Sunday 3 February 2013

Daruusa 12 daga rayuwar Imam Mahdi (AS)


Kasantuwar wannam wata da muke ciki, wato na Sha’aban a cikinsa ne aka haifi Hujjar Allah a doron }asa, kuma Shugababn wannan zamani, wato Imam Mahdi (AS), kamar yadda aka sani shi ne Imam na 12 a jerin }idaya na Imamai 12, wato shi ne Khalifan Manzon Allah (S) na }arshe.

An haifi Imam Mahdi (AS) a daren Juma’a, kuma daren 15 ga watan Sha’aban, a shekara ta 255 bayan hijira, a wani gari da ake ce wa Samarra, wanda a yau yana cikin }asar Ira}i. Saboda haka shekarun Imam Mahdi (AS) yanzu a duniya 1178. Imam Mahdi (AS). In mutum ya lissafa daga haihuwarsa zuwa yanzu, zai ga haka.
Ta yiwu wani ya yi mamaki, ko ya tambaya zai yiwu mutum ya yi tsawon rai haka? Amsa, zai yiwu. Domin tarihi ya tabbatar mana akwai daga cikin mutane wa]anda Allah (T) ya rayar da su shekaru masu yawa, wasun su Annabawa ne, wasu kuma ba Annabawa ba ne. In mutum ya duba cikin littafi mai suna A’IMMATUNA juzu’i na biyu akwai babi da ya yi kan wannan al’amari da ya shafi tsawon rai na Imam Mahdi (AS), ya yi bayani mai tsawo a kai. Daga }arshe kuma ya ba da misali na wasu da Allah (T) ya yi wa tsawon rai.
Ga misalan wasu da ya kawo; Annabi Nuhu (AS). Ya kawo wani Hadisi wanda aka samu daga Imam Sadi} (AS) ya ce, Annabi Nuhu ya rayu shekaru 2500, daga ciki ya yi shekaru 850 gabanin aiko masa sa}o, ya yi shekaru 950 wajen da’awa. (Wannan ma ya zo a nasssin Al}ur’ani). Sannan ya yi shekaru 700 bayan halakar da mutanensa”.
Wani misali kuma da ya kawo shi ne Annabi Adam (AS). Ya kawo Hadisi daga Manzon Allah (S) ya ce; “Baban mutane, Adam (AS), wanda ya rayu shekaru 930”.
Ya kawo kuma misalin Annabi Idris (AS), wanda ya rayu shekaru 965. Annabi Hudu (AS) ya rayu shekaru 962. Ga kuma misalin Khidir (AS), wanda Malaman Shi’a da kuma Sunna mafi yawansu, sun tabbatar da yana raye, mu duba ko tun zamanin Annabi Musa (AS) yake.
A ta}aice dai abin da ake so a fitar a nan shi ne, tsawon rai na Imam Mahdi (AS) ba wani ba}on abu ba ne a tarihin ]an’adam. Kuma ko dama ba hujjar wasu da suka yi tsawon  rayuwa kamar tasa, wato a ce gabaninsa ba a samu wani ]an’adam da ya yi tsawon rai haka ba, to hujjar cewa Allah (T) mai iko ne a kan komai ya wadatar.
Shi ya sa in mutum ya duba a wa]annan makarantu guda biyu, wato Shi'a da Sunna, zai ga a mafi yawan al’amuran da suka shafi Imam Mahdi (AS) sun yi ittifa}i a kai. Sa~anin da aka samu ka]an ne. Misali an haife shi, ko ba a haife shi ba. Ko shi ma wannan, in mutum ya yi bincike zai ga cewa mafi yawan Malaman Ahlus Sunna sun tafi a kan an haiife shi, kuma yana raye. In mutum ya bibiyi littafan Shehu Usman [an Fodiyo, wa]anda ya rubuta dangane da Imam Mahdi (AS) zai ga ya tabbatar da haka. Kuma a lokacinsa ya gina jama’a a kan haka. Wato a kan yana raye. Haka nan wani Malamin Ahlus Sunnah mai suna Shaikh Abu Abdullahi Muhammad Ash-Shaffi’iy ya fa]i a cikin littafinsa mai suna Al-bayan Fi Akhbaari Sahibuz-zaman. “Ha}i}a Al-Mahdi ]an Hasan Askari ne, kuma yana da rai, kuma yana nan wanzajje tun fakuwarsa har zuwa yanzu, kuma babu abin da zai hana wanzuwarsa, da dalilin wanzuwar Isah da Khidir da Ilyas (AS)”. Wannan ke nan a ta}aice dangane da kasantuwar Imam Mahdi (AS) a raye.
Sunansa MUHAMMAD, amma ya zo a kan cewa ana son sakaye sunansa a zamanin gaiba (fakuwarsa), wato wannan zamanin da muke ciki, har sai lokacin da ya bayyana. Sai dai a yi amfani da la}ubbansa wajen ambatonsa.
Sunan Mahaifinsa kamar yadda aka sani, Imam Hasan Asskari (AS). Sunan Mahaifiyarsa Narjis, kuma nasabarta tana tu}ewa ne da Sham’un, wato Wasiyyin Annabi Isah (AS). Kinayar Imam Mahdi (AS) ita ce Abul {asim, wato dai kamar yadda ya zo a wani Hadisi daga Manzon Allah (S) ya ce; “{arshen zamani  wani mutum zai fito daga zuriyata, sunansa kamar sunana ne, Kinayarsa kamar kinayata ce, zai cika }asa da adalci bayan ta cika da zalunci”.
Haka nan kuma Imam Mahdi (AS) yana da la}ubba masu yawa, amma wa]anda suka fi fice su ne Al-mahdi, Al-{a’im, Al-Muntazar, Al-hujja da kuma Sahibuz-zaman. Yana da shekara biyar a duniya Mahaifinsa ya rasu, wato ke nan yana da shekara biyar a duniya Imamanci ya koma gare shi. Bayan wafatin Mahaifinsa, ya shiga gaiba ta farko wadda ake ce wa Sugraah, wato }aramar gaiba. Domin gaiba ]in Imam Mahdi (AS) ta kasu }ashi biyu; akwai ta farko, akwai kuma ta biyu, wadda ake ce wa kubra, wato babbar gaiba.
Gaiba ]insa ta farko ta ]auki tsawon shekaru 69, a cikin wa]annan shekaru ya kasance yana da ala}a da Shi’arsa ta hanyar Jakadu guda hu]u. Ta hanyar wa]annan Jakadu guda hu]u umurninsa ko haninsa yake fitowa zuwa ga Shi’arsa. Haka nan su kuma Shi’arsa ta hanyar su ne matsalolinsu da kuma tambayoyinsu ke isa gare shi. Domin su Jakadun suna da dangantaka da shi kai tsaye, sai dai a nan yana da muhimmanci a fahimce cewa su wa]annan Jakadu guda hu]u ba a lokaci guda suka kasance ba. A’a sun kasance ne ]aya bayan ]aya. Na farko shi ne Usman Bn Sa’id. Na biyu shi ne Muhammad [an Usman. Ya rasu a shekara ta 304 bayan hijira. Na uku shi ne Husain [an Ruh, ya rasu a shekara ta 326 bayan hijira. Na hu]u shi ne Ali [an Muhammadd As-Samariy, ya rasu a shekara ta 329. Bayan rasuwar wannan Jakadan nasa na hu]u, shi ne ya shiga gaiba kubra, a lokacin yana da shekara 74 a duniya. Kuma tun daga wannan lokaci har ya zuwa yau ]inmu, yana cikin wannan gaiba kubra ne, kuma zai ci gaba da kasancewa a haka har ya zuwa lokacin da Allah (T) zai ba shi izni da ya bayyana. Allah (T) ka gaggauta bayyanarsa.
Sabodaa haka rayuwar Imam Mahdi (AS) ta kasu zuwa marhaloli guda hu]u. Marhala ta farko, rayuwarsa tare da Mahaifinsa, wanda shekaru biyar ne. Marhala ta biyu gaiba ]insa ta farko, wadda shekaru 69 ce. Marhala ta uku gaiba ]insa ta biyu, wadda ita ake ciki har yanzu. Marhala ta hu]u lokacin da ya bayyana domin tabbatar da addini a bayan }asa baki ]aya. Wadda zai kau da zalunci da azzalumai da kuma shimfi]a adalci da gaskiya a duniya baki ]aya.
Saboda haka a wannan zamani na gaiba ta biyu, Imam Mahdi (AS) yana da Niyaba (wakilci) wadda aka ce wa Niyaba  amma, wato ta Fu}ha (Mujtahidai), waccen kuma ta gaiba ta farko ta Jakadu guda hu]u da aka ambata ana ce mata Niyaba Khassa. Duk da wannan wani fage ne na daban, bahasinsa na muhallinsa.
Ta yiwu a nan mutum ya yi tambayar me ya sa Imam Mahdi (AS) ya kasance a gaiba? To a nan Malamai da dama, musamman Malaman Shi'a sun yi rubuce-rubuce dangane da wannan maudu’i, wanda a nan ba zai yiwu a iya kawo dogon bayani a kai ba. Amma ga mai bu}ata yana iya samun littattafan da ako rubuta a kan haka. Misali littafin GAIBA na Shaikh [usiy, ko kuma wasu littattafai na tarihin A’imma (AS). Misali, wani littafi da aka ambata a sama mai suna A’immatuna ya  kawo bayani mai tsawo a kan wannan maudu’i, kuma da a ce mutum zai bincika, ko ya karanci littattafan tarihi ya ga abubuwa da suka faru, gab da rasuwar Mahaifin Imam Mahdi (AS) da kuma abinda suka biyo bayan rasuwarsa, zai fahimci wasu daga cikin dalilan gaiba ]insa. Domin ya zo a kan cewa rashin lafiya ta }arshe da Imam Hasan Askariy (AS) ya yi, wadda a cikinta Allah (T) ya yi masa rasuwa, masu tafi da iko a lokacin sun yi ta bincike su gano inda ]ansa Imam Mahdi (AS) yake da nufin su kashe shi, amma ba su samu nasarar haka ba.
Saboda haka bayan rasuwar Imam Askari (AS) sai suka kamo matansa da kuyangunsa suka tsare da tsammanin ko akwai mai ciki a cikinsu! Sun yi haka ne, wato yun}urin kisa da kuma tsarewa, saboda Hadisai da suke da masaniya da su, wa]anda suka zo da cewa Imam na 12 shi ne wanda zai kau da zalunci da kuma azzalumai a bayan }asa, ya kuma shimfi]a adalci da kuma gaskiya a kanta, kuma sun tabbatar da Imam Hasan Askari (AS) shi ne Imami na 11, sun ga shi yanzu yana gab da zai rasu, shi ne suka yi wannan yun}urin na neman Imam Mahdi (AS) domin su kashe shi. Da ba su samu nasarar haka ba, shi ne suka tsare wa]annan iyalinsa da tunanin ko ba a haifi Mahdi ba, bayan rasuwar sa ne za a haife shi. Domin ya zo a kan cewa lokacin da aka haifi Imam Mahdi (AS), Imam Hasan Askari (AS) ya ~oye maganar haihuwarsa, sai Shi’arsa na kusa ya shaida wa. Saboda haka su masu tafi da iko suna cikin ]imuwa da kuma duhu kan haka. Wato ba su san cewa Allah (T) ya riga ya hukunta ikonsa ba na cewa an haifi Imam Mahdi (AS) har ya rayu tare da Mahaifinsa shekara biyar.
A ta}aice dai haihuwar Imam Mahdi (AS) ta so ta yi kama da haihuwar Annabi Musa (AS), wato na cewa, tun gabanin a haife shi, ana neman sa domin a kashe, amma Allah (T) ya yi ikonsa, aka haife shi ya tashi a gidan wanda yake neman sa domin ya kashe,Allahu Akbar !
 Saboda haka shi Imam Mahdi (AS) tun gabanin a haife, shi da kuma bayan da aka haife shi, masu tafi da iko na Khalifofin Abbasawa suna neman sa ne domin su kashe shi. Allah (T) bisa ikon sa ya kare shi daga mummunan wannan nufi nasu a lokacin,
Don hatta bayan rasuwar Imam Askari (AS) a cikin kuyangunsa, akwai wata wadda suka ga tana da alamar ciki, haka suka sa aka tsare ta, har tsawon shekara biyu, daga baya dai suka sake ta. Ba su san cewa Allah (T) ya riga ya yi ikon sa ba.
Domin shi Imam Hasan Askari (AS) ]a ]aya kawai yake da shi, shi ne kuma Imam Mahdi (AS). Bayan haka ta yiwu mutum ya yi tunani ko tambayar cewa, to menene fa’idar Imam wanda yake fake? Wato cikn gaiba. Akwai fa’idodi masu yawan gaske, amma ga guda uku daga ciki;
1. Mujarradin kasatunwarsa a doron }asa, aminci ne, da albarka da kuma rahma ga halitta kamar yadda ruwayoyi na Hadisai suka nuna.
2. Shi Imam Mahdi (AS) kamar rana ce wadda girgije ya ~oye ta. Ana amfana da ita ko da ba a ganin ta, kamar yadda Manzon Allah (S) ya gaya wa Sahabinsa Jabir [an Abdullahi Al-Ansari lokacin da ya tambaye shi dangane da gaiba ]in Imam Mahdi (AS). Ya ce; “Ya Manzon Allah (S)! Shin Shi’arsa za su amfana da shi a gaiba ]insa?” Sai Manzon Allah (S) ya ce masa; “Eh! Ina rantsuwa da wanda ya aiko ni da Annabta, lallai su za su haskaka da haskensa, za su amfana da wilayarsa gare shi, kamar amfanar mutane da rana, ko da ko girgije ya lullu~e ta.
3. Mas’uliyyar Imam Ma’asum (AS) a Madrasah ]in Ahlul Bait (AS) ya kasu kashi biyu. Akwai mas’uliyya zahiriyya, akwai kuma mas’uliyya ba]iniyya. Mas’uliyya zahiriyya ita ce tsare shi addini da kuma jaddada addini, wato aikata shi a aikace da kuma }iyada siyasiyya, wato jagoranci, wanda su a Madrasah ]in Ahlus Sunna wannan ne kawai suke la’akari da shi wajen shugabanci. mas’uliyyar ba]iniyya ta Imam Ma’asum (AS), ita ce kamar shahadatul a’amal. Wato ayyuka da ake kai masa na mutane, wato mabiyansa da ma wa]anda ba mabiyansa ba. Wasu ayyuka su faranta masa rai, wasu kuma su ba}anta masa rai.
Akwai kuma Nuzulul Barakat da kuma Su’udul A’amal, wato saukar da albarkoki ta hanyarsa da kuma kai ayyuka ta hanyarsa, da sauran su na mas’uliyya ba]iniyya. Kuma ko ba ma wa]annan mas’uliyya ]in ba, Imani da kuma i’it}adi da kasantuwarsa, wato cewa yana raye, ya na sa fata da kuma }warin gwiwa cewa insha Allah zalunci zai kau daga doron }asa a watan wata rana.
Sai kuma abun da ya shafi wasu ~angarori na rayuwarsa. Wato kamar ibadarsa, Akhlak ]insa, Zuhudunsa da dai sauransu. Ta yiwu wani ya yi mamaki ko tunanin cewa tun da Imam Mahdi (AS) mafi yawan rayuwarsa a cikin gaiba ne, ya aka yi aka san irin wa]annan ~angarori na rayuwarsa? Amsa a nan ita ce; idan mutum ya bibiyi tarihin Imamai ]aya bayan ]aya, wato tun daga Imam Ali (AS), har ya zuwa Imam Mahdi (AS), zai ga babu wani Imam daga cikin Imamai da bayanin sa ya zo sanka-sanka a cikin Hadisai da aka samo daga Manzon Allah (S) da kuma Ahlul Baiti (AS), kamar Imam Mahid (AS).
Bayaninsa ya zo sanka-sanka ta kuma kowace fuska, wato ta duk bayanai. Siffofinsa sun zo ‘khal}iyyan’ da kuma ‘khulu}iyyan’, wato na halitta da kuma ]abi’a. Saboda haka hatta wa]annan ~angarori na rayuwarsa, kamar Ibadarsa, Akhlak ]insa da Zuhudunsa, duk bayaninsu ya zo a Hadisai. Allah (T) shi ne mafi sani. Amma }ila hikimar haka ita ce; idan ya bayyana, al’amarinsa zai kasance tamkar hasken rana. Domin duk siffofinsa na halitta da ]abi’o’i ga su a Hadisai, kuma wannan zamani ko lokaci da muke ciki ga dukkan alamomi lokaci ne na gab da bayyanarsa.
Domin kamar yadda ya zo a Hadisai, gab da bayyanarsa, fitintinu da jarabawowi za su yawaita fiye da kowane lokaci. Domin gab da bayyanarsa, zalunci zai kai mataki na }arshe, kuma babi na }arshe, kuma idan ya bayyana, wata sabuwar jarabawa ce babba za ta fuskanci duniya baki ]aya, Musulmi da wanda ba Musulmi ba. Domin idan ya bayyana, duniya baki ]ayanta da ikon Allah sai ya du}ar da ita }ar}ashin Musulunci. Ba a na nufin kowa zai zama Musulmi ba, a’a, zai zamo dai kowace nahiya a duniya za ta kasance tana }ar}ashin iko na Musulunci. Sannan kuma zai dawo da fahimta da kuma koyarwa ta Musulunci tsantsa kamar yadda yake a lokacin Manzon Allah (S).
Saboda haka duk wani abu wanda yake akwai shi a cikin addinin Musulunci, amma aka fitar da shi, to zai dawo da shi. Haka nan kuma duk wani abu da aka sa a cikin addinin Musulunci wanda babu shi, to zai fitar da shi. Wato a ta}aice dai kamar yadda aka ce zai dawo da addini tsantsa kamar yadda yake a lokacin Manzon Allah (S). To nan ne mutum zai fahimci cewa, lallai jarabawa ce babba za ta kasance ga mutane a lokacin bayyanarsa. Kuma a lokacin babu wani }arfi da ya isa ya ja da shi, face ya samu galaba a kansa da ikon Allah.
Bayan ya tabbatar da addini a bayan }asa baki ]aya. To, lokacin duniya za ta numfasa, ta samu wani irin aminci da yalwa ta arzi}i, da lafiya, da dai sauran alherai da kuma albarkoki, wanda ba ta ta~a samu ba. A lokacin adalci zai shimfi]u ya mamaye duniya, kamar yadda zalunci ya mamaye ta gabanin haka. Saboda haka yana da gayar muhimmanci kowa ya yi wa kansa muhasaba, wato hisabi, ya tambayi kansa. Yaya ala}arsa take da Imam Mahdi (AS)? Wato, ya Imam Mahdi (AS) yake a wajensa? Ya shi kuma yake a wajen Imam Mahdi (AS)? Me yake yi ga Imam Mahdi (AS)? Da dai sauran tambayoyi ire-iren wa]annan da zai wa kansa dangane da ala}arsa da Imam Mahdi (AS).
Insha Allah shekara mai zuwa, in Allah (T) ya kai mu a munasabar wiladarsa, za a ]ora a kan abin da ya shafi ~angarorin rayuwarsa wa]anda aka ambata a sama.
Wani Tambihi ka]an dangane da wannan wata da muke ciki, wato watan Sha’aban shi ne; wannan wata na Sha’aban, wata ne da ake so mutum ya yi shiri da kuma yin shimfi]a ga babban ba}o mai zuwa, wato watan Ramadan, kamar yadda bisa ]abi’a da kuma al’ada, idan mutum zai yi babban ba}o, zai yi shirye-shirye domin zuwan sa. To haka nan ake so gabanin zuwan watan Ramadan. Ana so mutum ya yi shirye-shirye na musamman, wato shiri MA’ANAWI, ta hanyar tazkiyya ]in nafs ]inmu, wato tsarkake kawukanmu zahiri da kuma ba]ini da kuma lizimtar ayyuka na ibadodi daban-daban, kamar yawaita Salloli, karatun Al}ur’ani, Azkar da Addu’o’i da dai sauransu, ta yadda jikinmu zai saba sosai da tsayuwa da wa]annan ibadodi kafin shigar watan, wanda wannan zai taimaka mana in mun shiga watan Ramadan ]in, ba za mu samu wahala ba wajen tsawuwa da ibadodin da ke ciki. Sa~anin ko a ce mun shiga watan ba wannan mu}addima ]in na tazkiyya ]in nafs ]inmu, da kuma tsayuwa da ayyuka na ibadodi, wanda wannan zai shamakance mu daga samun zau}i da halawa na ibadodi a cikin watan. 



No comments:

Post a Comment