ya
kasance mai yawan azumi,kuma ya kasance ya kan
kwa]aitar da mai
azumi cewa idan mutum na azumi to ya kiyaye ruhin azumin.Alal misali ya kan ce;
“Idan kana azumi to jinka da ganinka da harshenka suyi azumi [wato su kame]
daga munanan abubuwa.Yace kada ranar da kake azumi ta zama kamar ranar da baka
azumi.Wato ranar da mutum yake azumi ya da]a kame ga~o~insa daga sa~a wa Allah [T] fiye da ranar da bai azumi.Yazo akan cewa wata rana
Imam Sadi} [AS] yana
fa]in cewa “Na kasance lokacin ina
saurayi,wato matashi,na kasance ina yawan ibada,har Babana yace min in
sassauta.Domin idan Allah [T] yana son
bawa,to yakan yarda da ka]an daga
wajensa”.A ta}aice dai Imam
Sadi} [AS] ya kasance mai yawan ibada ta
kowace fuska,wato a salloli,karatun Al}ur’ani,Azkar,Azumi,Addu’oi
da dai sauransu.
4.ILIMINSA:Mutum zai iya cewa duk janibobin rayuwar Imam Sadi} [AS] babu wani janibi daya fi fice
akai,kamar wannan janibi na iliminsa saboda ya samu yana yi na ba da ilimi da
kuma ya]a shi fiye
da sauran A’imma na Ahlulbayt [AS],har ma yana yawan fa]in cewa; “Ku tambaye ni gabanin ku rasa
ni,domin babu wanda zai baku Hadisai a bayana kamar yadda nake baku
Hadisan”.Akwai kuma in da yake cewa; “Na san littafin Allah [}ur’ani] ciki da bai kamar tafin hannuna”.Akwai kuma
in da yake cewa na san abinda yake cikin sama da abinda ke cikin }asa da abinda ke cikin Aljanna da kuma
wuta da abinda ya kasance da kuma abinda zai kasance daga nan har zuwa sa’ar }iyamah”. Shugabannin
mazhabobi guda biyu na madrasa ]in Ahlus
Sunnah duk a wajen sa suka yi karatu,wato Abu Hanifa,shugaban mazhaban
Hanafiyya.Akwai ma wata Magana tasa da yake cewa;ba domin shekaru biyu da yayi
yana karatu gun Imam Sadi} [AS] ba,to
daya halaka.Haka nan Malik ]an Anas
wato shugaban mazhaban Malikiyya,shima yayi karatu a wajensa,ba wai kawai yayi
karatu a wajensa bane,a’a ya tasirantu sosai da wasu abubuwa daya gani daga
rayuwar Imam Sadi} [AS],misali,yadda
yaga Imam Sadi} [AS] yana
ta’azimin Manzon Allah [S] in zai ambaci sunansa a wajen bada hadisi ko kuma
idan yaji sunansa ko kuma ba zai fa]i wani
hadisi na Manzon Allah [S] ba sai yana da alwala,ire-iren wa]annan abubuwan sun yi tasiri ga Malik
sosai,domin takai shima ya kwaikwayi haka daga Imam Sadi} [AS].Akwai ma lokacin da Imam Sadi} [AS] yace masa “Yana son sa.Yazo akan
cewa duk lokacin da Malik ya tuna wannan Magana ya kanyi farin ciki,kuma ya
gode wa Allah [T]. Kuma Imam Sadi} [AS] koyarwar da yayi,yayi ne a
dukkan fannoni na ilimi kamar Tafsir,Tauhid,Fi}hu,Hadisi.A ta}aice dai babu
wani fanni wanda Imam Sadi} [AS] bai
karantar ba,kai hatta fannin ilimin kimiyya wato ilimin ‘science’ kamar
Chemistry,Biology, da kuma Physics duk asalin su daga wajensa ne.Hatta malaman
kimiyya magabatansu sun tabbatar da haka.Kuma a cikin almajiran Imam Sadi} [AS],wanda yafi fice a wannan ilimi
na kimiyya shine Jabir ]an
Hayyan.Mutum in yana son }arin
bayani sosai kan wannan ilimin kimiyya da Imam Sadi} [AS] ya koyar, ya samu littafi mai
suna A’IMMATUNA juz’I na ]aya ya
duba.
Wannan kenan a ta}aice dangane
da iliminsa sauran darussan takwas insha Allah a wata munasabar ta wiladarsa
,ko wafatinsa za’a ]ora akai.
No comments:
Post a Comment