Kasantuwar wannan wata
da muke ciki na Zul –}ada
a cikinsa ne wilada da kuma wafatin Imam Ali ibn Musa Ar-Ridah[AS]suka
kasance,domin yazo a tarihi cewa an haife shi ranar Alhamis 11 ga watan zul }ada
a shekara ta 148 bayan hijira.Ya rasu 23 ga watan zul }ada
shekara ta 203 bayan hijira.Amma a wata ruwaya,yazo
a kan cewa rasuwarsa ta kasance a watan safar ne
.Shaikh Abbas Al-}ummiy
ya tafi akan 23 ga watan zul }ada,
kamar
yadda ya kawo a littafinsa na mafatihul Jinan.Har ya ci gaba da cewa sunna ne
ziyarar Imam Ridha[AS]a ranar daga kusa ko kuma nesa.In mutum ya duba littafin
mafatihul jinan zai ga ya kawo ziyarori
dabam-dabam na Imam Ridha[as].In mutum zai iya biya su duka a ranar yana da
kyau,ko kuma ya karanta abinda ya sau}a}a masa na
ziyarar. Haka nan in aka duba za a ga
cewa tsakanin haihuwar Imam Ridha[AS] da rasuwar Imam Sadi}[as]Kusan
kwanaki 15 ne.Domin wafatin Imam Sadi}[as]
a watan shawwak ne 25 gare shi,shekara ta 148,shi kuma wiladarsa 11 ga watan
zul }ada shekara ta 148.Ya mazo a kan cewa
Imam Sadi}[as] yayi fata da shau}in
ha]uwa
da Imam Ridha[as]domin ya gan shi,har
ambatonsa yayi da kalmar MALAM,tun gabanin a haife shi,kamar yadda zamu ga haka
in sha Allah dangane da bayani na ilminsa. Imam
Ridha[AS]kamar yadda aka sani shine Imam na takwas a jerin Imamai
12,an haife shine a Madina,sunan mahaifiyarsa, [ahira,sunan mahaifinsa
kamar yadda aka sani Imam Kazim[AS]kuma yana da la}ubba
da yawa,amma wanda yafi shahara shine wannan la}abi nasa na Arri-dha.An tambayi Imam Jawad[AS]cewa mi yasa ake cewa babanka Arri-dha,ya ba da
amsa da cewa;Saboda ma}iyan sa
sun yarda da shi,kamar yadda masoyan sa suka yarda dashi.yace haka bai kasance ga Imamai da suka gaba ce
shi ba.Shekarunsa a duniya 55,muddan shekarun Imamancinsa 20,wato
ya na da shekaru 35 a duniya Imamanci ya dawo gare shi.kabarinsa yana a
khurasan ne,wato a }asar Iran.Kuma yaro ]aya yake da shi
shine,Imam Jawad[as]idan
mutum ya bincika zai ga cewa Imam Ridha[as]shine mafi }arancin’ya’ya,
idan an kwatanta da Imaman da suka gabace shi da kuma wa]anda
suka biyo bayansa,in ka ]ebe Imam Hasan
Al-askari[as]da yake yazo akan cewa shima yaro ]aya
yake dashi,shine Imam Mahdi[AF].
Ga adadin
‘ya’ya na kowane daga cikin A’imma na Ahlulbayt [AS].Imam Aliy [AS] ‘ya’ya
25,maza 11,mata 14.Imam Hasan [AS] 15,maza 8,mata 7.Imam Husain [AS] ‘ya’ya
7,maza 4,mata 3.Imam Zainul Abidin [AS] 16,maza 12,mata 4.Imam Ba}ir [AS] 7,maza 5,mata 2.Imam sadi} [AS] 10,maza 7,mata 3.Imam Kazim [AS]
36,maza 17,mata 19.Imam Ridah [AS] yaro namiji guda ]aya.Imam Jawad [AS] 4,maza 2,mata 2.Imam
Hadi [AS] 5,maza 4,mace 1.Imam Hasan Al’askari [AS]yaro guda ]aya,shine Sahibuz- Zaman,Imam Mahdi [AS].Allah Ta’ala ya
gaggauta bayyanarsa.Sayyida Fa]imah [AS] 5,maza 3,mata 2.Sai kuma fiyayyen
Halitta,wato Manzon
Allah [S] 7,maza 3,mata 4. Sai
dai tambihi anan shine,kamar yadda akan samu bambancin ruwayoyi na shekara ko
wata ko rana na haihuwar ]aya daga cikin Ma’asumai [AS],ko kuma
wafati,to,haka nan akan samu bambancin ruwayoyi na adadin ‘ya’yansu.Saboda haka
babu mamaki mutum yaga wata ruwaya akasin yadda aka kawo adadin anan,wannan
ruwaya na adadi da aka kawo,itace wadda mai littafin A’IMMATUNA ya tafi a kai.
Saboda haka kamar yadda aka ambata,in mutum ya
duba zai ga Imam Ridah [AS] da kuma Imam Askari [AS] kowannensu na da ]a ]aya ne,wanda kuma yafi yawan ‘ya’ya a
cikin A’imma [AS],shine Imam kazim [AS],domin yana da ‘ya’ya 36.Sai dai wani
tsokaci anan shine,wa]annan ‘ya’ya mata na Imam kazim [AS] su 19 a wata ruwaya
21,dukkansu ba wadda ta ta~a yin aure har suka koma ga Allah[T].Malaman tarihi
sun kawo dalilai na rashin yin aurensu,in Allah [T] ya kai mu munasabar
shahadar Imam kazim [AS] za’a kawo wa]annan dalilai.Sai dai kasantuwar wannan wata da
muke ciki na Zul }adah,Ranar farko na watan ne aka haifi
Sayyida Ma’asuma [AS],wato wadda kabarin ta ke birnin -}um,ita ce kuma babbar ‘yar Imam kazim
[AS].}an-wa
ke nan take ga Imam Ridha[AS]saboda haka,Anan tabarrukan za’a kawo tarihinta a ta}aice. 1.WILADARTA:
Watau haihuwarta,an haife ta a madina,1 ga watan zul }adah,Hijira ta 173. 2.NASABARTA:
Mahaifinta shine Imam kazim [AS],sunan mahaifiyarta [ahira,wato mahaifiyarsu ]aya da Imam Ridah [AS],kuma ita wannan
mahaifiya tasu,[ahira
bai war Allah ce mai yawan ibada, kamar yadda yazo a tarihinta.Ya mazo a tarihinta
cewa,lokacin da ta haifi Imam Ridah [AS] ta bu}aci a nemo mata mai raino,aka tambaye ta
dalili,sai tace ibadodin da ta saba yi sun ragu,saboda haka tana bu}atar taimakawa wajen reno domin ta cike gi~in ibadodinta.Kakanta shine Imam Sadi} [AS].Yazo akan cewa tun gabanin a haife ta yayi albishir da haihuwarta da kuma fa]in falalar ta da kuma ziyarar ta. Daga
cikin falalar ta da Imam Sadik [AS] ya fa]i,akwai cewa tana da matsayi a wajen Allah [T].Shi
yasa wanda duk Allah [T] yayi wa muwafa}a da ziyarar haramin kabarinta dake birnin }um,a kofar shiga haramin zai ga an rubuta “Ya Fa]ima ki ce ce ni a wajen Allah,domin ki na da
matsayi a wajensa”.Allah Ta’ala ya saka mu cikin wa]anda zata ceta. 3.LA{UBBANTA: Tana da la}ubba masu yawa,amma biyun nan su suka fi fice,sune Karimatu- Ahlulbayt da kuma
Ma’asuma.Wannan la}abi
na Ma’asuma yazo akan cewa Imam Ridah [AS] yayi mata la}abi da shi,wanda wannan yana alam ta, gayar
kamalar ta da kuma matsayin ta. 4.FALALAR
ZIYARAR KABARINTA: An samo daga Imam Ridah [AS] cewa duk wanda ya ziyarce
ta,Aljanna ta tabbata a gare shi.Haka nan makamancin wannan Hadisin,an samo
daga Imam Jawad [AS] cewa duk wanda ya ziyarce ta,Aljanna ta tabbata gare shi. 5.KARAMOMINTA:
Ma’asuma [AS] ta kasance ta na da
karamomi masu yawa,tun tana raye da bayan wafatinta,kai har wannan zamanin namu
kullum karamominta da]a bayyana suke.Za kaga masu ziyararta, zasu yi
tawassuli da ita kan bu}atocin su,kuma ka ga Allah ya biya musu bu}ata.marasa lafiya zaka ga an kawo su,ayi tawassuli da ita,ka ga Allah
ya basu lafiya.shi yasa wani daga cikin malaman tarihi yake cewa babu wani daga
cikin ‘ya’yan ma’asumai [AS] da yake da karamomi masu yawa kamar ta.Haka nan
yau a doran }asa
babu wata bai war Allah da take samun masu yawan ziyara kamar yadda take
samu.Domin idan mutum yaje Haramin ta zai ga dare da rana maziyar ta ne,daga
cikin karamominta daya bayyana a wannan zamanin
namu a shekarun baya,shine akwai
gyaran ainihin shi kabarin ta da
akayi ,aka za~i
manyan malamai daga ciki akwai Ayyatullah Najafi Almar’ashi,shine yake cewa
babu wani abun daya canza na likkafanin ta da kuma jikinta,yace kamar kace yau
aka sata.
6.JARABAWOYIN TA: Ma’asuma [AS] ta fuskanci
jarabawoyi masu yawa a rayuwarta,musamman a }arshen rayuwarta,misali bankwana da kuma zafin rabuwa da ]an uwanta Imam Ridah [AS] lokacin da zai
bar madina zuwa khurasan,tafiya wadda ba zai dawo ba,kamar yadda ya shaida
masu.Duk da sun yi bankwana,amma ta hau soron dakin na gidansu, tayi ta kallon
Imam Ridah [AS] har ta dai na ganinsa,kuma wannan shine }arshen ganinta da Imam Ridha,a gidan duniya domin bayan
haka basu sake ha]uwa ba.Ala}a da kuma sha}uwa na Imam Ridah [AS] da Sayyida
Ma’asuma,kamar ala}a da
kuma sha}uwa
na Imam Husain
[AS] da kuma Sayyida Zainab [AS]ne.
Bayan haka ga kuma jarabawar mahaifinta,
wato Imam kazim [AS] da ta gani na zamansa a kurkuku da kuma shahadarsa a ciki, da dai sauran jarabawowi masu yawa da ta fuskanta,wanda ba za’a iya kawo su ba saboda
gudun tsawaitawa.
7.ILIMINTA:Sayyida Ma’asuma [AS]
ta kasance mai yawan ilimi,akwai wani abin da ya ta~a faruwa,wanda ya nuna matsayinta a ilimi
wannan abin ko shi ne akwai wani lokacin da wasu daga cikin mabiyan Imam kazim
[AS] suka zo daga garinsu zuwa madina,domin su ga Imam kazim [AS] su gai she
shi,su kuma gabatar da wasu tambayoyi,
da suka zo madina suka isa gidan Imam kazim [AS]sai suka samu bai nan yayi
tafiya,sai suka rubuta tambayoyi suka ba
Sayyida Ma’asuma [AS] cewa in ya dawo ta bashi,kashe gari sai suka dawo suka samu bai dawo
ba,alhali su kuma suna son su koma garinsu a ranar,sai Sayyida Ma’asuma [AS] ta rubuta masu
amsoshin tambayoyin, suka amsa suna farin ciki.Kan hanyarsu ta komawa sai
suka ha]u
da Imam kazim [AS] yana dawowa sai suka shaida masa ma}asudin zuwan su da kuma abinda ya faru sai Imam
Kazim [AS] yace su kawo amsar takardar ya gani,bayan ya gani ya fa]i wannan kalmar sau uku, “ta fanshi
babanta”.
8.IBADARTA: Ta kasance mai yawan ibada.Hatta in da
take yin ibadar ta,salloli da makamantansu yana nan har yanzu a birnin }um ana ma kai ziyara wajen.
9.WAFATINTA: Ta rasu tana da shekaru 30 a
duniya,sababin rasuwar ta shine; ta bar madina ita da wasu ‘yan uwanta da nufin
su tafi khurasan wajen Imam Ridah [AS], akan hanya a wani waje mai suna SAWA rashin
lafiya ya kama ta,ta bu}aci a tafi zuwa }um,da suka isa kwanan ta 17 Allah yayi
mata rasuwa. Wannan dai a ta}aice kenan dangane da Tarihin Sayyida Ma’asuma[AS]
Bayan haka,anan insha Allah za’a kawo darussa 12
daga rayuwar Imam Ridah [AS] da nufin ya zama madubin da zamu dubi kawukanmu
dashi da kuma yin sa’ayi da kuma mujahada wajen ganin mun aikata su, domin su
amfane mu duniyarmu da kuma lahirarmu. 1.IBADARSA:
Imam Ridah [AS] ya kasance mai yawan ibadah,domin a zamaninsa babu wanda ya kai
shi yawan ibadah,ga misalan wasu daga cikin ibadodinsa.
A.SALLOLINSA: Imam Ridah [AS] ya kasance mai yawan
salla,yazo a tarihinsa cewa ko wane dare ya kan yi salla ta nafila raka’a dubu,wato
yana ]aya
daga cikin Imamai guda hu]u wanda a tarihin rayuwarsu yazo akan cewa kowane
rana suna salla raka’a dubu ta nafila.Wa]annan Imaman kuwa sune,
Imam Ali [AS],Imam Husain [AS],Imam Zainul Abidin [AS],da kuma Imam
Ridah [AS].ya ma ta~a ba wani daga cikin mabiyansa rigar sa,Imam Ridah
[AS] yace masa, “ka kiyaye wannan rigar domin na yi sallah dare dubu da ita,ko wane
dare raka’a dubu,kuma na sauke Alkur’ani sauka dubu da ita”.Mu duba wannan yawan ibada,
mu kuma kwatanta da kawukanmu mu ga gi~in dake tsakani. Haka
nan yazo a tarihinsa cewa da daddare ka]an yake bacci,mafi yawan darensa yakan raya
da ibadodine,wasu dararen ma, baki ]ayansu yakan raya sune.An tambayi ]aya daga cikin matayensa dangane da
ibadarsa,tace ya kasance idan yayi
sallar Asuba,yakan sallace ta a farkon lokacinta,ya kan yi ta’a}ibat [Azkar bayan sallah]bayan haka yayi sujuda
ba zai ]ago
kai ba har sai rana ta keto.Akwai ma wani da ya ta~a ganinsa bayan ya gama sallah,sai yaga yayi
sujuda,sai yaji yana tasbihi,sai shi wannan mutumi ya shiga lissafa tasbihin,
sai da ya lissafa guda 500,saannan yaga ya ]ago daga sujudar.
B.KARATUN - }UR,ANI-Imam Ridha[AS] ya kasance mai yawan
karatun }ur’ani,domin
yazo a tarihinsa cewa ya kan sauke shi a duk kwana ukku.Har ma ya kance;Da ina
so in sauke }asa
da kwana ukku da na sauke,amma in, ina karatunsa,duk ayar da na biya na kan
tunani a kan me ta sauka?kuma yaushe ta sauka?Saboda haka nake sauke shi kwana
ukku.’’Kuma yazo a tarinsa cewa,zantukansa baki ]aya da kuma amsoshin tambayoyi da aka yi
masa,ya kan bada su, da Ayoyin Alkur’ani ne.Wato shigen }issar wata bai war Allah, mai suna
FIDDHA,ta kasance tana yiwa Sayyida Fa]ima[AS]hidima ne,To yazo a tarihinta ta
shekara 30 bata yi magana da wani abu ba face ayoyin Ayoyin Alkur’ani.Misali ko
abu take so sai ta fa]e shi da wata aya da tayi kama dashi domin a
fahinta.A ta}aice
dai Imam Ridha[as]ya kasance mai yawan karatun
Alkur’ani.Mu duba abinda aka ambata a sama
na rigar daya ba, ]aya daga cikin sahabbansa,yace masa ya sauke
Alkur’ani da ita sauka dubu.
C.AZUMINSA: Imam Ridah [AS] ya kasance mai yawan
azumi,kuma azumi na kowane wata basu ku~uce masa,wato ya kasance yana lizimtarsu, a
zumin shahariyya[wata-wata] Sune Alhamis ]in farko na ko wane wata da kuma Alhamis ]in }arshe da kuma larabar farko ta goman
tsakiya,ya kance duk wanda ya lizimci wannan azumin,to kamar yana azumin kullum
ne.Kuma yazo a tarihinsa cewa in yayi azumi baya bu]e baki sai yayi sallah.
D.ADDU’O’IN SA:Imam Ridah [AS]ya kasance mai yawan
addu’oi,akwai adduoi da yawa wanda aka ruwaito daga wajensa.Mai bu}atar wa]annan addu’oi yana iya samun littafin addu’a mai suna SAHIFATUR -RIDHA,wanda
wani malami mai suna shaikh Jawad }ayyumiy, ya rubuta.Ana samun sahifa ]in. Sai
dai wani tambihi muhimmi anan shine;akwai wata addu’a da aka samo daga
Imam Rida [AS] wanda yayi umarni da a din ga biyawa, ga Sahibul-Amr wato Imam mahdi
[AF].Saboda haka ya na da muhimmanci ga kowannenmu ya lizimci biya addu’ar a}alla ko wace juma’a,addu’ar akwai ta cikin
littafin Mafatihul jinan,mutum ya duba ta gaban Dua’ul Nudba,to addu’a ta }arshen fasalin,to itace,zai ga ta soma da
“Allahumma idfa’a, an waliyyika wa
khalifatuka……..
E.AZKAR [IN SA:Imam Ridah [AS] ya kasance mai yawan
Azkar,ya mazo a tarihinsa cewa idan yayi sallar Asuba yakan zauna yayi
azkar,wato tasbihi da tamhidi da takbiri da tahlili,[Subhanallah -walhamdulillah wala ilaha illallah -wallahu
akbar],da kuma salati ga Manzon Allah da Alayensa [AS],ya kan yi haka har rana
ta keto.Wani tambihi anan shine idan mutum yayi sallar Asuba yana da gayar
muhimmanci ya kasance bai koma bacci ba har sai rana ta keto,domin sunna ce ta
Manzon Allah [S] da kuma Ahlulbayt [AS].Kuma akwai hadisai masu yawa da suka zo
da bayani dangane da falalar da ke tsakanin ketowar Alfijir zuwa ketowar
rana,da kuma kashedi dayin barci tsakaninsu.Alal misali ga wasu daga cikin
hadisan.An samo daga Imam Ba}ir [AS] yace, “Allah Ta’ala yana raba arziki tsakanin
ketowar Alfijir zuwa ketowar rana,saboda
haka kashedinku da yin barci tsakaninsu”.Haka
nan an samo daga Imam Rida [AS] dangane da tafsirin wannan ayar “Fal mu}assimati Amra”.yace, “Mala’iku suna raba arzikin
‘yan Adam tsakanin ketowar Alfijir zuwa ketowar rana,duk wanda yayi barci
tsakaninsu,to yayi barci daga arzikin sa”.Wato ba zai zamo daga cikin wa]anda za’a raba wa arziki na ranar ba. Har
ila yau an samo Hadisi daga wajen Imam Ba}ir [AS] yace, “Iblis la’antar Allah ta
tabbata gareshi yakan watsa [aika] rundunarsa lokacin ketowar rana da kuma
lokacin fa]uwarta.Saboda
haka ku yawaita Azkar [Ambaton Allah] a wa]annan lokuta guda biyu,kuma ku nemi tsarewar
Allah daga iblis da rundunarsa,kuma ku nemi tsari ga yaranku a wa]annan lokuta guda biyu [watau safe da kuma
yamma daga sharrori na zahiri da kuma ba]ini]. Imam Ba}ir [AS] ya }arasa
hadisin da cewa domin wa]annan lokuta guda biyu lokaci ne na gafala.Haka nan
yazo akan cewa Manzon Allah [S] idan yayi sallar Asuba yakan zauna inda yayi
sallar yana Azkar har rana ta fito,Akwai ma hadisin da Manzon Allah [S] yake
cewa “In zauna a In da nayi sallar Asuba, ina Azkar har zuwa hudowar rana,yafi soyuwa gare ni akan in ‘yanta bayi
guda hu]u”. An
samo dag Imam Hasan [AS] yace, “Naji Babana,Ali bn Abi [alib [AS] yana cewa,Manzon Allah[S] yace
duk mutumin daya zauna,a in da yayi sallar Asuba yana Azkar har rana ta
fito,to yana da ladar kamar wanda yayi aikin hajji,kuma Allah zai gafarta masa
zunuban daya gabatar”. Haka
nan daga Imam Ali [AS] yace, “ wanda yayi sallar Asuba ya zauna in da yayi
sallar, har rana ta keto,to wannan zai kasance hijabi tsakaninsa da wuta”.A ta}aice dai akwai hadisai masu yawa da suka zo
akan haka,shi yasa fu}aha suka tafi akan cewa makaruhi ne yin barci
tsakanin ketowar Alfijir zuwa ketowar rana,ana so mutum ya raya tsakaninsu da
ibada da kuma Azkar,karatun Alkur’ani,adduo’i, da dai makamantansu,haka nan
idan rana ta fito mustahabbi ne kafin ya tashi daga wajen yayi nafila raka’a
biyu,wato salatul Ishra},itama akwai hadisi akan haka wanda aka samu daga
Imam Hasan [AS].Da fatan za’a kiyaye wannan tambihi domin samun falalar dake
cikin lokacin,
2-AKHLA} [INSA:Imam Ridha[as] a wannan fage na Akla}, a zamaninsa ba wanda ya kai shi
ballantana ya wuce shi,ga misalan wasu daga cikin Akla} ]insa.
A.TAWALIU’NSA,Imam
Ridha [as]ya kasance mai gayar tawali’u,saboda ma yawan tawaliu’nsa,yazo a
tarihinsa cewa mafi yawan lokuta shi yake yima kan sa hidima.Haka nan idan yayi
ba}i
da kansa ya ke yi masu hidima.Akwai lokacin da yayi ba}o,sun zauna suna tattaunawa,fitilar dake
wajen sai ta ]an
canza,wato haskenta ya ragu,da yake da daddare ne,to sai shi wannan ba}o yayi nufin ya gyara fitilar,sai Imam
Ridha [as]ya tashi da kansa ya gyara fitilar.Sai yake cewa ba}on ; “Mu mutane ne wa]anda ba musa ba}inmu hidima.’’ Daga cikin
tawali’unsa,yazo akan cewa wani lokaci
ko abinci zai ci yakan kira bayinsa domin suci tare.Shine wani daga cikin
sahabbansa da ya ga haka,sai yace wa Imam Ridah [AS] “in zamo fansa gare ka,wa]annan ai da an zuba masu nasu daban su koma
gefe suci.” Da yake yawancin bayin nasa launin jikinsu ba}i ne,wato ba}ar fata, kamar yadda yazo a ruwayar,sai Imam
Rida [AS] ya bashi amsa da cewa, “Ai asasi
ubangiji ]aya
ne,uwa ]aya,uba
]aya.sakamako
akan asasin aiki ne” [wato ba’a launi ba].Haka nan daga cikin tawali’unsa,yazo
a tarihinsa cewa wani lokaci ko da, ]aya daga cikin bayinsa ya kira domin yasa
shi wani aiki,to idan bawan na cin abinci ne,yakan ce yaje ya gama sannan yazo.
B.KYAUTARSA:Imam Ridah [AS] ya
kasance mai yawan kyauta da kuma sadaka.Saboda ma gayar kyautarsa,da kuma sadakarsa,akwai wani da
yayi zamani dashi,yake cewa “Duk wani wanda ku kaji yana riya cewa yaga wanda
ya kai Imam Ridah [AS] kyauta da kuma sadaka,to kada ku gaskata shi.yazo a
tarihinsa cewa a lokacin yana khurasan, yaba da baki
]ayan
abinda ya mallaka ga matalauta.Haka nan ya kasance idan aka kai masa abinci,to
kafin ya fara ci, yakan ce a kawo masa kwano,sai ya ]ebi abincin yasa a kwanon,sai yace akai ma
miskinai.Haka nan daga cikin kyautarsa yazo akan cewa yakan sai, bayi ba don
kome ba,sai don kawai ya ‘yanta su daga bauta.A kan asasin haka yazo akan cewa
sai da ya’yanta bayi dubu. Akwai }issar wani da yazo aikin Hajji,sai ku]insa suka }are,ya zamanto abin da zai mai da shi
Madina ba shi dasu,sai ya samu Imam Ridah [AS] ya shaida masa halin da yake
ciki.Don haka yana ro}onsa ya taimaka masa da abinda zai koma garinsu,alabashi
in ya koma yayi sadaka da abinda ya taimaka masa ]in.Sai Imam Ridah [AS] yace ya zauna,ya
shiga gida ya ]auko
ku]i
dirhami ]ari
biyu ya bashi,yace masa gashi yayi guzuri da shi da kuma biyan bu}atunsa.In ya koma garinsu ba sai yayi sadakar ba,
da abinda yaba shi,da ma lokacin da wannan mutumin yazo, Imam Ridah [AS] yana
tare da wani sahabinsa mai suna Sulaimanil ja’afari,shine sai yace ma Imam Ridah [AS] “In
zamo fansa gareka,ha}i}a ka kyautata ma wannan mutumin, amma naga da
zaka bashi ka suturta fuskarka,me yasa haka?” Da yake kamar yadda yazo a }issar, da Imam Ridah [AS] ya shiga gida da
ya ]auko
ku]in
da zai mi}a
masa,sai ya mi}o
hannunsa ta }ofa
ya bashi,shine wannan sahabin sa yake tambaya akai.Sai Imam Ridah [AS] yace “Nayi
haka ne saboda gudun kada in ga }as}ancin tambaya a fuskarsa,domin na biya masa bu}ata.Ba kaji hadisin Manzon Allah [S] da yake
cewa ba,mai ~oye
kyawawan aiki ya nada lada kamar wanda yayi Hajji saba’in”.Da dai misalai da
yawa na irin kyautar Imam Ridah [AS] saboda gudun tsawaitawa ba za’a iya kawo
suba. C.AFUWARSA:Imam
Ridah [AS] ya kasance mai yawan afuwa ga wa]anda suka zalunce shi ko kuma suka yi masa abin da bai dace ba,akwai
wanda yayi masa abinda bai dace ba,shi da iyalansa,amma da Imam Ridah [AS] ya
samu sul]a
[iko] akansa sai yayi masa afuwa.A ta}aice dai kyawawan ]abi’u, a zamaninsa babu wanda yakai shi,kamar yadda wani wanda
yayi zamani dashi mai suna Ibrahim ]an Abbas ya tabbatar.Yake cewa ni ban ta~a
gani ko jin wanda yakai Imam Ridah]AS]kyawawan ]abi’u ba, ban ta~a ganin wani mutum ya kawo masa wata bu}ata, a wajensa bai biya masa ba.Kuma ban
ta~a ganin yana }yal-}yatar dariya
ba,dariyarsa itace murmushi,da dai sauran Akhla} na Imam Ridah da ya jero.
3.ILIMINSA:A wannan fage na ilimi, shima a
zamaninsa baki ]aya
ba wanda ya kai shi,kamar yadda wani da yayi zamani da shi yake cewa, “Ban ta~a ganin wanda ya kai Ali bn Musa Ridah
ilimi ba,kuma duk malamin da ya gan shi sai yayi masa wannnan shaida,irin
shaidar da na yi mashi”.Akwai ma lokacin
da khalifan Abbasawa a lokacin mai suna Ma’amun, ya tara malamai na fannoni
ilimi daban daban da malaman yahudawa da kuma nasara, akan suyi mu}abala da Imam Ridah [AS],baki ]ayansu.Daga }arshe kowannensu sai da ya tabbatar da
fifikon ilimin Imam Ridah [AS] akansa.kuma irin wannan majlisi,shi Ma’amun ]in ya sha shirya yin haka,watau ita mu}abalar a lokuta daban daban. Akwai ma lokacin da Imam Ridah
[AS] yake cewa, “Na kasance na kan zauna a rauda a cikin massallacin Manzon
Allah[S]Malaman Madina masu yawa(da suke karantarwa amassallancin)idan ]ayansu wata matsala ta shige masu duhu ko
kuma bai sani ba,sai suyi ishara zuwa
gareni da a zo a tambayeni,ni kuma sai in basu amsa.’’Haka nan Imam Kazim[AS]
ya kance ma ‘ya’yansa “Wannan ]an uwan naku Ali, Malami ne na Ahlul baiti[as]ku
tambaye shi dangane da mas’alolin addininku,Abinda ya fa]a maku to ku kiyaye,domin na ji babana, Ja’afar
]an
Muhammad[as]ba sau ]aya ba, ba sau biyu ba,yana ce mani lalle Malami
na gidan Manzon Allah[s]yana tsatson ka,ina ma dai na riske shi.Sunan sa yayi muwafa}a da na Amiru muminin.’’Mu duba shadar
kakan sa Imam Sadi}[as]gare shi tun gabanin a haife shi.Ya ambace shi
da kalmar MALAM.Ikon Allah tsakanin rasuwar Imam Sadi}[as]da kuma haihuwar Imam Ridha [as]kusan
kwanaki goma sha biyar ne. Haka
nan yazo akan cewa tafiyar da suka yi daga madina zuwa khurasan,Birni da }auye da suka yada zango jama’a kan zo suyi
tambayoyi na mas’aloli na Addini,ya kan basu amsa,da kuma fa]a masu Hadisai na Manzon Allah[s]da kuma
Ahlul-Bait[as]Saboda haka nema Ma’amun khalifan Abbasawa,abubuwan da yaji kuma
ya gani daga Imam Ridha[as] na ibada da kuma ilmi,sai Ma’amun ]in,yace
wannan shine mafi ililmi a bayan }asa.mu duba shaidar ma}iyinsa,watau wannan khalifa na Abbasawa,shaidar da yayi
masa na fifikon iliminsa a doron }asa a lokacin.
Akwai ma wani da yake cewa bai ta~a ganin an tambayi Imam Ridha akan wani abu
ba,face ya san abun,da dai misalai da yawa na ilimin Imam Ridha [as]wanda baza
a iya kawo suba, saboda gudun tsawaitawa.
4.ZUHUDUNSA:Watau gudun duniyarsa,Imam Ridah [AS]
a wannan fage ya kai mustawa aliya,wanda a zamaninsa babu wanda ya kai shi a
wannan fage na gudun duniya,akwai }issar wata kuyanga [baiwa] ta khalifan
abbasawa Ma’amun, tana zaune a gidan Ma’amun ]in ne,sai ya bada ita ga Imam Ridah
[AS].Sai ta koma gidansa,shine take cewa lokacin da take gidan ma’amun tana
cikin wal-wala da jin da]i na abinci da abin sha,da ku]a]e,amma da ta koma gidan Imam Ridah [AS] duk
sai ta rasa wa]annan
abubuwa na jin da]i.Tace,kuma
baya ga haka a gidan akwai wata mata, aikinta shine ta dinga tada su sallar
tahajjud [sallar dare],tace to wannan shi yafi tsanani gare ni [watau tashi
sallar].Tace, “Ina ta fata da burin in bar gidan,daga }arshe Imam Ridah [AS] ya bada ni ga
wani.Da na koma gidansa sai na kasance kamar an
sani a Aljannah.” Daga
}issar
wannan mata zamu iya fahimtar rayuwa ta zuhudu na Imam Ridah [AS].Akwai misalai
da yawa,amma gudun tsawaitawa za’a ta}aita da wannan.
5.ALA{ARSA DA SHI’ARSA[mabiyansa]: Akwai wani da ake cema
Musa ]an
sayyar yace, “na kasance tare da Imam Ridah [AS],mun kusan isa [us [Mash-had] sai muka ga janaza.Sai Imam
Ridah [AS]ya nufaci wajen janazar,sai yace min, “ya Musa ]an sayyar duk wanda ya raka janaza ta ]an shi’a daga cikin shi’armu,to zai fita daga zunubansa kamar ranar da
mahaifiyar sa ta haife shi.” watau zai dawo bai da
zunubi ko guda]. Lokacin
da aka zo za’asa Mamacin a kabari,kafin sa shi sai Imam Ridah [AS] ya ta~a }irjinsa yace, “ya wane ]an wane albishirin ka da aljannah,babu tsoro gare ka bayan wannan
lokacin.” Sai shi wannan da ke tare da Imam Ridah [AS] yace in zama
fansa gare ka,kasan wannan mutumin ne? Domin wallahi baka ta~a
tako wannan }asa ba gabanin yau.” Sai Imam Ridah [AS] yace masa,
“ya Musa ]an sayyar,shin baka san cewa, mu A’imma ana
bijirowa [kawo] da ayyukan shi’armu gare mu safe da yamma ba? Abinda suka ta}aita
na ayyukansu,mu ro}a masu Allah ya
yafe masu,abin da suka aikata mai kyau,mu ro}a
masu Allah ya }ara masu.” A wannan al’amari zamu ga
akwai darussa masu yawa a ciki ,amma ga guda uku daga ciki:
1.Ala}ar
Imam na kowane Zamani da shi’arsa,domin
shi wannan mutum da yake tare da Imam Ridah [AS] yana mamakin ina yasan wannan
mutumin, alhali bai ta~a zuwa wannan
waje ba,wannan kuma yana nuna wilaya Tak-winiyya da kuma Wilaya Tashri’iyya da A’imma [AS] suke dashi.Insha Allah wani
lokaci za’a yi bayani dangane da wa]annan wilaya guda
biyu na A’imma [AS] a muhallinsu.
2.Tausayin Imamin
kowane zamani akan mabiyansa na zamaninsa,su duba in an kai, aikin da bai dace ba ko kuma aka ta}aita,su
ro}i
Allah ya yafe wa mutum.
3.Wanda yake yana da
gayar muhimmanci, shine mutum ya san da cewa,duk aikin da yake aikatawa mai
kyau da kuma mara kyau,to akan kai shi ga Imamin zamaninsa.mu a wannan zamanin
namu akan kai shi ga Imam Mahdi [AS] ne,saboda haka kowannen mu yayi tunanin
ayyukan da yake aikatawa,ayyuka ne da in an kai ma Imam Mahdi [AS] zai yi farin
ciki dasu ko kuma zai yi ba}in ciki dasu?
Domin tabbas kai ayyukan bayi ga Ma’asumai [AS] wani abu ne wanda yazo a
ruwayo yin hadisai masu yawa.Wanda shima wannan wani lokaci a muhallinsa za’a
kawo wa]annan
hadisai,saboda haka yana da muhimmanci kowannen mu ya lizimci ayyukan da zasu
kyautata ala}arsa da Imaminsa,ba wa]anda
zasu raunana ala}arsa
da shi ba.kamar fa]in wata magana ta
Ayatullah Bahjati yana cewa, “kada mu dinga fa]i
da harsunan mu,Allah ya gaggauta bayyanar Imam Mahdi [AS],amma kuma da ayyukan
mu muna jinkintar da zuwansa.”
6.JARABAWOWINSA:Imam
Ridah [AS] ya fuskanci jarabawowi masu yawa a rayuwarsa,kamar sauran A’imma na Ahlulbayt
[AS] da suka gabace shi da kuma wa]anda suka biyo
bayansa.
Domin idan mutum
ya bibiyi tarihin Imamai ]aya bayan ]aya,
zai ga kowannensu ya fuskanci jarabawa iri biyu.ta farko jarabawa ta amma,ta
biyu jarabawa ta khassa.Jarabawa ta amma itace jarabawar da dukkan Imamai sha
biyu sun yi musharaka a ciki.Misali A- jarabawar }wacen
tafi da iko daga gare su wanda ha}}insu ne,wanda
Allah [T] ya basu. B-Zaluntar su da kuma mabiyansu da kuma sauran jama’a suna ganin haka,amma babu yadda za suyi. C- Tasarrufi a cikin shi Addinin.
Watau masu iko su }ago
abu ko su jirkita yadda yake,su sa shi a cikin addini,kuma su gina mutane akan
haka, har saboda ginuwa akai mutane su ]auka
Addini ne.Da yake nan ba muhallinsa ba ne da an kawo misalai akai.To,idan mutum
ya duba wa]annan misalai guda ukun da aka kawo
zai ga duk A’imma [AS] sun yi tarayya wajen wannan matsaloli da aka haifar. Jarabawa
ta khassa itace wadda kowa ne Imami ya fuskanta
shi }ashin
kansa daga masu tafi da iko na zamaninsa,kuma a wata munasaba ta wafatin Imam
Ridah [AS],za’a kawo jarabawa wadda ta ke~anta da
shi.Wannan jarabawa itace ta “ Waliyyul-Ahd” watau na]a
shi a matsayin khalifa mai jiran gado wanda khalifan Abbasawa Ma’amun
yayi,wanda in mutum ya dubi abin a zahiran ce,zai ]auka
ko abu mai kyau Ma’amun yayi,alhali abin ba haka nan yake ba,a ba]ininsa
makirci ne da kuma yaudara.Asasin wannan abu ya taso ne daga shi wannan khalifa
na Abbasawa Ma’amun,lokacin daya hau
khalifanci yaga matsaloli sun yi masa yawa,ga matsalar ]an
uwansa mai suna Amin,wanda yana ya}ar sa domin ya tunku]e
shi shi ya hau.Ga kuma ta wa]anda suka yi masa
tawaye daga sassa daban daban a lokacin,musamman ma daga ~angaren
mabiya Ahlulbait [AS],Saboda abin da baban shi Ma’amun watau Harunar-Rashid,
yayi na kashe Imam Kazim [AS] a kurkuku,ta hanyar sa masa guba.To,wa]annan
matsaloli daya ga sun yi masa yawa,kuma matsalar da yafi jin tsoro daga cikin wa]annan
matsaloli,ita ce ta ~angaren
mabiya Ahlulbait [AS],sai yayi tunani shi a }ashin
kansa ba tare da yayi shawara da kowa ba,na
bari ya ]auko Imam Ridah
[AS] daga madina ya kawo shi khurasan,lokacin itace cibiyar tafi da ikonsa.Domin ya bashi mu}ami
na khalifa mai jiran gado. Manufarsa
~oyayya
itace domin ya kwantar da wancan tawaye da mabiya Ahlulbait [AS] sukayi a sassa
daban daban, wanda daga }arshe
idan abubuwa suka lafa,komai ya koma dai dai na ikonsa sai ya kashe Imam Ridah
[AS] ta hanyar sa masa guba.Wannan ‘plan’ ]in shi a }ashin
kansa ya kitsa.Imam Ridah [AS] ne ya tona asirin haka.lokacin daya ha]u
dashi yace masa,nasan manufarka.Sai Ma’amun yace masa mece ce manufata? Imam
Ridah [AS] ya fa]a masa,nan take ya daburce ya fusata,saboda ya san wannan abin bai fa]a
wa kowa ba,amma gashi Imam Ridah [AS] ya fa]i,don
hatta ‘yan uwansa na jini,lokacin da ya ba Imam Ridah [AS] wannan matsayi,sun maganganu me yasa zai yi haka? Don bai bayyana wa kowa manufarsa
ba. Bayan
Ma’amun ya kitsa wannan tunani a zuciyarsa,sai ya fara ]aukar
mataki na aiwatar dashi.Saboda haka sai ya aika aje madina a zo masa da Imam
Ridah [AS].da ‘yan sa}o suka isa
madina,suka samu Imam Ridah [AS] suka shaida masa sa}on
Ma’amu,jin haka sai Imam Ridah [AS] ya tafi masallacin Manzon Allah [S] domin
ya yi ban kwana dashi,saboda yasan }arshe yazo,kuma
zamansa a birnin Manzo ya }are.Saboda
haka yaje kabarin Manzon Allah [S] yayi bankwana dashi,yana kuka sai ya fito
masallacin,sai ya sake komawa domin sake bankwana,yana bankwana da Manzon Allah
yana kuka.Har wani daga cikin mabiyansa,ya gan shi yayi masa sallama Imam Ridah
[AS] ya amsa masa sallamar,ya kuma ce
masa ka ziyarce ni domin ni za’a raba ni da birnin Manzon Allah [S]. Zan rasu a
can ina ba}o.Bayan haka ya koma gida ya tara
iyalansa baki ]aya yayi masu jawabi.Acikin jawabin
nasa yace masu “TO zan tafi bazan
dawo ba har abada,saboda haka mai juyayi
yayi juyayi,mai kuka yayi kuka a gare ni.”
Bayan haka ya raba masu ku]i,Dirhami dubu
goma sha biyu.Lokacin da zai fita ya dubi ]ansa,guda
]aya
da yake dashi watau Imam Jawad [AS] lokacin ya nada shekaru bakwai a duniya,ya
kama hannunsa ya shiga dashi masallacin Manzon Allah [S], ya isa kabarinsa,ya
kama hannun wannan ]a nasa ya aza a
kabarin Manzon Allah [S] yace “to ya Manzon Allah [S] gashi nan ajiya gare ka.” Haka ya bar madina birnin Manzon
Allah [S],kuma ya bar mahaifiyarsa da kuma iyalansa baki ]aya,suka
kama hanya dashi zuwa khurasan.[khurasan tana cikin Iran ne yanzu] Don
ma makirci da dasisa irin na Ma’amun,cikin umurnin daya ba wa]anda
ya aika suzo da Imam Ridah [AS] har da ce masu,kada ku biyo dashi ta gari kaza
da kaza,ya ambaci wasu garuruwa,watau duk garin da ya san akwai ‘yan shi’a da yawa,yace
kada a biyo dashi ta nan,daga ciki har da birnin-}um.Mu
duba irin wannan dasisa da makirci,haka suka yi watanni har suka isa
khurasan.Kuma duk wanda Allah [T] yasa yaga wannan waje,ko ya san yanda wannan
yanki yake da Hamada da kuma tsanuka da zafin yana yi,wani wajen kuma sanyin
yana yi, zai fahimci matsanancin wahalar da Imam Ridah [AS] ya sha a tafiyar.Domin
zan iya tunawa zuwana Iran na
farko,kimanin shekaru goma sha bakwai da
suka wuce,lokacin da Malam ya tura mu karatu a birnin }um mu
goma sha biyu,Allah yasa mun tafi daga }um zuwa mashhad a
mota,tafiyar kimanin awa goma sha ]aya ce.To,a lokacin
da ake tafiyar yadda naga tsaunuka daban daban,ga Hamada wani wajen,ga tsananin
sanyi,akwai garin da muka biyo,dole tasa aka tsaya muka sa kayayyakin
sanyi,sa’annan aka ci gaba da tafiya.To,lokacin abinda nake tunani a raina
shine,yanzu a wannan yana yi na Hamada da tsaunuka da sanyi da zafi tun daga madina har ya zuwa mashhad,watau
khurasan aka biyo da Imam Ridah [AS].A irin wannan yanayi ne ‘yan uwansa na
jini bayan shekara ]aya da
tafiyarsa,suka kamo hanya daga madina da nufin su same shi a khurasan.Wa sunsu
akan hanya Allah [T] yayi masu rasuwa aka binne su anan, har yanzu kabur-buransu
na nan,in mutum yabi ta hanyoyi zai
gani,wanda wannan tafiya har yau har gobe,idan na tuna da ita,sai naji
tasirinta a zuciyata.Wannan a ta}aice dai yana
nuna irin wahalhalu da wa]annan bayin Allah
suka sha a tafiyar.
Sayyida Ma’asuma [AS]
akan hanyar su,ta zuwa khurasan,domin zuwa wajen Imam Ridha[AS] rashin lafiya ya
kamata,wani waje da ake ce ma Sawa.Ta
tambaya,tsakanin nan da }um, far-sakhi nawa ne?
Aka ce mata goma,tace to a }arasa da ita }um.Kuma
wani abin ba}inciki da ban takaici da ya faru
gare su,da suka iso wannan gari na Sawa.Shine Hujumin da akayi a kansu,wanda ya kai
ga an kashe wasu daga ciki,wasu kuma aka ji masu ciwo.Wasu malaman Tarihi sun
tafi akan cewa,wannan rashin lafiya nata,yana da ala}a
da wannan mummunan abin da aka yi masu,mu duba mu gani zuriyar Manzon Allah [S]
sun taso daga madina su kimanin 30 kamar yadda yazo a ruwaya aka tare su a
hanya akayi masu wannan mummunan abu.Malaman tarihi sun yi tambaya kan wannan
abu cewa,Ma’amun ne ya kitsa ayi wannan abu,ko ko su mutanen Sawa ne suka yi?
Domin yazo a tarihi cewa su mutanen Sawa a lokacin, sun kasance suna gayar gaba
da }iyayya
da Ahlulbait [AS].Ko ma dai mene ne,musabbabin wannan aika-aika da akayi ma su
Sayyida Ma’asuma[AS].To yau ina Ma’amun ]in?ina
mulkin nasa?ina kuma wa]anda ya mulka? Bayan isar su Imam Ridah [AS]
khurasan,Ma’amun ya gana dashi,ya shaida masa abinda yake bu}ata,na
ya kasance khalifa mai jiran gado.Imam
Ridah [AS] yace masa a’a,sai Ma’amun yace masa ko dai ya amshi wannan matsayi
na Waliyyul-Ahd, ko kuma ya kashe
shi.Imam Ridah [AS] ya amsa,amma da shara]in cewa ba zai
zartar da komai ba.Wannan ya kasance babbar jarabawa ga Imam Ridah [AS] saboda
yasan meye manufar Ma’amun kan wannan abu. sHaka
Imam Ridah [AS] ya zauna a cikin wannan jarabawa,wadda sai da ta kai koda wane
lokaci in ya dawo daga masallacin juma’a,
yakan ]aga
hannu sama yace “Ya Ubangiji idan faraj ]ina yana ga
rasuwata,to ka gaggauta wafatina.” An ce ko da wane lokaci yana cikin damuwa da
kuma ba}in
ciki har ya koma ga Allah Ta’ala.Daga }arshe Ma’amun Yasa
masa guba a inabi,a wata ruwaya a rumman,wanda hakan yayi sanadiyar
shahadarsa.Ya rasu yana da shekara 55 a duniya.Sauran darussan shida,insha
Allah sai wata munasabar za’a ]ora akai.
No comments:
Post a Comment