Sunday 3 February 2013

Darussa 12 daga rayuwar Imam Muhammad Al-Ba}ir [AS].


Wannan wata da muke ciki na zulhijja,bakwai gare shine wafatin Imam Muhammad Ba}ir [AS] domin  ya rasu ne ranar litinin  7 ga zulhijja shekara ta 114 bayan hijra.Ya rasu ya na da shekaru 57 a duniya,muddan imamancinsa kuma shekara 19.Kabarinsa yana madina ne,watau a Ba}i’a.Kuma kamar yadda aka sani a jerin }idaya na Imamai goma sha biyu,shine Imam na biyar.Kuma shi ]ane ga Imam Zainul Abidin [AS] ]an Imam Husain [AS].
Ya rayu tare da kakansa ,watau Imam Husain [AS] shekara hu]u.Ya ma zo akan cewa wa}i’ar karbala a gaban idonsa ta gudana,wato yana wajen.Saboda haka duk abubuwan da suka biyo bayan wa}i’ar  karbala na kai su sayyida  Zainab [AS] zuwa kufa,daga nan zuwa sham,daga nan kuma dawowa madina,da kuma abinda ita wannan tafiya da aka yi da su  ta }unsa,na cutarwa da kuma musgunawa,duk tare dashi aka fuskanci wa]annan matsaloli,lokacin yana da shekara hu]u a duniya.                                                        
Imam Ba}ir [AS] yayi kama da Manzon Allah [S] sosai,shi yasa daga cikin la}ubbansa ana ce mashi “SHABIH”Akwai ma ]aya daga cikin sahabban Manzon Allah [S] wanda ake cewa Jabir ]an Abdullahi Al-ansari [RA] da yace, Manzon Allah [S] yace mini “Ya jabir lallai zaka rayu har sai ka ga wani daga cikin jikoki na da yayi kama dani,sunansa kamar sunana ne.Ana ce masa Muhammad.Idan ka gan shi,ka isar da sallamata gare shi”.Sa’annan Manzon Allah [S] yace masa, “Ka sani wanzuwarka bayan ka gan shi ka]an ne”watau tsakanin ganinsa dashi ,da kuma rasuwar sa ba nisa.Wa]annan ababe da Manzon Allah [S] ya fa]a ma sahabinsa,haka ko suka faru.Allah [T] yayi masa tsawon rai har sai da yaga Imam Ba}ir [AS],ya kuma isar da wannan sallama gare shi,kuma bayan daya ganshi bai jima ba,Allah [T] yayi masa rasuwa.Har ma akwai fa]in Jabir da yake cewa “Allah [T] ya jinkirta mani ajali na,har naga Ba}ir [AS] na isar masa da sallamar kakansa Manzon Allah [S]”.Kuma  Jabir ]an Abdullahi Al-ansari [RA] shine farkon wanda ya ziyarci kabarin Imam Husain [AS] a karbala bayan shahadar sa da kwana arba’in.Tare dashi Jabir a wannan ziyara akwai wani da ake cema A]a’a ,ya na daga cikin tabi’ai,sa’annan kuma da wasu daga cikin bani Hashim.                                                                                                                                                                                      Kuma kamar yadda yazo a littafan tarihi,su  Sayyida Zainab [AS],akan hanyar su ta dawowa daga sham zuwa madina sun biyo ta karbala,sun iso karbala ne 20 ga watan safar,watau ranar bisa ikon Allah [T] tayi muwafa}a da ranar arba’in ]in Imam Husain [AS].Saboda haka ko da su Sayyida  Zainab [AS] suka iso  kabarin Imam Husain [AS] sun samu su Jabir [RA]  a wurin.Haka wa]annan bayin Allah [T] baki ]ayan su suka zauna a wajen,su kayi juyayi da kuka da kuma zaman makoki har na tsawon kwana uku,a wata ruwaya.Sa’annan suka kama hanya zuwa madina.Yazo akan cewa lokacin da  Sayyida Zainab [AS] ta iso kabarin Imam Husain [AS] ta fashe da kuka tana fa]in “WA AKAH,WA AKAH,WA AKAH!”.                                        Imam Ba}ir [AS] an haife shi a madina,ya rayu a madina,ya rasu a madina.An haife shi a ranar juma’a,a wata ruwaya ranar litinin ]aya ga watan Rajab,hijira na da shekara 57.Sunan mahaifiyarsa Fatima ‘yar Imam Hasan.Yazo akan cewa shine ka]ai wanda ya ha]a irin wannan nasabar na cewa mahaifiyarsa itace Fatima ‘yar Imam Hasan [AS],mahaifinsa Imam Sajjad [AS] ]an Imam Husain [AS].Kuma ita wannan mahaifiyar tasa yazo daga Imam Sadi} [AS] cewa a zuriyar Imam Hasan [AS] baki ]aya babu mace kamar ta.Har ma  siffan ta da cewa ita Siddi}a ce.Kuma idan mutum ya bibiyi tarihin rayuwarta zai ga akwai karamomi da yawa da suka bayyana daga gareta.Alal misali ga wasu daga ciki:                                                                                                                                                                                                         1.Yazo daga Imam Ba}ir [AS] yace, “akwai lokacin da mahaifiyarsa tana zaune a jikin Katanga ,ashe Katangar ta tsage ,zata fa]i.Ganin haka sai mahaifiyarsa tayi ishara da hannunta ga katangar  tace,a’a da ha}}in  Mustafa,Allah bai yi miki izinin ki fa]i ba”.Haka katangar ta tsaya a karkace sai da ta bar wajen ta fa]i.
                2.Lokacin da take ]auke da cikin Imam Ba}ir [AS] ta kan ji sautin Magana a cikin gida ana ce mata albishirinki da yaro mai ilimi,mai ha}uri,ta kan ji haka,amma kuma bata ganin mai maganar.
                3.Haka nan yazo akan cewa a daren da zata haifi Imam Ba}ir [AS],wani haske ya bayyana wanda ya haskaka dukkan gidan, amma ikon Allah ba mai ganin hasken daga ita sai mahaifinsa,watau Imam Zainul Abidin [AS],da dai sauran karamomin ta wa]anda ba za’a iya kawo su ba, saboda gudun tsawaitawa.
                Imam Ba}ir [AS] anai  masa kinaya da Abu ja’afar.Ya nada la}ubba masu yawa,amma wanda yafi shahara shine wannan lakabi nasa na Al-Ba}ir.Kuma Manzon Allah [S] ne ya yi masa wannan la}abi da haka.An ruwaito daga Shaikh Sadu}  cewa an tambayi Jabir ]an Ju’ufiy me yasa ake ce masa  Ba}ir ? Sai yace, “saboda ya tsaga ilimi tsagawa,ya bayyanar da shi bayyanarwa.A takaice wannan la}abi nasa na Al-ba}ir  yana  alamta  yawan iliminsa da kuma fito da  ba]ini  na ilimi  domin bayyanar dasu.Kuma tabbas idan mutum ya bibiyi tarihinsa  a fagen ilimi za iga haka,domin hatta sahabbban Manzon Allah [S] wa]anda Allah yayi wa tsawon kwana da suka yi zamani dashi sun amfana da ilimin sa kamar yadda zamu ga haka nan gaba,a bayanin iliminsa [AS].Imam Ba}ir [AS] yana da ‘ya’ya bakwai,maza biyar,mata biyu.Mazan sune,Imam Sadi} [AS],Ali,Abdallah,Ibrahim,da kuma Ubaidullah.Matan sune,Zainab,da kuma ummu salma.Imam Ba}ir [AS] ya rayu tare da mahaifinsa kusan shekaru 25.                                                                                                                                    
Bayan wannan shimfi]a na janibobi daban daban da suke  da ala}a da Imam Ba}ir [AS],sai kuma Darussa sha biyu daga rayuwarsa da aka saba gabatarwa a irin wannan munasabobi na wafatin A’imma na Ahlul bayt [AS],da nufin su kasance madubin da zamu dubi kawukanmu da kuma yin mujahada wajen ganin cewa mun ]abba}a su gwargwadon ikon kowannenmu.
1.       IBADARSA:Imam Ba}ir [AS] ya kasance mai yawan ibada.Ga misalan wasu daga cikin ibadodinsa.A -Azkar ]insa,ya kasance mai yawan zikiri,kamar yadda aka ruwaito haka daga Imam Sadi} [AS] yace “Babana ya kasance mai yawan zikiri.Na kasance in muna tafiya tare dashi sai in ji yana zikiri,in muna cin abinci sai inji yana zikiri.Haka nan ko tattaunawa yake da mutane wannan bai shagaltar dashi daga zikirin Allah [T].Na kasance ina ganin harshensa yana yawan fa]in “La ilaha illallah”.Imam Sadi} [AS] yaci gaba da cewa,ya kasance yakan tara mu bayan sallar asuba,ya umurce mu da yin azkar har rana ta fito.Wanda ya iya karanta Alkur’ani daga cikin mu sai yace yayi karatun Alkur’ani,wanda bai iya ba sai yace yayi zikiri.                                                      B.Sallolinsa:Imam Ba}ir [AS] ya kasance kowace rana ya kanyi sallah ta nafila 150,duk da cewa mafi yawan lokutansa ya kasance yana karantarwa ne da kuma amsa tambayoyin masu tambaya,na kusa da kuma na nesa.Amma duk da haka kowace rana ya kanyi  wa]annan nafiloli C.Karatun Al}ur’ani:kuma ya kasance mai yawan karatun Al}ur’ani,kuma ya kasance mai yawan son sauraron karatun Al}ur’ani.Wani lokaci ya kasance yakan sa wani daga cikin mabiyansa ya karanta masa Al}ur’ani,watau domin ya saurara.Sai dai wani tambihi a nan dangane da karatun }ur’ani, shine yana da gayar muhimmanci ga  kowannenmu ya zamanto yana da wani tsari na lokaci daya tsara ma kansa na karatun }ur’ani ta fuskoki guda uku.Fuska ta farko ya zamanto akwai wani lokaci daya ke~e ma kansa na karatun shi Al}ur’ani kowace rana,ta yadda wannan zai sa ya sauke shi a}alla kowane wata sau ]aya.Wato kada ace wata ya kama har ya }are bai sauke Al}ur’ani ba.Kuma wannan sassau}a ne in dai har mutum zai tsara lokacinsa.In ma saboda yawan shugul a cikin yini,to mutum ya yasa karatun a cikin sallar Tahajjud ]insa.ko da ma bai haddace Al}ur’ani ba,to ya dinga amfani da mus’hafi wajen Tahajjud ]insa.Domin dai haka ya ba shi damar ya dinga saukewa sau ]aya ko fiye da haka a kowane wata.Akwai wani da na sani a haka  ]in  yakan sauke duk kwana uku.A Tahajjud Raka’a 8,wato in ka ]ebe shafa’i da wuturi da kuma raka’a 2 na bu]ewa.Da yake yazo a hadisi cewa,a na son mutum yayi raka,a biyu kafin ya fara sallar tahajjud ]in sa.Raka’a ta farko ana son mutum ya biya }ul-huwallahu ]aya,wato bayan fatiha.raka’a ta biyu bayan fatiha }ul-ya ayyuhal- kafirun ]aya.bayan sallama sai mutum ya Tashi,ya fara tahajjud ]insa. .Kaga kenan idan a wata mutum sau ]aya yake saukewa a kowane wata,to a wa]annan raka’o’i  8,sai ya biya izu biyu.wato kowace raka’a ya  dinga biya rubu’in  izu .In kuma duk mako yake saukewa sai ya dinga biya izu 8 a Tahajjud ]in,wato a kowace raka’a  ya biya izu ]aya kenan.Idan kuma aduk kwana ukku yake saukewa ,sai ya dun ga biya izu 2o a raka’a 8 ]in,ko wace raka’a 2, izu 5,raka’a ta farko izu 3,raka’a ta biyu izu 2,kamar yadda wancan ]an’uwan ya keyi,wanda na ambata a sama cewa yana saukewa a duk kwana ukku.Idan kuma Tahajjud ]insa ta samu matsala wani lokaci, sai ya biya abinda ya saba karantawa na Alkur’ani ]in a cikin yini.                                                                                Fuska ta biyu shine ya zamanto akwai lokacin daya ke~e ma kansa na sauraron karatun Al}ur’ani.Alhamdulillah a wannan zamani ga kasusuwa na CD ne da MP3 da makamantansu na makarantan Alkur’ani daban-daban.Sai wanda mutum yake bu}ata, kuma izu sittin cikakke.Sai mutum ya samu wanda yake bu}ata na makarantan,ya kasance lokaci bayan lokaci,yana sauraron karatun, ya ]auko sauraron karatun Alkur’ani ]in tun daga suratul Ba}ara har zuwa Nasi.Ta yadda dai a}alla ko sau ]aya a shekara ya sauke Alkur’ani, ta hanyar sauraro da kunnensa.Kuma nasan mutum zai yi farin ciki gobe }iyama,kunnensa yaba da shaida cewa ya sauke Alkur’ani dashi ta hanyar sauraro,banda kuma ladar da mutum zai samu na falalar sauraron karatun Alkur’ani.                                                                                                                                                             Fuska ta uku,ya zamanto akwai lokacin daya ke~e ma kansa na haddar Al}ur’ani.In kuma Allah [T] yayi masa muwafa}a da haddacewa,sai lokacin ya mai dashi na biya haddarsa.Idan Kuma bai haddace ba, kuma  ya kai wata mustawa a shekaru,wato shekaru sun yi nisa,to bai makara ba.Yana iya farawa koda ko aya ]aya ]aya ko fiye da haka,yake haddacewa ko wace rana,idan ya tsayu akan haka,har ajalinsa  ya sauka,to zai koma ga Allah [T] a matsayin wanda yake da niyyar haddace Al}ur’ani,wanda kuma wannan niyyar a bisa lu]ufi na Allah [T] na iya zama sanadiyyar da Allah [T] zai sa mutumin cikin ajin bayinsa mahaddata Al}ur’ani  gobe }iyama,sa~anin ko in mutum na ganin shekaru sunyi nisa bai yi niyyar haka ]in ba.Saboda haka mutum yayi niyya ]in,ya fara.Kuma wa]annan fuskoki guda uku da aka ambata,watau na karatun Al}ur’ani da sauraron sa da kuma haddar sa, akwai hadisai masu yawa da suka zo daga Manzon Allah [S] da kuma Ahlulbayt [AS] na falalar kowannensu,amma saboda gudun tsawaitawa ba za’a iya kawo suba.Amma ga mai bu}atar ganin wa]annan hadisai yana iya duba littafin Mahajjatul Baida’a na Faidul-Kashani,wanda littafin Ta’ali}i ne yayi ga littafin Ihya’ul-ulumuddin na Gazzali.
2.       JARABAWOWINSA:Imam Ba}ir [AS] kamar yadda A’imma wa]anda suka gabace shi da kuma wa]anda suka biyo bayansa suka fuskanci jarabawowi daban-daban,ta kuma fuskoki daban-daban a zamunansu,musamman ma ta fuskar masu tafi da iko,to shima ya fuskanci irin wa]annan jarabawowin.Daga cikin jarabawowin daya fuskanta ta fuskacin masu tafi da iko akwai zaman kurkuku,domin in mutum ya bibiyi tarihin Imamai zai ga guda hu]u ne suka zauna a kurkuku.Sune,Imam Ba}ir [AS],Imam Kazim [AS],Imam Hadi [AS],Imam Al-Askari [AS].Wato kenan Imam Ba}ir [AS] shine Imami na farko da masu tafi da iko suka kama da nufin sawa a kurkuku,kuma suka sa.Wannan ya auku a mulkin Khalifan Umayyawa mai suna Hisham ]an Abdulmalik.Da yake Imam Ba}ir [AS] yayi zamani da khalifofin Umayyawa guda biyar,sune Walid ]an Abdulmalik,wanda ya kekketa Alkur’ani, yace in yaje wajen Allah [T] yace Walid ne ya kekketa shi.Wannan yana nan a littafan tarihi,musamman ma na madrasah ]in Ahlus-Sunnah.,Sai kuma Sulaiman ]an Abdulmalik,sai Umar ]an AbdulAziz,sai Yazid ]an Abdulmalik,sai kuma na }arshe Hisham ]an Abdulmalik.To,a cikin wa]annan guda biyar, wanda yafi cutarwa da kuma gallazawa ga Imam Ba}ir [AS] shine Hisham.A lokacinsa ne yasa aka ]auko Imam Ba}ir [AS] daga madina zuwa sham.Bayan an kawo shi sham,aka kai shi fada wajen Hisham.Bayan tattaunawa da yayi dashi,daga }arshe yace akai shi kurkuku.Zaman Imam Ba}ir [AS] a kurkuku,sai ya zama sabab,ba wai kawai na samun canjin  tunani ga wa]anda suke cikin kurkukun ba,a’a ya zamanto sanadiyyar haka sun yi tamassuki da wilaya ]in Ahlulbayt [AS],watau sun zamo ‘yan shi’a.Aka je aka shaida ma Hisham cewa fa ga abinda yake faruwa a kurkuku,sanadiyyar kawo wannan da ya yi. Jin haka sai Hisham ya bada umurnin a fito dashi,a kuma mai da shi madina.Daga }arshe dai,shi wannan Hisham ]in shine ne sabab ]in wafatin sa [AS] ta hanyar sa masa guba.Amma cikin wa]annan khalifofi na umayyawa guda biyar da Imam Ba}ir [AS] yayi zamani dasu,wanda yafi samun sau}i da kuma samun damar karantarwa na ulum na Ahlulbayt [AS] a lokacinsa, shine Umar ]an AbdulAziz.Kuma shi Umar ]an AbdulAziz  ya yi wasu ababe ga Imam Ba}ir [AS],wa]anda su Banu Umayya ba suji da]i ba.Daga ciki akwai mai da FADAK na Sayyida Fatima [AS] ga Imam Ba}ir [AS],banda kuma ha]uwa da yake da Imam Ba}ir [AS] in yazo madina,ga kuma hana la’anta na Imam Ali[AS] da yayi,wato wadda ake yi lokacin a masallatai.Wanda daga }arshe shi kansa Umar ]an AbdulAziz Banu Umayya basu bar shi ba.Guba suka sa masa yayi sanadiyyar wafatin sa, bayan mulki na shekaru biyu da wata biyar.
3.       ILIMINSA:Imam Ba}ir [AS] ya kasance a wannan fage na ilimi.malaman da su kayi zamani dashi,dama wa]anda ba suyi zamani dashi ba,duk sun tabbatar da haka,cewa a zamaninsa baki ]aya ba wanda ya kai shi ilimi.Domin hatta sahabban Manzon Allah [S],wa]anda Allah yayi wa tsawon rai sun amfana da iliminsa.Ga misalan wasu daga ciki,Abdullahi ]an Umar,ga duk wanda ya bibiyi tarihin Abdullahi ]an Umar a fagen ilimi,a littafan madrasah ]in Ahlus-Sunnah zai fahimci abinda ake nufi a matsayinsa na fagen ilimi,amma duk da wannan ilimin nasa,wani lokaci za’a zo mishi da tambayoyi na mas’aloli na Addini,wa]anda ya sani ya bada amsa wa]anda bai sani ba  sai yace “kuje ku tambayi wancan saurayin,Yana nufin Imam Ba}ir [AS],amsar daya fa]a muku kuzo ku fa]a mani,” haka nan,Sahabin Manzon Allah [S] Jabir ]an Abdullah,wani lokaci in ya fa]i wasu hadisai da yaji daga Manzon Allah [S],Imam Ba}ir [AS] ya kan gyara masa wasu,yace ga yadda hadisin yake.Akwai misalai da dama irin haka,kamar fa]in wani malami da yayi zamani dashi,yace “ ban ta~a ganin wani wanda manyan malamai suke gabansa kamar yara ba,sai Abu Ja’afar.Shine ya bada misali da wani babban malami a lokacin mai suna Hakam ]an Utaiba.Yace duk da matsayin sa a ilimi,ya gan shi a gaban Imam Ba}ir [AS] kamar yaro gaban mai karantar da shi”.A ta}aice dai,a lokacin sa hadisai na Manzon Allah [S] da kuma Ahlulbayt [AS] sun ya]u fiye da kowane lokaci  a gabaninsa.Kuma ko yanzu mutum ya duba littafan hadisai na madrasah ]in Ahlulbayt [AS] zai ga haka;wato hadisan da aka samo daga Imam Ba}ir [AS] da kuma Imam Sadi} [AS] sun fi yawa,in an kwatanta da wa]anda aka samo daga sauran Imamai [AS].
4.      AKHLAK-[INSA:Shima a wannan fage kamar sauran fagagen rayuwarsa,a zamaninsa ba wanda ya kai  shi ballantana ya wuce shi,ga misalan wasu daga cikin Akla}-]insa.
A-Ha}urinsa:akwai wani Ahlul-kitab daya  fa]a masa Magana ]ai-]ai har guda uku,wa]anda basu da da]in ji ko karantawa ko rubutawa.Amma saboda amana  ilimiyya ga ]aya daga ciki,yace ma Imam Ba}ir [AS] “kai ba}ara ne.”Ya mayar masa da amsa cikin murmushi yace, “a’a ni Ba}ir ne”.Sai ya fa]i sauran munanan maganganun guda biyu,Imam Ba}ir [AS] ya mayar masa da amsa cikin murmushi,ganin haka sai wannan Ahlul kitab ]in abin ya bashi mamaki, domin ya ga ya fa]i maganganu wa]anda yake tunanin, zasu fusata Imam Ba}ir [AS],amma shi ya mayar masa da akasin abinda yake tunani.Daga }arshe dai ganin wannan Akhla}  na Imam Ba}ir [AS] sai nan take ya tuba,ya musulunta.Mu duba irin wannan jarabawa,ace  Ahlul-kitab,bama musulmi ba yayi irin wannan.Mutum zai ji mamaki ta wani ~angare kan haka,ta wani ~angare kuma ba zai ji mamaki ba,saboda kafa suka samu na yin haka daga masu tafi da iko;wato yadda suke zagin Imaman  Ahlulbaiti [AS] a lokacin a masallatai,musamman ma Imam Aliy [AS].Har wala yau daga cikin ha}urinsa akwai wani mutumin sham,daya kasance yakan je majalisin Imam Ba}ir [AS]. ya fa]i sunansa gatsai “ya Muhammad!”Ina zuwa wannan majalisi naka ne,ba wai don ina son ka ba,kuma ni bani da wani da nake }iyayya dasu  kamar ku Ahlulbayt [AS],domin na san }iyayya daku shine ]a’a ga  Allah da kuma khalifah [mutanen sham haka aka gina su a lokacin,wato }iyayya da kuma gaba da Ahlul-bayt].Saboda haka abinda yasa nake zuwa majlisin ka saboda fasahar maganarka da kuma balagar dake ciki.Bayan daya gama  sai Imam Ba}ir [AS] cikin murmushi ya mayar masa da jawabi mai ratsa zuciya.Nan take mutumin ya samu canjin tunani daga }iyayya ga Ahlulbayt [AS] zuwa wila’a garesu.Ya ma fasa  komawa sham ]in,ya za~i ya zauna wajen Imam Ba}ir [AS].Ya bar wasiyyar cewa in ya rasu,Imam Ba}ir [AS] yayi masa sallah.Akwai misalai da yawa irin wannan na ha}urin  Imam Ba}ir [AS] wanda wannan Akhla} nasa na ha}uri, ya zama makami babba na canza masu gaba da }iyayya dashi zuwa ga masoya.
A.      Kyautarsa.Imam Ba}ir [AS] ya kasance mai yawan kyauta.Akwai wani daya kawo kukan halin da yake ciki na bu}ata.Yace,da  yana dashi,mutane suna tare dashi,amma yanzu da bashi da shi  sun waste sun bar shi.Shine Imam Ba}ir [AS] yace masa tir da ‘yan uwantakar  da in kana dashi,ana tare da kai,in baka dashi a yanke maka.Sai Imam Ba}ir [AS] ya bashi dirhami ]ari bakwai yace, “kaje ka biya bu}atar ka da wannan,in sun }are ka fa]a mani”.Har wala yau daga cikin kyautarsa yazo daga Imam Sadi} [AS] yace “na shiga wajen babana wata rana,sai na same shi yana sadaka ga matalautan madina da dirhami dubu takwas.Haka nan ya kasance mai yawan ihsani ga ‘yan uwansa na jini.Yazo a tarihinsa cewa,in suka zo wajensa ya kan basu ku]a]e,tufafi,da kuma kayayyakin abinci.Har akwai lokacin da wata baiwarsa  tayi masa Magana akan haka,yace mata, “meye duniya in ba kyautata ma ‘yan uwa da abokai ba?” Akwai misalai da yawa na irin kyautarsa,amma za’a ta}aita akan wa]annan.
B.      Tawali’unsa.Imam Ba}ir [AS] ya kasance mai yawan tawali’u.Ga misalin wani daga ciki.Yazo a tarihinsa cewa da daddare a munajatinsa da Allah[T] yakan fa]i haka “Ya Allah ka umurce ni,amma ban umurtu ba,ka hana ni,amma ban hanu ba,gani bawanka gaba gare ka”.Mu duba,mu gani a matsayinsa na ma’asumi a I’iti}adin da muke dashi,amma yana fa]in haka,to ina gamu? Kuma wannan itace dama ]abi’a ta bayin Allah [T],wato suna kusantar Allah,amma kuma suna ganin }as}ancin kansu da kuma lalacewar su gaban Allah [T],saboda suna gaban wanda yake da kamala wadda bata da iyaka.Saboda haka yana da muhimmanci ko wannenmu ya zamo mai yawan }as}antar da kai ga Allah [T] da kuma bayinsa,musamman ma ga ‘yan uwansa muminai.
C.      Kukansa.Imam Ba}ir [AS] ya kasance mai yawan kuka saboda tsoron Allah [T].Akwai wani da yaje aikin hajji tare dashi,yaga yadda yake kuka har sautin kukan yana fita,sai shi wannan mutumin yayi wa Imam Ba}ir [AS] Magana,Sai Imam Ba}ir [AS] ya kira shi da sunansa Aflah Ya Aflah! Ina ]aukaka sautin kukana ne,domin Allah [T] ya gan ni ya dube ni da Rahma,domin in rabauta da ita gobe }iyama.”Har wala yau shi wannan dai da yayi aikin hajji da Imam Ba}ir [AS] yake cewa,akwai lokacin daya ga yana sallah,da yayi sujuda,bayan ]agowarsa daga sujada,sai yaga wajen duk ya ji}e da hawayensa.Shima wannan akwai misalai da yawa akan haka,amma za’a ta}aita akan wannan. 

No comments:

Post a Comment