Inna-lillah-wa-inna- ilaihi- rajiun, na tafiya da kuma rabuwa da
wannan babban ba}o mai girma da kuma daraja da ya ba}uncemu,
wato watan ramadan. Domin idan mutum ya bincika zai ga cewa a duk watanni 12 da
ake da su a musulinci, babu wani wata da aka samu ruwayoyi daga Manzon Allah
(S)da kuma A’imma na ahlul-baiti (AS) na bankwana da shi da kuma umarni da yin haka face watan ramadan, wanda wannan ka
]ai ya isa ya nuna falala da darajan wannan watan.
Misali shine ruwaya
na addu’an bankwana da watan da aka samo daga Manzon Allah (S). An samo daga
Jabir ]an
Abdullah al-ansariy (RA), yace: “Na shiga wajen Manzon Allah (S) a juma’ar }arshe ta watan
ramadan, lokacin da Manzon Allah (S) ya ganni sai ya ce min,ya Jabir` wannan
itace juma’an }arshe ta watan ramada. kayi bankwana da shi, Ka ce;
YA UBANGIJI! KADA KA SA YA ZAMA AZUMIN {ARSHE A RAWUWATA.
IN KASA HAKA, TO, KA SANI CIKIN RAHAMAR KA, KADA KA SAN YANI CIKIN WA[ANDA
AKA HARAMTA WA RAHAMA”. Manzon Allah (S) ya ce duk wanda ya fa]i
haka, zai rabauta da ]aya daga cikin
kyawawa guda biyu: ko dai Allah (T) ya raya shi zuwa watan Ramadan na gaba
ko kuma Allah ya gafarta masa ya yi masa
rahama.
Haka nan akwai
ruwayoyi daban-daban guda biyu na bankwana da aka samo daga Imam Zainul Abidin
(AS) wanda idan mutum ya karanta su, musamman ma a ce lokacin da yake karantawa
zuciyarshi na halarce, tabbas zai samu tasirin haka a ruhinsa. Domin zai ga
yadda Imam Zainul Abidin yake magana da sallama da bankwana da watan ramadan da
kuma jin zafin rabuwa da shi, kamar ka ce mutum ne yake gabansa yake bankwana da shi da kuma nuna damuwa na rabuwa
da shi. Ga misali wasu daga cikin kalmomi na bankwana da ya yi ga watan ramadan
da suke a cikin addu’o’i da aka ruwaito daga wajen sa (AS). Yana
cewa;”Innalillahi wa inna ilaihi rajiun saboda rabuwa da watan azumi, watan tsayuwa kuma wata na al}ur’ani. Ya kai wannan wata namu! Muna bankwana da kai
ba domin mun }osa da azumi a cikin ka ba, ba domin
muna son rabuwa da kai ba. Da a ce za a iya cewa wata, Allah ya sakamaka da
alheri da an ce, Allah ya saka maka da alheri ya watan ramadan”. Awani wajen
yana cewa muna bankwana da kai bankwana na ba}in
ciki da kuma jin zafin rabuwa da kai”.
Akwai kuma wani sashe
da ya jero sallama ga wannan wata mai albarka. Misali yana cewa;”sallama gareka
ya kai wannan watan idin walliyyan Allah.Sallama gareka ya mafificin wanda ake
abota dashi daga lokuta.Sallama gareka na ma}wabci,wanda
zukata suka lausasa a cikinsa,kuma
zunubai suka }aranta a cikinsa.Sallama gareka na mataimaki daga mataimaka akan she]an.Sallama
gareka wanda kazo mana da albarkoki,ka kuma wanke mu daga dattin
zunubai.Sallama gareka wanda ake bege da nema gabanin zuwansa,ake kuma ba}in
ciki gabanin rabuwa dashi.Sallama gareka
da kuma lailatul }adari,wadda take
mafi alheri daga wata dubu.Sallama gareka a bisa falalarka,wadda aka haramta
mana da kuma albarkokinka wadanda suka shu]e,wanda yanzu mun rasa su”. A
ta}aice
dai idan mutum ya biya wannan addu’a, ta
Imam Zainul Abidin [AS] ta bankwana da watan ramadan zai ga yayi wa wannan wata
mai albarka sallama biye da juna, ]ai ]ai
har guda 20.Haka nan Imam Sadi} [AS] an samo irin
wannan addu’a ta bankwana da watan ramadan daga wajensa, kuma idan mutum
ya duba dukkan wa]annan addu’oi da aka samo daga Aimma [AS] zai ga Ahlulbayt [AS]
in an kwatanta da madrasah ]in
Ahlus Sunna.Mu ]auki misali addu’oin da ake yi na watan Ramadan ,wanda shaikh Abbas Al-}ummy
ya kawo a cikin littafin sa na mafatihul
jinan,ya duba zai ga irinsu a madrasah ]in Ahlus Sunna ? wanda in mutum yayi bincike zai ga babban littafi
da ake dashi a madrsah ]in Ahlus Sunna,da ya tattaro addu’oi da kuma
Azkar da aka samo daga Manzon Allah [S] shine littafin Azkar na Nawawi,idan mutum na da shi
ya ]auko
ya duba babin da yazo na Azkar da kuma addu’oi na watan Azumi da kuma na daren
lailatul }adr, zai ga ]aya
bisa uku bai kai ba akan yadda suka zo a mafatihul jinan,kuma wannan bai ta}aita ga Azumi ba,a’a haka abin yake ga dukkan janibobi na ibadat,
kamar sallah da makamantansu,wanda ko wanne
daga cikin salloli wajibai guda
biyar,mutum zai ga bayanansu,suna da ta’a}ibat na amma,da
kuma ta’a}ibat
na kassa.Da sujudu shukur,wanda shima
wannan mutum ya duba cikin wannan
littafin Azkar na Nawawi, ya ga ko zai ga irin haka.Wanda wannan kawai ya isa ya sa mutum ya yawaita godiya ga Allah [T] a bisa ni’imar tamassuki
da wilaya ]in Ahlulbayt [AS],wanda dama sune Manzon Allah [S] ya bar wa wannan
al’ummar wasiyyar yin tamassuki dasu.A ta}aice
dai bayin Allah [T] kamar yadda suke shau}i da farin
cikin zuwan watan Ramadan, saboda falaloli da darajoji da zau}iyyat
da halawat da kuma ma’anawiyyat na ibadodi da ake samu a cikin watan,wanda babu irin haka a sauran watanni,don me haka bazai zama ba alhali Allah [T]ne ya kirayi bayinsa zuwa ga liyafa, kamar yadda yazo a
hadisi.Kamar yadda aka sani a liyafa,akan gabatar da abinci da abin sha daban
daban,to ita wannan liyafa abincinta da abubuwan shanta na ruhi, sune salloli,da karatun
Alkur’ani,Azkar,Addu’oi da sauran ayyuka
na ]a’a
da bayi suka tsayu da su a cikin watan,wanda halartar
da zuciya lokacin yin wa]annan ayyuka na
ibadat da aka ambata, shike haifar da samun wannan ma’anawiyyat da zau}i
da halawa da aka ambata a sama.Saboda haka ya na da gayar muhimmanci duk wanda
Allah Ta’ala ya raya shi ya nuna masa watan Ramadan tun daga farkonsa har }arshensa,to,ya gode
wa Allah [T] ta hanyar salatu shukur,ko kuma sujudu shukur bayan watan Ramadan ]in,domin
in mutum yayi tunani,zai ga da yawa akwai wa]anda
basu samu wannan ni’imar ba.Wato Allah[T] bai raya su ya nuna masu watan ba,ko
kuma Allah ya nuna masu watan amma basu ga }arshensa
ba.
Baya ga wa]annan
Addu’oi da aka ruwaito daga ma’asumai [AS] na bankwana da watan Ramadan,malaman
Irfan sun }ara da wasu ladubba da ake son mutum
ya aikata }arshen watan
Ramadan ]in,ko kuma bayansa.Ga wasu daga ciki:Idan mutum ya duba littafin
mai suna Mura}abat na
Ayyatullah Mirza Jawad Attabrizy;ya na ]aya
daga cikin manya manyan malaman Irfan,kuma ya fitar da malamai da yawa a wannan
fage, ya ma zo akan cewa Imam khumain [KS] ya yi karatun Irfan a wajensa.Idan
mutum ya duba a wannan littafin na sa da aka ambata zai ga ya kawo wasu ladubba
a fasali na tara a }arshensa.Ga guda
uku daga ciki. 1.Muhasaba:Wato
mutum ya zauna yayi wa kansa hisabi,ta hanyar yin tafakkuri [tunani] ya binciki
kansa,shin ya samu ci gaba a addinance in an kwatanta da gabanin kamawar watan Azumi da kuma yanzu da ya
kare.Misali alakarsa da Allah [T],alakarsa da manzon Allah [S] da kuma
Ahlulbayt [AS] da damfaruwa da gidan lahira,iltizaminsa da addini,sun cigaba
ne,ko suna nan yadda suke gabanin watan Azumi,ko kuma wa’iyazubillah ya samu ci
baya? Haka nan ta janibin akla}
]insa
ya da ]a
samun tsal-kakuwa daga akla} marasa kyau da kuma
siffantuwa da kyawawan akla}? Da dai sauran
abubuwa na muhasaba da shi mai littafin
ya kawo.Shine daga }arshe yake cewa duk wanda watan Ramadan ya kama ya }are
bai samu tasirantuwa da hasken watan Ramadan ba,to ya sani duhun zunubansa sun wuce
hasken wannan wata mai haske mai
haskakawa.yace in ba haka ba yaya za’ayi ace ba zai tasirantu da hasken watan
Ramadan ba da kuma na dararen lailatul }adar? Yace irin
wannan mai zaluntar kansa yaji tsoron fa]awa cikin addu’ar Manzon Allah [S] da yake cewa; “duk wanda
watan Ramadan ya wuce ba’a gafarta masa ba,ka da Allah ya gafarta masa”.yace
wannan kuwa itace mafi tsananin musiba. Dama musiba kamar yadda aka sani takan samu bawa,
imma a fagen duniya,ko kuma a fagen
addini.Musiba a fagen duniya itace;misali rashin lafiya,}uncin
rayuwa,rashin aminci,cutarwa sakamakon
kama tafarkin Allah [T],ko kuma
sakamakon ri}o
da Ahlul bayt [AS],duk wa]annan
alheri ne ga bawa.Domin ta hanyar haka zai samu lada da kuma daraja a
wajen Allah[T].Sa~anin musiba a
addini,wanda shine mutum ya dinga aikata sa~o,ko
kuma zai iya aikata wani aikin ]a’a, ya zamanto bai aikatawa,ko kuma yayi abinda
zai janyo masa fushin Allah [T],ko kuma ya janyo Manzon Allah [S] da Ahlul bayt
[AS] ba su son shi.Shi ya sa yazo a wata
addu’a daga Manzon Allah [S] cewa, ‘Ya Allah kada ka sanya musibarmu a
addininmu’. A
ta}aice
dai musiba ce babba ga mutum watan Ramadan ya }are,
bai samu sauyi da kuma tasirin watan ba.A cikin wani littafi na Imam khumain
[KS] mai suna jihadul- Akbar yana cewa,
‘Idan watan Ramadan ya wuce mutum bai samu wani canji a ‘suluk’[]abi’unsa da ayyukansa] ]insa
ba,to ya sani bai tsayu da Azumi yadda ake so ya tsayu dashi.Yace a wannan wata
an kiraye ku liyafa ne,idan saninku ga
Allah bai }aru ba,to ku sani baku amsa wannan
kira [na liyafar] yadda ya kamata ba.Wannan kenan a ta}aice
kan muhasaba.Kuma ita muhasaba in son samu ne,mutum ya kasance ko wace rana ya na
yinta,ko da safe ko da yamma,ko in zai kwanta da daddare, ko kuma in ya tashi
tahajjud to ya bainciki kansa kyawawa da munanan ayyukan da ya aikata a
ranar,daga }arshe kyawawa ya gode wa Allah [T] da yayi masa muwafa}ar
aikatawa,munana ya nemi Allah [T] ya gafarta masa,an samo daga Imam
kazim [AS] yana cewa, ‘Ba ya daga cikin mu wanda bai yi wa kansa hisabi ko wace
rana’.
2.Afuwa:A nan shima
littafin mu}araba,ya kawo wata }issa
mai tsawo wadda Imam Zainul Abidin [AS]
ya kasance yana aikatawa tsakaninsa da bayinsa idan watan Ramadan ya }are.Kulasar
}issa
]in
shine Imam Zainul Abidin [AS] ya kasance idan watan Ramadan ya kama,bayinsa
baki ]aya
duk wanda yayi laifi bai ce masa komi,bai yi masa
komai sai dai ya rubuta wane yayi laifi kaza,rana kaza,sai daren }arshe
na watan Ramadan ya tara wa]annan bayinsa
baki ]aya
ya ]auko
wannan littafi yace; “Wane kai ka aikata abu kaza rana kaza banyi maka komai ba,ka tuna? Yace, “lallai na
tuna ya ]an Manzon Allah [S]”.Haka zai dinga kiransu ]aya bayan ]aya
wa]anda
su kayi laifi ]in,sannan sai ya mi}e tsaye a
tsakaninsu, yace masu ku ]aga sautinku kuce, “Ya Ali Bn Husain! Lallai ubangijinka ya
kiyaye duk abinda ka aikata,kamar yadda ka kiyaye duk abinda muka aikata,saboda haka kai mana afuwa kamar
yadda kake fatan ubangiji yayi maka afuwa”.Sannan sai Imam Zainul Abidin [AS]
yace, “Ya ubangijinmu,ka umurce mu mu yi afuwa ga wanda ya zalunce mu,ha}i}a
mun zalunci kawukanmu, mun yi afuwa ga wanda ya zalunce mu kamar yadda kayi
umurni, kai mana afuwa”.Sannan sai ya juya ga wa]annan
bayin na sa,yace musu na yi maku afuwa,ni ma kun yi mani afuwa? Sai suce, “mun yi
maka afuwa ya shugabanmu!” sai ya sake ce masu kuce; “Ya ubangiji kayi afuwa ga
Ali Bn Husain kamar yadda yayi mana afuwa”.Sai Imam Zainul Abidin yace,
“Allahumma Amin Ya Rabbil Alamin”.Wannan
}issar
duk da kulasar ta aka
kawo, akwai darussa masu yawa aciki amma ba za’a iya fitar dasu ba saboda gudun
tsawaitawa,mu duba Imam Ma’asumi a ii-ti}adinmu,kuma
khalifan Manzon Allah [S] ya na aikata irin haka, domin neman afuwa a wajen
Allah [T],to,ina ga mu.Shine mai wannan littafi daga }arshe
yake cewa,idan mutum zai yi koyi da Imaminsa a wannan aiki ya na da kyau, ya ba
da misalin mutum zai iya yin haka cikin iyalinsa da ‘ya’yansa, a ta}aice
dai abinda ake so,kamar yadda ko wanne yake fata yake kuma kyautata zato ga
Allah [T] cewa,Allah [T] ya gafarta masa, ya yafe masa }arshen
watan Ramadan, shima ya yafe wa wa]anda
suka zalunce shi,ko suka munana masa musamman ‘yan uwansa mabiya Ahlul bayt [AS] domin kamar yadda wani
malami yake cewa zai ji kunyar Manzon Allah [S] gobe }iyama, a ce gashi ya tsaya da wani masoyin gidan
Manzon Allah [S] domin wani ha}}insa.Saboda haka
wannan malamin ya kasance ko wace rana yakan ce; “Ya Allah! Duk wani mabiyan
Ahlul bayt [AS] da aka rubuta masa laifi saboda ni yau na yafe masa”.Saboda
kamar yadda mutum yake fata ya fita watan Ramadan yana yafaffe,to shima ya yafe
wa mutane.Wannan kenan a ta}aice.
3.Tuba:kamar yadda mai
littafin mura}abat ]in ya
kawo,shine mutum ya tuba da kuma neman gafara wajen Allah [T] dangane da ta}aituwarsa
wajen tsayuwa da ayyukan ibadodi a watan da kuma rashin kyautatawarsa ga ayyukan ibadodi da ya aikata,wato wajen
tsayuwa da ruhin ibadodi yadda ya kamata.Da ma Malaman Irfan sun kasa tuba kashi uku. 1.Tuba
ta awwam, ita ce tuba daga zunubi. 2.Tuba
ta kusus,[za~a~~un bayin Allah],ita ce tuba daga gafala.wato daga
tunanin Allah[T] ko kuma tunanin gidan lahira.3-Tuba ta kususul-kusus[za~a~~un-
za~a~~un bayin Allah[T] ita ce tuba daga ta}aitawa
da kuma rashin kyautatawa ga ayyukan
bauta,watau duk da yawaituwar ayyukan su na bauta da kuma kyutatawa a cikinsu
watau wajen ruhinsu.Suna ganin sun ta}aita kuma basu
kyautata ba a ciki,shi yasa wasu daga
cikin malaman irfan suka tafi akan cewa
kalmomi na tuba,gafara, neman afuwa da suka zo daga Addu,oin ma’asumai [AS] wannan nau’in tuba na ukku ne.Domin su Ma’asumai basa aikata
zunubi,haka nan basu kasancewa cikin gafala.saboda haka neman tubar su,a wajen
Allah[T] na yadda suke shu’urin ta}aitawar su ga bautar AllahT].
kamar yadda yazo a hadisi,akwai mala’ikan da tun da aka halicce shi yake sujuda,wani
yana ruku’u,wani yana tsaye da dai sauransu,amma ranar gobe }iyama
zasu ce, ya Allah ba mu bauta maka ba ha}i}anin
bauta”.Bayan haka ana son mutum ya samu isti}ama da sabati
ga wa]annan
ayyuka na ibadodi dai dai gwargwadon iyawar sa, ya tsayu akai har ya zuwa wani watan
Ramadan insha Allah.Daga }arshe babu abin
cewa face mu na godiya ga Allah [T] daya nuna mana farkon wannan wata,kuma ya
nuna mana }arshen sa.Ayyuka na ibadodi da Allah
[T] ya bamu ikon aikatawa,Allah[T]ya kar~a mana,Addu’oin da muka
ro}a,Allah[T] ya bamu fiye da abinda muka ro}a.Abubuwan
da muka nemi tsari na sharrori,Allah ya tsare mu fiye da abinda muka nemi tsari
a kai,Amin.
No comments:
Post a Comment