Saturday 9 February 2013

RANAR GHADIR A MAHANGAR AHLULBAIT [AS] DA AHLUS SUNNA.


Al-hamdu-lillah,kasantuwar wannan wata da muke ciki,wato na zul hijja,a cikin sa ne,kamar yadda aka sani,18 gare shi,shekara ta goma bayan hijira,wannan munasaba ta ghadir ta kasance.Kuma tun daga wancan lokaci har ya zuwa yau dinmu wato yau shekara sama da dubu da dari hudu,mabiya Ahlulbaiti [AS] a duk shekara a kuma sassan duniya dabam dabam suke raya wannan rana ta ghadir ta fuskoki daban daban.
Misali raya ranar tayin wasu ibadodi,kamar azumtar ranar,karanta wasu addu’oi da ake son karantawa a ranar,dadai sauran ayyuka na ibadodi da sukazo a hadisai,da ake son yin su a ranar,har wala yau mabiya Ahlulbait [AS] suna rayar da wannan rana,i tayin tarurruka  domin tunasar da juna dangane da wannan rana ta ghadir dadai sauran ababe dake da alaka da ranar,Wanda irin wadannan ayyuka na raya wannan rana ta ghadir,ba zaka jishi ko ka ganshi ba a tsakan kanin ‘yan uwanmu musulmi Ahlus Sunnah ba.Duk da cewa shi wannan al’amari na ghadir,ba abu bane daya shafi mabiya Ahlulbaiti ba kawai.A’a abu ne da ya shafi kowa da kowa a wannan al’umma ta manzon Allah [S],Domin khutbar da manzon Allah [S] yayi a ranar ghadir,wadda ta kunshi wadanda zasu kasance khalifofi a bayansa.abune wanda ya shafi kowane musulmi.                                                                                                                                             Baya ga haka kuma shi wannan al’amari na ranar ghadir mutum zai iya tabbatar dashi sanka sanka dinsa, a littafan Ahlus Sunnah, kai hatta wasu ibadodi da akeyi a ranar,sunzo a littafan Ahlus Sunnah misali anan shine Azumin ranar ghadir,akwai hadisi da yazo a cikin littafan Ahlus Sunnah akan shi,ga hadisin.An samo daga Abu Huraira yace, Manzon Allah [S] yace “Duk wanda ya azumci ranar sha takwas ga watan zulhijja,za’a rubuta masa azumin wata sittin itace ranar ghadir khum”........ wato har ya zuwa karshen hadisin.Mu duba muga wannan hadisi,gashi dai daga masadir ne na Ahlus Sunnah, amma da wuya kaji ambaton hadisin tsakan kanin malaman Ahlus Sunnah, kuma mutum ya kwatanta wannan hadisi da wanda suke yawan kawowa na Azumin Ashura,wanda wannnan ya isa ya nuna ma mutum cewa lalle wani abu ya auku a tarihin wannan al’umma, wato an gina mutane akan abunda akeso a ginasu.An kuma kautar dasu akan abunda akeso a kautar dasu.Wadanda suka yi riko da wannan al’amari na ghadir,aka dauki matakai akansu dabam dabam na cutarwa da galla zawa,mutum ya tambayi tarihi zai bashi amsa.Saboda haka wannan kadai ya isa ya nuna banbanci n mahanga tsakanin shi’a da sunna,dangane da al’amarin ranar ghadir.Wato a aikace zaka ga wadannan sun san da zamansa, kuma suna raya shi.Akasin daya bangaren ba zaka ji ambaton haka ba,ballan tana su raya shi, alhali mutum na mutuwa bayan an sa shi a kabari,daga cikin tambayoyin da za’a yi masa akwai abinda yake da alaka da wannan al’amari na ghadir,wato bayan an tambayi mutum waye Ubangijinka? Waye Annabinka?  Sa’annan sai a tambayi mutum waye Imaminka? Kuma wani abin lura anan shine,wadannan tambayoyi suna nuna lalle al’amarin Imamanci ko Khalifanci yana da alaka da akida ne,ba kamar yadda malaman Ahlus Sunna suka tafi akai cewa baida alaka da akida.Wato baya cikin Usuluddin yana cikin Furu’uddin ne.Kuma ko baya ga wannan mu duba irin su hadisai da suka zo,kan alamarin imamanci,misali hadisin da ya zo cewa “Wanda ya mutu bai san Imamin zamanin sa ba,to ya mutu mutuwar jahiliyya”Saboda haka,al-amarin imamanci ko khalifanci babban  abune,a wannan addini,shiyasa,a mad-rasa din Ahlul-bait, yana cikin usulid-din ne.kuma shi imamanci ko khalifanci,shine abu na karshe da Manzon Allah[S]yayi,a sakon da ya isar tsawon shekaru 23.Domin daga shi babu wani abun da ya sauka,mai matsayin wajibi,shiyasa bayan da Manzon Allah ya Nasabta Imam Ali[as]A ranar ghadir,sai ayar Al-yauma akmal-tu lakum-dinakum,ta sauka.Saboda haka isar da sakon imamanci ko khalifanci,tamkar khatma na sakon da Manzon Allah[S] yazo da shi,Kuma ayyana Imam Ali[as]A matsayin khalifa,a bayan Manzon Allah[S]ya kasance a matsayin rasmiyyan  ne wato officialy,domin gabanin haka,a wajaje da dama, a kuma lokuta dabam-dabam,Manzon Allah[s]yayi isha-rori da kuma hannun ka mai sanda,na khalifa a bayan sa,shiyasa Manzon Allah na cewa zai bayyana khalifan sa,sai wasu fuskoki suka bata rai,saboda sun san ko waye za a bayyana.Kuma baya ga haka,A sahabban Manzon Allah baki daya,babu wani sahabi wanda dajojin sa da fifikon sa,a ka ruwaito su daga Manzon Allah kamar Imam Ali[S]wannan magana,Ahmad ibn hanbal ya fade ta.Misali ga wasu hadisai na Ahlus sunna kan haka.Manzon Allah[s]yace “Bayana fitina zata kasance,idan haka ya faru,to ku lizimci Ali dan Abi Dalib,domin shi mai rarrabewa ne tsakanin gaskiya da karya”.A wani hadisin kuma,Manzon Allah[s] yace ma Ammar dan Yasir, “Ya Ammar idan kaga Ali yabi wata hanya,mutane kuma suka bi wata hanyar da Ali bai bi ba,to kabi hanyar da Ali yabi,kabar hanyar da saura  mutane suka bi,domin shi ba zai fitar da kai daga shiriya ba.”Har wala yau a wani hadisi kuma,Manzon Allah [s]yace “Zai kasan ce tsakanin mutane,za a samu sabani da rarraba,zai kasance wannan[wato imam Ali] da sahabban sa,su ke kan gaskiya.”da dai hadisai masu yawa,makamantan wadannan,da suka  zo a litafan Ahlus sunna,da suke nuni ga matsayi na Imam Ali[as]Saboda haka koda ma ace,kamar yadda Ahlus-sunna,suka tafi a kai,na cewa,wai  Manzon Allah[s]bai khalifan tar da kowa ba,ya bar al-umma ne ta zaba.To ashe ire-iren wannan matsayi na Imam Ali[AS]wadanda Manzon Allah,ya fadi game da shi,basu isa su can-cantar dashi ba,khalifan Manzon Allah?To ballantana kuma shine Manzon Allah,ya nasabta.Saboda haka Imam Ali[AS] shi ne ka dai ya cika  sharuddan da shia da suna suka tafi akai,na zama khalifa,in ka tafi akan nassi,ba zabin jama’a ba,to yana da nassi akai,in katafi akan zabin jama’a ne,to shi jama’a ne suka zabe shi.Sboda haka anan,wannan rubutu zai gudana ne Insha Allah akan wadannan ababe:
1.Muhimmancin ranar ghadir.
2.Abubuwan da suka auku ranar ghadir.
3.Tawili da kuma kwaskwarima da akayi ma al’amarin ghadir a littafan Ahlus Sunna.
4.Ayyukan da akeyi a ranar ghadir.
5.Kafa hujja da A’imma na Ahlulbaiti [AS] da kuma wasu daga cikin sahabbai da tabi’ai sukayi da hadisin ghadir akan wasu mutane.
6.Illoli da suka auku kuma suke aukuwa a wannan al’umma ta manzon Allah [S] saboda rashin aiwatar da al’amarin ghadir.
7.Wasu darussa da zamu koya daga al’amarin ghadir.                                                                                                                      Yanzu bayani a takaice dangane da wadannan ababe guda bakwai:
                1.MUHIMMANCIN RANAR GHADIR.                                                                                                                                        Ranar ghadir rana ce muhimmiya, a tarihin wannan  al-umma,da kuma  tarihin al ummun da suka gabaci wannan al-umma.Domin abubuwa da yawa na tarihin na tarihin Annabawa sun aukune,a  irin wannan rana ta ghadir.Alal misali yazo akan cewa  Annabi Musa[as] a irin wannan rana ce ya bayyana wasiyyinsa,wato khalifansa mai suna Yusha’u dan Nun.Haka nan ma Annabi Sulaiman a irin  wannan rana ya bayyana wassiyyinsa mai Sham’un.Haka nan yazo a kan cewa’yan-uwantaka da Manzon Allah[s]ya hada tsakanin Muhajirin da Ansar,a irin wannan rana ce ta kasance.wato 18 ga watan zul-hijja.Haka nan samun nasara dawasu daga cikin Annabawa  sukayi kan makiyan su, da yawa haka ya auku ne, a irin wannan rana.A takaice dai abubuwa da yawa sun auku,a tarihin dan-adam ,a wannan rana.Amma abun mamaki da yawa abubuwan da suka auku,a irin wannan rana a tarihi sai aka jir-kita-su,a ka nuna wai a ranar Ashura suka faru.Hatta al-amarin yal-wata ma iyali da yin ado da dai sauran su,da akazo dasu a ranar ashura.Asalinsu a ranar ghadir suka zo,amma aka canza.Ire-iren wannan abubuwa na canza tarihi da yawan su sun aukune,a lokacin daular bani-umayya.Saboda haka mutum zai iya cewa ba a bisa hatsari bane,Manzon Allah[s]ya bayyana ma wannan al-umma tasa wadanda zasu kasance khalifofi a bayansa.,wato a wannan rana ta 18 ga zul-hijja,in mutum ya dubi abubuwan da suka auku a tarihi a ranar,wato na Annabawan da suka gabata.Haka nan kuma daga cikin muhimmancin ranar ghadir.An tambayi Imam Sadik[as] “Shin Musulmi suna da wani idi banda ranar jumma’a da babbar sallah da kuma karamar sallah?sai Imam Sadik yace:Na am wanda ma ya fisu daraja,sai wanda ya ruwaito hadisin ya tambaya:wane idi ne wannan?sai  Imam Sadik[as]yace masa.Ranar da manzon Allah[s]ya Ayyana Imam Ali[as]a matsayin khalifa a bayansa,i tace ranar 18 ga zil-hijja.”Saboda haka, a ido-din da ake dasu a Musulunci ,to idin ghadir shine mafi girmansu da kuma daraja.Haka nan wannan rana ta ghadir sanan-niya ce a sama,wato tsakan-kanin Mala’iku,a sama ana cema ranar “YAUMUL AHDUL –MA’AHUD.”A takaice dai  ranar ghadi rana ce mai daraja da kuma falala mai tarin yawa.ya mazo daga Imam Ridha[as]yace, “Da ace mutane sun san hakika nin falalar da ke cikin ranar ghadir da Mala’iku sunyi musafaha dasu  a kowace rana sau goma.”Saboda muhimmancin al-amarin ghadir zamuga, Malamai na mad-rasa din Ahlul-bait[as]da yawa sun rubuta littafai akai.Ga sunayen wasu littafai daga ciki.1-Asrarul ghadir na Muhammad Bakir al-ansariy.2-Idul ghadir fil Islam na Allama Amini.3-Ghadir fil kitabi wa sunna wal-adab shima na Allama Amini.Da dai sauran littafai masu yawa akan haka.                            2-Abubuwa da suka auku ranar ghadir:-Sanin abubuwan da suka auku a ranar ghadir dama  abubuwanda suka auku gabanin ranar da kuma abun da ya biyo bayan ranar yana da gayar muhimmanci.Domin sanin  wadannan bangarori ukku na ghadir,wato abinda ya faru gabanin ghadir da ranar ghadir da kuma bayan ghadir,mutum zai fahimci lallai babban jarabawa da manzon Allah[s] ya fuskanta,a tarihin rayuwar sa,itace wannan al-mari na ghadir.Domin in mutum  ya dubi tsawon shekaru 23 da aka aiko ma Manzon Allah[S]da sako na wahayi.To babu sakon da yazo wanda Manzon Allah[S]ya nemi ayi masa afuwa wajen isar da shi.Sai wannan al-amari na ghadir.Domin yazo akan cewa lokacin da Manzo Allah[s]ya bijoro da al-amarin,na cewa zai bayyanar da magajinsa,wato khalifansa,gobe a ranar Arfa,sai  fuskokin wasu da yawa suka canza.Haka al-amarin ya kasance,har ya zuwa saukar aya mai cewa “Ya kai wannan Manzo,ka isar da abinda aka saukar zuwa gareka daga ubangijinka.Idan baka  aikata[haka]ba,to baka isar da[sauran]sakon ba.Kuma Allah zai kare ka daga mutane.Lalle Allah ba ya shiryatar da jama’a kafirai.[suratul-ma’ida aya ta 57]Bayan saukar wannan aya,nan take,sai  Manzon Allah[s] ya aika da a tsayar da mahajjata da suka wuce,da yake ita ayar ta sauka ne bayan aikin hajjin bankwana da Manzon Allah[S]yayi,wato bayan ya bar makka a kan hanyarsa ta komawa madina,sai ayar ta sauka a wani waje da ake ce masa ghadir-khum.wasu ‘yan milamilai tsakanin su da birnin Makka.Kuma shi wannan waje na ghadir-khum,wata mararraba ce da hanyoyi suka rarrabu zuwa Madina,Masar,Sham da Iraki.To a wannan waje ne na ghadir khum, Mala’ika Jibril[AS]ya sauko wa Manzon Allah[S]da wannan aya.Saboda haka sai ya tsaya a wajen,ya kuma bada umarni na cewa,wadanda suka kama hanyar garuruwan su,ace su dawo.misali wadanda suka kama hanyar sham,masar da dai sauran su.Wadanda kuma basu iso ghadir khum din ba daga makka,ManzonAllah[S]ya tsaya sai da suka iso.Ranar da wannan al- mari ya faru ranar Alhamis ne,18 ga watan zul-hajji,shekara ta goma bayan hijira.Bayan                                                                                                  da aka taru,adadin wannan taro malamai sunyi sabani akai,akwai wadanda suka tafi akan cewa a dadin ya kai sama da dubu dari, a kwai kuma wadanda suka tafi a cewa kasa da haka ne.koma dai minene adadin, taro ne mai yawa.Kuma wannan taro ba rana daya aka yishi aka tafi ba.A’a  sai da aka kwashe kwana ukku a wannan waje na ghadir khum,saboda haka abubuwa da yawa sun faru a cikin waddannan kwanuka.Amma ga guda biyar daga ciki.1-KHUDUBA:Kafin hudubar,Manzon Allah[s]yasa a kira sallah bayan nan ya jagoranci sallar Azahar,bayan kammala sallah ya hau mumbari wanda aka yishi da siridda na dabbobi da dai sauransu,sa annan yace ma Imam Ali[AS]ya hawo kan mumbarin,ta yadda kowa zai iya ganin su.Bayan haka sai Manzon Allah yayi huduba mai tsawo,wanda a tarihin sa ba huduba mai tsawo da yayi kamarta.Hudubar ta kunshi bangarori dabam dabam.Wanda a cikin ta Manzon Allah[S]ya bayyana RAS MIYYAN wato OFFICIALY wadanda zasu kasance khalifofi a bayan sa.Adadinsu da kuma sunayen su,su goma sha-biyu ne,na farkon su Imam Ali [AS] na karshen su Imam Mahdi[AS]a cikin khudubar sunan Imam Ali[AS] yazo a waje 40,kalmar Aimma waje 10,Imam Mahdi[AS]waje 20,da dai sauran su.Har wala yau,a lokacin da Manzon Allah[s]ya ke khudubar akwai inda ya daga hannun Imam Ali[AS]sama yace “Duk wanda na kasance shugabansa ne,to wannan ALI ma shugabansa ne,Allah ka jibinci wanda ya jibin ce shi,ka ki wanda ya kishi,ka taimaki wanda ya taimake shi,ka tabar da wanda ya tabar da shi.”2-Bayan wannan huduba,Manzon Allah[s]ya sa ma Imam Ali[AS]Rawani, na muamman,sunan rawanin SAHAB.Asalinsa na Manzon Allah ne [S]Mala,iku suka zo masa da shi a yakin Badar. 
                3-WAKE:Bayan haka wani mawaki sahabin Manzon Allah mai suna Hassan dan sabit ya nemi iznin Manzon Allah[S]ya ba shi dama yayi wake kan wannan al-amari na ghadir,Manzon Allah ya ba shi  dama yayi waken,ga mai bukatar ganin waken yana iya duba littafan da aka ambata sama.                                           4-BAI’A:Bayan haka ,Manzon Allah[S]yasa ayi hemomi  guda biyu,domin yin bai’a,ya zauna a daya,yace Imam Ali ya zauna a dayar,Haka aka ci gaba da yin wannan bai’a har kwana ukku,Domin kowa sai da yayi, har da mata,amma da aka zo kansu Manzon Allah[s]ya sa akawo ruwa ne a cikin kwarya,ko wace tazo, sai ta saka hannun ta a ciki.wato a matsayin tayi bai ‘a.wani tambihi a nan shine,cikin wadannan mataye har da iyalin manzon Allah[s]baki dayan su.Domin yazo akan cewa a wannan tafiya aikin hajji da su ya tafi dukkan su.Haka nan yazo akan cewa,a cikin wadannan kwanaki ukku  da ake wannan bai’a,Manzon Allah[s]yana  yawan cewa,Ku taya ni murna,Allah ya keban ceni da Annabta,ya kuma keban ce Ahlu-bai-tina da imamanci.
5-MU’UJIZA:Yazo akan cewa a karshen yini na rana ta ukku,wata mu’ujiza ko aya ta bayyana.yadda abun ya faru ko shine,wani mutum da a ke cema Haris al-fihiri,yazo wajen Manzon Allah[S]ya ce masa “Ya ubangiji in wannan gaskiya ne daga wajen ka ne[wato nada Imam Ali a matsayin khalifa]ka ai ko mana da duwatsu daga sama ko kuma kazo mana da azaba mai radadi”An ce nan take a wajen,Allah[T]ya aiko dutse daga sama ya samu kansa ,ya fita ta duburar sa,nan take kuma ya mutu.Wani abun mamaki shine bayan da manzon Allah[s]ya gama huduba,sai wasu suka koma gefe suna,tattaunawa kan wannan abu.Wani cikin su yace Manzon Allah yayi hauka[Wal’iyazu billahi] wani yace ba hauka bane,son rai ne ka wai,sai wani yace koma hauka yayi ko son rai ne,to abin da ya fadi ba zai yiyu ba.Saboda haka akayi  kulle-kulle ,na  kashe Manzon Allah[S] kan hanyarsa ta komawa Madina.Allah[T]ya tona asirin su,ya kiyaye Manzon Allah[s] ya isa Madina lafiya.Bayan komawar sa madina akwai lokacin daya bukaci akawo masa tawada ya rubuta, abinda in suka yi riko da shi a bayan sa ba zasu bace ba,nan ma aka yi haya niya wani ya hana yace kur’ani ,ya wada cesu,ya shirya rundunar yaki karkashin Usama dan Zaid,aka ki  tafiya.Ire-iren wadannan abubuwa da suka faru,tsakanin ghadir da wafatin Manzon Allah[kwana 70 ne tsakani] suke nuna lalle al-amarin ghadir ya kasance jarabawa babba ga manzon Allah [s].Domin in mutum yayi tunani sosai,zai ga cewa dukkan jarabawowin da Manzon Allah[S]ya fus kanta  a rayuwarsa,zafinsu da dacinsu a zuciya bai kai wadanda ya fuskanta a cikin wadannan kwanaki 70 ba,na karshen rayuwarsa.Domin in mutum ya dubi wadancan matsaloli zai ga mafi yawan su matsaloli ne na waje,amma wadannan matsaloli ne, na cikin gida,saboda haka jarabawar sa tafi tsanani.Wannan ke nan a takaice dangane da abubuwan dasuka faru aranar ghadir khum.                                          3-Tawili da kuma kwas kwarima da aka yima al-amarin ghadir a littafan Ahlus-sunna:-Idan mutum yayi bincike a littafan Ahlus-sunna,kan al-amarin ghadir,zai ga babu  wani abu  da aka yi masa tawili ko aka jirkita shi,kamar hadisin ghadir.Kasantuwar in kari ko musa ,asalin aukuwar al-amarin bazai yiyu ba.Shi yasa aka dauki matakai na tawili da kuma kwas-kwa-rima,ga hadisin ghadir.Baya ga haka kuma,in mutum ya bibiyi Matanin hadisin ghadir a littafan Ahlus-sunna,zai ga sun  yayyayen keshi,kaga nan an kawo wani yanki,can an kawo wani sashe, wato gutsi-gutsi a kayi da shi.Shi yasa kammalalliyar hudubar da Manzon Allah[S]yayi ,a ranar ghadir,baki daya babu ita a littafa n Ahlus-Sunna,sai dai, kai tacin karo da yanki-yankin ta ,alittafai.Saboda haka samun cikakkiyar hudubar,sai a littafan shia.Ga misalin haka,a littafin Hadis na sunna.Mutum ya duba littafin Riyadhu-Salihin,babin dakemagana kan girmama,Ahlu baitin Manzon Allah,Hadisi na farko a babin,An samo daga dan Hibban,yace,mun tafi ni da Husain dan sabarata da Amru dan Muslim,zuwa ga,Zaid dan Ar-kam.Lokacin da muka zauna gaban sa,sai Husain yace masa.Lalle Zaid ka hadu da al-hairi mai yawa,kaga Manzon Allah[s]ka kuma ji daga gareshi,kayi yaki tare dashi,kayi sallah a bayan.Saboda haka ya Zaid,ka fada mana wani abu da kaji daga Manzon Allah[S]sai Zaid yace wallahi na tsufa,na manta wasu abubuwan da naji daga Manzon Allah[S].Bayan haka sai ya ce masu,wata rana Manzon Allah[S]ya tsaya a cikin mu ya na mai khuduba,a wani tabki na ruwa a nace masa KHUM,yana tsakanin makka da madina ne.Yai godiya ga Allah,yai yabo ga reshi,yai waazi kuma ya tunasar[wato a hudubar]saannan yace bayan haka:Yaku mutane,ni mutum ne,yayi kusa Manzon  ubangiji na yazo in amsa masa[wato kusantowar  wafatinsa]Saboda haka na bar maku nauyaya guda biyu,na farkon su littafin Allah,cikinsa akwai shiriya da haske.sa annan kuma yace,da Ahlu-baitina,ina tunasar daku Allah game da Ahlu-baitina.”Muslim ne ya ruwaito hadisin.kuma  iyaka  abunda  aka yanko daga khudubar ghadir ke nan,a hadisin.Can kuma wani Hadisin,a binda aka yanko a hudubar shine,Manzon Allah yace a ghadir-khum,Man-kutu maulahu,fahaza Aliyu maulahu.shi kuma abunda aka yanko kenan.A takaice dai haka aka gutsutsura hadisin ghadir a littafan Ahlus-sunna.Dama ace abun ya tsaya ga haka,A’a wadanda aka kawo a gutsutsure din,sai aka yi  masu tawili ko aka canza su.misali  wadannan hadisai biyu da aka kawo,Kalmar maula anan suka tafi akan cewa, wai tana nufin masoyi ko mai taimako,ba wai shugabanci ba.Al-hali su wadanda akayi abun gaban su ,sun fahimce ta , a matsayin shugaban ci.Kuma mutum ya auna da hankalin sa,ace manzon Allah ya tara irn waddanan, jama’a waje daya,kuma cikin zafin rana,saboda ya shaida masu yana son Imam Ali,saboda haka suma, su soshi.Haka nan kuma a daya hadisin,kalmar ,wa Ahlu baitiy sai aka canza shi da Wa-sunnatiy,a wasu hadisan.Kai hatta ma,ayoyin da suka sauka a ghadir khum,suma an canza Makan na Nuzul dinsu,wato wajen da suka sauka.Wai Ayar Alyauma akmaltu lakum dinakum,a ,Arfa ne ta sauka.Ayar kuma Ya ayyuhar Rasul ballig ma unzila ilaik.Wai a makka ta sauka.Al hali Suratul Ma’ida,Ai Madaniyya ce  ba Makkiyya ba.Da dai abubuwa da dama da akayi tawilinsu ko aka canza su,dangane da,al-amarin ghadir.Baya ga haka kuma,mu duba a farkon ai-amari,yadda aka dauki matakai na hana rubuta hadisai na Manzon Allah[S] da kuma watsa su.Ba dun komi ba face saboda danne wannan al amari na ghadir.Amma Allah[T]bisa ikonsa,ya hukumta wannan al-mari na ghadir ba zai boyuba.Wannan kenan a takaice dangane da tawili da kuma canje-canje da aka yima al-amarin ghadir.                                                       4-Ayyukan da  akeyi a Ranar ghadir:-Akwai ayyuka na Ibadodi ,da suka zo daga Manzon Allah[S]da kuma Aimma na Ahlul-bait[AS]wadanda ake son yin su ,a daren ghadir da kuma ranar ghadir.Wanda wadannan ayyuka suna da falaloli masu yawan gaske.A daren ghadir,akwai wata sallah mai,Raka’a  goma sha-biyu,yadda ake yin sallar mutum na iya duba littafin Ik-bal na sayyid ibn Dawus.Da yake babu ita acikin littafin Matihul-jinan.Haka nan a daren  akwai, wata addu’a da ake biyawa.Ita ma mutum ya duba a littafin Ik-bal din.Sai kuma ranar ghadir,ayyukan da suka zo sune:1-Azumi .2-Wanka.3-Ziyarar Imam Ali[as].daga kusa ko nesa.4-Sallah raka’a biyu,yadda ake yinta mutum na iya duba Mafatihu.5-Biya dua’un Nudba.6-karanta wata addu’a da aka samo daga shaikhul Mufid,ita ma akwai ta cikin mafatihu.7-Taya juna murna,ta fadin cewa “Al-hamdu lillahil-lazzi-ja’alana minal-mutamassikina,biwi-layati Amiril ma’uminin,wal-aimma [as]”Da dai sauran ayyukan da ake son aikatawa a ranar.kuma kamar yadda aka ambata wadannan ayyuka ,an samo sune daga Ma’asumin [AS] misali yazo akan cewa an tambayi Imam Sadik [AS]mi ya kamata mutum yayi ranar ghadir?sai yace.Azumi,ibada,yawaita yima Manzo salati da Alayen sa.Kuma kiyaye irin wadannan ayyuka na  Munasabobi yana da gayar muhimmanci.Domin rashin kiyaye war zai sa mutum ya dun ga hasarar lada mai yawa,misali wannan azumi da ake son yi a ranar,yazo a kancewa wanda yayi shi,za a kan kare masa zunubin shekara sittin,a wata ruwaya kuma yana da lada kamar ya kasance kullum yana azumi ne,a wata ruwayar kuma yana da lada  kamar wanda yayi hajji da umra,sau dari.Mu duba  irin wadannan falaloli.Kuma idan mutum ya saba yana kiyaye wadannan ayyuka na munasabobi,ko da sun zagayo,sai uzuri  ya hana shi aikatawa misali rashin lafiya,tafiya da dai makaman tansu.To za’a ba mutum  lada kamar ya aikata su.sabanin ko mutum idan jefi-jefi ,yake yin su,shi ba zai samu irin wannan ladar ba.Saboda haka  duk watan da ya kama ,mutum sai ya bincika yaga wadanne munasabobi ne ke cikin watar.domin mutum ya aikata su.mutum ya dun ga yin haka,har ya zama masa malaka wato  jiki.Misali yanzu munasabar  da ke gabammu itace ta yaumul-mubahala,wato 24 ga watan zul hajj.ita ma akwai ayyuka da suka zo a ranar,mutum na iya duba mafatihu.                                                                                                                     5-Kafa hujja da Hadisin ghadir a kan wasu mutane da,Ahlul bait[as] sukayi.Idan mutum ya bibiyi tarihin Aimma [AS]zai ga wani lokaci cikin lokuta,sun kafa hujja da hadisin ghadir,misali Imam Ali[as]ya kafa hujja da shi, a wajaje dabam-dabam,misali a ranar shura,a yakin jamal,a yakin siffin,a kufa,da dai sauransu,Haka nan ya kafa hujja da shi a kan dai-dai kum mutane,wadansu sun tabbatar wasu kuma suka boye.yai addu’a,akan su,kuma ta kama su,wato wadanda  suka boye din,cikin su,akwai wanda ya makance,akwai kuma wanda ya kutur-ce da dai sauran su,Haka nan Sayyida Fadima[as]i tama ta kafa hujja dashi.Haka nan Imam Hasan da Imam Husain [AS].Haka nan Ammar dan Yasir shima ya kafa hujja da shi a yakin siffin.Haka nan Umar dan Abdul-aziz,shima ya kafa hujja da shi,da dai sauran mutane masu yawa,da suka kafa hujja da hadisin ghadir,a kan cewa I mam Ali[as]shi ne khalifan Manzon Allah,mubasharatan bayan sa.                                                                                                                                                                            6-Illolin da suka auku,saboda rashin bin umarnin Manzon Allah[s]dangane da al-amarin ghadir,wadannan illoli a bayyane suke.Duk abubuwan da suka faru a wannan Ai- umma ta manzon Allah[S] tun daga farko har yau din mu,Asasi da kuma sabab din aukuwar su,shi ne rashin aiwatar da al-amarin ghadir ne.misali da an ai watar da al-amarin ghadir,mutum fajiri,fasiki irin  Yazidu[LA]zai iya zama khalifa,ballantana yayi abunda yayi.Saboda haka illolin da haka ya haifar suna da yawa.Ga wasu daga ciki,1-An she, hakki daga hannun masu hakki,da Allah[T]yaba,wato na khalifanci.Baya ga haka kuma aka cutar da su aka gallaza masu,mutum ya bibiyi tarihin Aimma[as]daya bayan daya,wato tun daga Imam Ali [as]har ya zuwa imam Mahdi[AS]yaga ko wannen su yaddu aka cutar dashi ,aka gallaza masa,daga karshe kuma ko wannen su daga wanda aka kashe da takobi[kamar Imam Ali da Imam Husain]sai wanda aka sama ma guba,Abin  mamaki ma shine Imam Mahdi[as] tun gabanin a haife shi ana nemansa akashe shi.Wato shigen na Annabi Musa[as] da Fir’auna.Baya ga haka kuma aka cutar da wadanda sukayi Riko da su,ta fuskoki dabam-dabam,kisa ne,dauri ne, kora daga kasa,cutarwa- ta,fatan baki da dai sauransu.in ma mutum bai san na zamanin da ba,to ya duba na wannan zamani da yake ciki,yaga yadda ake cutarwa da gallazawa ga mabiya Ahlul-bait[as] a sassan duniya dabam-dabam.2-Daga cikin illolin da wannan abu ya haifar,akwai gina mutane akan jabun addini,wato ga ainihin koyar war Manzon Allah[s]akan abu,sai  a barshi,agina mutane kan wani abu dabam,wato abinda  ake cema,IJTIHAD-MAKABILI-NAS.mutum ya duba tarihin khalifofi zai ga haka.Wanda ire-iren wadannan abubuwa,Imam Mahd[as]ne kadai zai gusar da su idan ya bayyana.Domin yazo akan cewa,duk wani abun da aka sa shi acikin addini wanda babu shi a lokacin Manzon Allah[S]sai ya gusar da shi.Duk kuma wani abu wanda akwai shi a addini,amma aka debe shi,to sai ya dawo da shi.Akwai mislai da yawa,na gina mutane kan abun da ba dai dai ba,a lokaci guda kuma suna ganin addini ne.Mu duba yadda aka gina mutane kan al-amarin Ashura,a duniyar Ahlus-sunna.3-Daga cikin  illolin da wannan abu ya haifar,Akwai sabani da rarraba ga wannan Al-umma ta Manzon Allah[s]Saboda haka duk wani sabani da rarraba da muke gani tsakanin musulmi,a yau,da kuma wanda ya auku daga magabatan mu,to asasin abuda ya haifar dashi,shine rashin aiwatar da al-amarin ghadir.4-Daga cikin illolin da wannan abu ya haifar,akwai takai-tuwar ,amfana da wadanda Manzon Allah ya bayyana su,a matsayin khalifofi a bayan sa ranar ghadir.Misali Imam Ali [as]ya rayu bayan Manzon Allah[s]shekara talatin,mutum yayi tunani,wadannan shekaru 30,da Imam Ali yayi su a khalifanci,kai tsaye bayan manzon Allah,wane irin gayar amfanuwa,wannan al-umma zata samu,mu duba shekaru biyar da yayi na khalifanci,irin natijojin da aka samu,duk ko da yayi sune cikin matsaloli dabam dabam.misali Nahajul-Balaga,hudubobin sane da wasikunsa da zantukan sa,da yayi, a wadannan shekaru  biyar  na khalifancin shi.Mu kuma duba ilimomi da aka samo daga Imam Sadik da Imam Bakir [AS]saboda yana yi da suka samu na bada ilmin.To me ake tsammani da ace wannan imamai 12 sun gudanar da khalifanci,irin amfanuwa da za a yi dasu,wani abun mamaki su wadanda suka kwace khalifanci daga wajensa, in ta kuke masu a fagen ilimi suna komawa ne gare su.mutum ya binciki tarihi zai ga haka.                          7-Darussa da zamu koya daga wanna al-amari na ghadir,Akwai darussa masu yawan gaske a cikin wannan ai-amari na ghadir,ga wasu daga ciki.1-Sallama ma hukuncin Allah[T] wato yana da muhimmanci,mutum ya kasance,a rayuwarsa,mai sallamawa ga abun da Allah[t]ya hukunta,misali wannan al-amari na ghadir,haka Allah[T]ya hukunta,shi ya zabi wadannan bayin Allah,akan su kasance khalifofi bayan Manzon Allah,saboda haka miya hau kan mutum,sallamawa,domin yin haka shine zaman lafiyar mutum duniyar sa da lahirar sa.Domin ko a ranar ghadir din,akwai wadanda suka zo suka samu Manzon Allah[s] suna tambayar sa,wannan abu daga wajen Allah ne,ko daga wajen ka.Manzon Allah[s]yace masu daga waje Allah ne.Amma wasu da yawa saboda Hassada ya kai su da inda ya kaisu.saboda haka,akwai abun lura anan.2-Muhimmancin kyakkyawan karshe a rayuwa,in muka dubi ranar da wannan al-mari ya faru.yadda kowannen su yayi bai’a ga Imam Ali[AS]akwai ma wadanda har taya shi murna sukayi cewa ya zama shugaban su da kuma dukkak muminai.Amma kuma duk da haka daga baya mutum ya canza,wannan akwai abun tsoro a ciki.Akwai kuma wadanda suke har bayan zaben sakifa,suna bayan Imam Ali[as]suma daga baya suka canza.saboda haka mutum ya kasance mai yawan tunanin akibar sa,a addinance yana da muhimmanci.3-Illar saba ma manzon Allah[s] Idan mutum ya dubi,abubuwan da suka auku,ga wadanda aka yi wannan al-amari na ghadir gaban idon su,abun yana da ban tsoro da kuma tada hankali,ga kuma fadin Allah[T]wadanda suke saba ma,umarnin manzon Allah,su ji tsoron kada fitina ta same su ko azaba mai radadi”mu duba irin fitinonin da suka gudana,a lokacin.mutum ya binciki tarihi ,zai ga haka.mu duba,abubuwan da suka faru,a madina  lokacin da yazid ya halatta ta ga mayakan sa kwana ukku,yadda aka ci mutuncin wadanda akayi wannan abu gaban idon su,aka ma’ya’yan su fyade,akwai ma sahabin da suka shiga gidan sa duk da ya tsufa sosai,amma haka suka kama shi suna fisge mai gemunsa daya bayan daya,da dai sauran su.mutum ya duba cikin Tarihul-khulafa na suyudi zai ga haka.mutum ya yi tunani da ba’a saba ma umarnin ManzonAllah ba,haka zai faru?wato na irin wadannan fitinoni,da cin mutun ci.                                                                                                                  8-Natijojin da za a samu da an ai watar da al-amarin ghadir.Tabbas da an aiwatar da Al-amarin ghadir,da an samu natijoji masu yawan gaske,a duniyan ce,da addinan ce da kuma a lahiran ce.Aduniyance  da an samu zaman lafiya,yelwar arziki,izza akan wadanda ba musulmi ba,da dai sauran su,na ni’imomin duniya.A addinan ce kuma da an samu fahimta sahihiya ta addini,wato ba gurba-tacciyaba.kamar yadda mafi yawa ake akai yanzu.A lahiran ce kuma  mutum ya samu tsira,da ga azabar Allah da kuma shiga cikin rahamar sa.Domin ba dadi ace mutum ya rayu a gidan duniya,gobe kiyama ta bayyana masa akan cewa,abinda yake akai,ko kuma,wadanda yayi riko dasu a matsayin khalifofin manzonAllah ,ba haka abun yake ba,Saboda haka kira anan musammam ga ‘yan uwanmu musulmi Ahlus-sunna,da suyi bin cike a littafan su,kan wannan al-amari na khalifanci.domin shine a sasi na sabani tsakanin shia da sunna.kuma wani abun mamaki shine,hujjojin shia kan wannan mas’ala ta khalifanci,zasu iya tabbatar da su a littafan sunni,misali cewa khalifofi goma sha-biyu ne,ya na nan a cikin littafin hadis na Buhari,Muslim da dai sauran su.Amma da mutum zai samu malamin sunni,yace yana  son ya nuna mai hadisi da yazo daga Manzon Allah,da yace,khalifofi a baya na gu da hudu ne,ba zai,iya nuna  waba koda ko hadisin mai rauni ne.kada a manta sunce manzon Allah bai khalifantar ba,wai ya barma al-umma ,ta zaba.shi kuma wanda aka zaba na farko,da zai rasu sai ya ayyana magajin sa.mutum na iya tambaya,to mai yasa shi bai yi koyi da sunnan manzon Allah,wato na ya barma alumma ta zaba,shi kuma wanda aka ayyana da zai rasu,sai ya kafa kwamitin mutum shidda,a kan su zaba,a tsakanin su,wanda aka zaba din bayan an kashe shi ,jama’a sukayo tururuwa wajen Imam Ali[as]su kace shi suke so a matsayin khalifa,saboda haka Imam Ali[as]a cikin wadannan khalifofi shi kadai ne jama’a suka zabe shi.wannan kuma wata ayane ga masu tunani.Ta yiyu wani yace a sakifa  ba zabe akayi ba?mutum ya binciki abun da kyau,zai ga mafi yawan sahabbai,basu wajen, daga baya sukaji labari, na abunda ya faru.Shi kuma Muawiya shi ya nada kansa,da zai rasu ya nada dansa Yazid,tun daga nan sai abun ya koma gado da kuma juyin mulki,wato in mutum nada maya ka, sai yakauda wanda yake akai,domin ya hau.mutum ya duba wancan littafi na suyudi da aka ambata ,zaiga wannan abubuwa da aka kawo.kuma wani abu shine,wannan littafi na Tarihil-khulafa na suyudi,to mutum ya bibiyi,rayuwar wadannan khalifofi na bani umayya da kuma banul-Abbas,ya gani zai ga cewa, Ayya ko wadannan sune khalifofin Manzon Allah?Amma da ace anbi zabin Allah[T] da, duk wannan abubuwan basu faru ba.kuma mutum yabi tarin Aimm[AS] yagani,ko wannen su anyi mai shaida cewa a zamanin sa ba wanda ya kai shi,ballantana ya wuce shi,wato ta kowa ce  fuska,a ilimi ne ,ibada ne ,Aklak ne da dai sauran su .saboda haka da ace su sukayi khalifanci a bayyane, da an samu natijoji masu yawa a wannan al-umma.                                                9-Abin da ya hau kanmu dan gane da wannan al-amari na ghadir:-Abu  na farko shi ne ya waita godiya ga Allah[T] kan wannan babbar ni’ima, da yai mana na tamas-suki da wanna wilaya ta Ahlul bait,da kuma Bara’a daga makiyan su.wannan ba karamar niima bace, musamman in mutum yayi la’akari da nahiyar da muka taso a cikin ta.Abu na biyu ,shine mutum yayi mujahada wajen ganin cewa,rayuwarsa tayi muwafaka,da koyar war Aimma[as]dai dai gwargwadon ikon sa.Na ukku mutum ya saba ma kansa,da yin wasu ayyuka na ibadodi,lokaci bayan lokaci da niyyar Allah [T]ya kai ladar gare su.misali akwai wata sallah da akeyi ga Manzon Allah da Ahlul-bait,wato da niyyar Allah ya kai ladar garesu,mutum na iya duba mafatihu,zaiga yadda ake sallar.Ko kuma  a munasabobi na wafatin su ko wiladar su,mutum yayi wasu ayyuka da nufin Allah[T]ya kai ladar gare su,misali ace ya sau ke Al-kur’ani,ko ya biya abinda ya saukaka,ko ,yai wata kyauta,da dai makaman tan su.Domin irin yin wadanan ayuka, garesu yana daga cikin kyatata,alaka da su.Na hudu,Yin wani abu domin raya wannan al-amari na ghadir,tsakan-kanin mutane,misali,a’iyalin sa,’yan’uwan sa na jini,abokan mu’amalar sa,idan shi dan makaranta ne ko dan kasuwa  ko ma’akaci da dai makamantan su.Zai yi haka ne dai dai gwargwadon ikon sa,ta hikima da kuma uslubin da za’a fahimce shi.Domin ranar da Manzon Allah[S]yayi wannan khuduba,a ghadir khum,yace wanda kenan ya sanar da wanda bai nan,uba ya sanar da dansa.                                    10-Ai’katuwar wannan al’amari na ghadir.Kasantuwar  wannan al’amari na ghadir,bai gudana,a zahiran ce ba,wato a aikace ba,kamar yadda Allah[T] ya hukumta,Manzon Allah kuma ya isar da sakon haka.To tambaya haka ya tada Ai’mma[as] daga matsayin da Allah[T]ya basu,na cewa sune khalifofin Monzon Allah a bayan sa.Amsa bai tada su.Dalilin yin wannan tambaya shine,so da yawa,malaman Ahlus-sunna,suna yawan  kawo haka,cewa idan ance sune khalifofin Manzon Allah[S] ai ba suyi shugabanci ba.Kasantuwar basu yi shugaban ciba,bai tada su daga matsayin suba na khalifofi,misali kamar Allah[T]ya aika daAnnabi ga wasu mutane,sai ya zamanto ba wanda yayi imani da shi,to haka ya tada shi daga Annabi?kuma kamaryadda ba mutane ne ke zabar Annabi ba,to haka nan shima,khalifanci na Manzon Allah[S]Allah[T]yake zaba,ya kuma zaba.Abinda ya hau kan kowa da kowa shine bin zabin Allah[T]In kuma  mutum na shakka kan haka ko ya jahilci wannan abu,to abun da ya hau kansa, yanzu shine yayi bincike,a littafan Ahlus sunna bama na shia ba,kan wannan al-amari na ghadir.kuma koda ma hadisin da yazo a cikin sahihul Buhari da Muslim na fadin ManzonAllah cewa khalifofi a baya na 12 ne,ya isa yasa mutum yayi tunani kuma ya tambayi kansa,to su waye wannan 12.In mutum yace ai 12,ana nufin  khulafai-rra-shidin,to ai hudu ne,a ,Ahlus sunna,in kuma kace khalifofin bani umayyane,su 14 ne,in kace khalifofin abbasawa ne,su,47 ne.saboda haka,inka hada adadin khalifofi na umayyawa da Abbasawa da kuma khulafa guda hudu da suka gabace su,a dadin zai ta shi,65.To kuma ga hadisi ingatance,yazo akan cewa khalifofi a bayana 12,shi yasa mafi yawan malaman Ahlus suna,basu da fahimta guda daya ko matsaya guda kan wannan hadisin.Zai yi kyau mutum  ya samu Tarikhul khulafa na suyudi,yaga yadda ya kawo zantukan fitattun malamam Ahlus-sunna kan wannan Hadisi.ko kuma wani rubutu da akayi abaya mai taken.Imama a mahangar Ahlul bait[as]da kuma Ahlus-sunna,an kawo waddanan zantukan.To bayan duk matakai da  aka dauka na ganin cewa ,wadannan bayin Allah basu yi wannan khalifan ci,A zahiran ce ba,wato basu rike iko ba.Wani abu wanda yake tabbatacce kuma saiya auku,shine cewa,cika-makin wadannan khalifofi 12,wato Imam Mahdi[AF]i dan ya bayyana  sai wannan khalifanci ya tabbata,a aikace,wato zai kasance,a lokacin duniya baki daya,zata kasance kar’kashin ikon sa.To a lokacin zata bayyana ma wasu akan cewa,a she angina mutane a tsawon tarihi kan wani abu dabam,wato akasin abinda Manzon Allah[S ]ya bayyana,A ranar ghadir khum.Saboda haka wadanda suka haifar da wannan abu,mutum zai iya ceawa sun zalinci kansu,sun kuma zalinci ‘yan’baya.                       Daga karshe babu abun da zamu ce,face godiya ga Allah[T]da yayi mana wannan babbar ni’ima ta riko da Ahlul-bait[AS]muna kuma rokon sa,ya rayar damu akai,ya karbi rayuwarma akai,ya kuma tada mu a kai.Sauran ‘yan uwanmu musulmi, muna rokon Allah[T]kamar yadda yayi mana,wannan ni’ima ta riko da Ahlul-bait [AS]suma yai masu.

No comments:

Post a Comment