Sunday 3 February 2013

Darussa 12 daga rayuwar Imam Hasan Al-Askari (AS)


Kasantuwar ran 8 ga watan jiya, wato Rabi’ul Awwal shi ne ya yi daidai da wafatin Imam Hasan Al-Askar. Kamar yadda ya zo a tarihinsa, ya rasu ne ranar Juma’a 8 ga Rabi’ul Awwal Hijira ta 260. Imam Hasan Al-askari (AS) an haife shi ne a Madina, a watan Rabi’us-Sani, sai dai an samu sa~ani dangane da ranar da aka haife shi, da kuma nawa ga wata aka haife shi.
Allama Majalisi, watau marubucin littafin Biharul Anwar ya ce abin da ya fi shahara shi ne, an haife shi ne ranar Juma’a takwas ga watan Rabi’us Sani. Amma Shaikh Mufid ya tafi a kan 10 ga watan ne a shekar ta 232 bayan hijira.
Imam Askari (AS) kamar yadda aka sani, shi ne Imami na 11 a jerin }idaya na Imamai 12, kuma ya rayu shekaru 28 ne a duniya. Ya rasu yana da ]a ]aya shi ne; Imam Mahdi (AS). Muddan Imamancinsa shekaru shida ne, kuma ya yi zamani da Khalifofin Abbasawa guda uku sune; Mu’utasim, Muhtadi da kuma Mu’utamad, kuma dukkansu su ukun nan, babu wanda bai gallaza wa Imam Askari (AS) tare da yun}urin kashe shi ba, kamar yadda haka zai zo nan gaba a bayanin jarabawowinsa, insha Allah (T).
Sunan Mahaifinsa kamar yadda aka sani, shi ne Imam Ali Al-Hadi (AS). Sunan Mahaifiyarsa Salil. Idan mutum ya bibiyi tarihin rayuwarta zai ga cewa ta kai matsayi ma]aukaki wajen kusanci ga Allah (T) da kuma tsoronsa, kuma ta kasance makoma ga Shi’a ]in Ahlul Baiti (AS) bayan wafatin Imam Hasan Al-Askari (AS). Akwai ma lokacin da Imam Ali Al-Hadi (AS) yake cewa; “Salil tsarkakakkiya ce daga aibobi na zahiri da kuma ba]ini”. A ta}aice dai ta kai mustawa Aliya a fagagen Addini. Misali a Ilimi, Ibada, ta}awa da dai sauransu kamar yadda ya zo a tarihinta.
Imam Hasan Al-Askari yana da la}ubba da yawa, amma wanda ya fi fice a ciki shi ne Al-Askari (AS), wannan la}abi nasa na Al-Askari ya samo asali ne daga sunan wata unguwa da ya zauna shi da Mahaifinsa a Samarra, wacce a yanzu tana }asar Ira}i ne. Asalin ita wannan unguwa sansani ne na maya}a, wanda Khalifan Abbasawa mai suna Mu’utasim ya kafa. Wato a wannan zamanin namu kamar a ce barikin soja.
Imam Hasan Al-askari yana da shekaru hu]u da watanni, shi da Mahaifinsa Imam Hadi (AS) suka bar Madina zuwa Ira}i. (Insha Allah idan an zo darussa 12 daga rayuwar Imam Ali Al-Hadi (AS) za a yi bayani dangane da dalilin barinsu Madina zuwa Ira}i).
Imam Askari ya rayu tare da Mahaifinsa shekara 22. Bayan rasuwarsa an birne shi a kusa da Mahifinsa. Saboda haka }abarinsu yana nan a Samarra ne a }asar Ira}i, kuma daga wannan rana ta rasuwarsa, wato 8 ga watan Rabi’ul Awwal shekara ta 260 bayan hijira, Imamancin Imam Mahdi (AS) ya fara. Ya ma zo a kan cewa ana son ziyarar Imam Askari (AS) da kuma Imam Mahdi (AS) a wannan rana ta 8 ga watan Rabi’ul Awwal. Saboda haka rayuwar Imam Hasan Al-Askari za a iya kasa ta zuwa marhaloli guda biyu;marhala ta farko daga haihuwarsa zuwa rasuwar mahaifinsa.marhala ta biyu rayuwarsa bayan rasuwar Mahaifinsa, sai kuma abin da ya shafi wasu darussa daga cikin rayuwarsa mai albarka.
1. IBADAR SA: Imam Hasan Al-Askari (AS) ya kasance mai yawan ibada. Wa]anda suka yi zamani da shi, kuma suka zauna da shi, sun tabbatar da haka. Kai hatta ma ma}iyansa sun yi furuci da haka. Ga misalin wasu daga cikin Ibadodinsa. Akwai wani da ake ce wa Muhammad Shakiri ya ce; “Imam Askari (AS) yakan zauna ya yi sujuda a wajen Sallarsa in je in kwanta har in tashi daga barci, amma in samu bai ]ago daga sujudar ba”. Wato wannan yana alamta tsawaitawarsa a sujuda idan ya yi.
Khalifan Abbasawa mai suna Mu’utamad lokacin da ya sa shi a kurkuku sai aka fa]a masa ai kullum Azumi yake, kuma kowanne dare baki ]ayansa yakan raya shi da Salloli. Akwai wani da ake ce wa Muhammad [an Isma’il shi me ya fa]i makamancin haka. Ya ce; “Imam Askari a kurkuku ya kasance mai Azumi kullum, ya kuma raya dare dukkansa. Ya kasance bai shagaltuwa da komai face Ibada”.
Wa]anda suka tsare Imam Hasan Al-Askari (AS) sun fa]a wa mai kula da kurkukun cewa ya }untata masa, kada ya sassauta masa ko ya yalwata masa. Shi ne mai kula da kurkukun yake ce masu. “To me zan yi masa alhali kun wakilta mafi sharri daga cikin mutane su biyu domin su musguna masa da kuma }untatawa gare shi, amma yanzu sun zama bayin Allah (T) waje Ibada na Salloli da Azumi?
Jin haka, nan take su wa]annan jami’an Hukuma na Abbasawa suka sa aka kira wa]annan Gandirobobi guda biyu. Da suka zo, sai suka ce masu; “Menene sha’aninku dangane da wannan mutum?” Sai suka ce masu. “To, mu dai tunda aka kawo shi wannan kurkuku kullum Azumi muka ga yake yi, dare kuma baki ]aya yana Ibada. Ko magana ma bai yi, ya shagaltu ne kawai da ibada”.
Jin haka sai su wa]annan jami’an Hukuma na Abbasawa suka fice daga kurkukun a fusace. Domin ganin cewa su wa]annan Gandirobobin guda biyu su suka fi kowa mugunta da kuma bushewar zuciya, shi ya sa aka ji~inta masu }untata wa Imam Askari (AS), amma sai aka samu akasin haka, wato sai suka tasirantu da zamansu da Imam Askari (AS) har ta kai ga su ma suna aiki irin nasa na Ibadodi, wato Azumi da kuma Salloli.
Imam Hasan Askari (AS) ya kasance mai yawan Addu’o’i, musamman ma a }unut ]in Sallolinsa, kamar yadda ya zo a tarihinsa. Akwai ma wata Adddu’a ya kasance yakan biyata a }unut ]in Sallolinsa. Addu’ar ita ce “Allahumma wa }ad shamilana zaigul fitan…….” Malam ma, wato Sayyid Zakzaky (H) ya kasance yana yawaita biya wannan Addu’a ]in a }unut ]in Sallolinsa. Domin in mutum ya dubi wannan Addu’a zai ga ta }unshi hali da kuma yanayi na fitinoni dakuma jarabawowi da al’ummar Musulmi, musamman ma mabiya Ahlul Bait(AS) suke ciki a wannan zamani na gaiba da kuma neman mafita daga wajen Allah (T).
2. AKLA{ [IN SA: Imam Hasan Askari (AS) a wannan fage na Akla}, a zamaninsa ba wanda ya kai shi balantana ya wuce shi, domin su A’imma (AS) kowanne Imam a zamaninsa, to babu wani fage daga fagage na addini da za a ce an samu wani ya kai shi ballantana ya wuce shi. Mutum ya bibiyi tarihin Imamai ]ayan bayan ]aya a dukkan fagage na Addini zai ga haka. Misali a fagen Ilimi, Ibada, Akhla}, Mujahada da dai sauran su. Kuma wannan shaida ta fifikon Imamai (AS) ga mutanen zamaninsu a fagagen na addini ba wai daga mabiyansu ba ne kawai, a’a hatta wasu daga cikin Malaman Ahlus Sunnah da suka yi zamani da su sun tabbatar da haka. Wani abin mamaki ma shi ne, hatta wasu daga cikin Malaman Ahlul Kitab, wato Yahudu da Nasara sun yi shaida a kan haka, musamman ma a fagagen Ilimi, wanda da yawansu wannan shi ne ya zama sanadiyyar musuluntarsu. Idan mutum na son ya ga irin wannan shaida ta fifiko da Malaman Ahlus Sunnah da kuma Ahlul Kitab suka yi wa Imamai (AS) da suka yi zamani da su, ya duba littafi mai suna A’IMMATUNA, zai ga marubucin wannan littafin a tarihin Imamai 12 da ya kawo, na kowane Imami daga cikin Imaman nan (AS). Wato tun daga Imam Ali (AS) zuwa Imam Mahdi (AS) zai ga ya fitar da babi mai taken “zantukan Malamai gare shi”. To zai ga wannan shaida ta fifikon kowane Imami a zamaninsa a dukkan fagage na addani. Ga wasu misalai na Akla} ]in Imam Askari (AS)
A. KYAUTAR SA: Imam Askari (AS) ya kasance mai yawan kyauta. Akwai wani mutum da abubuwa na rayuwa suka tsananta masa, shi da ]ansa, sai shi wannan mutumin ya ce wa ]an nasa; “Abubuwa sun yi mana tsanani, mu tafi wajen wannan mutum (yana nufin Imam Askari) domin an ce mutum ne mai yawan kyauta”. Sai ]an ya ce wa Baban nasa; “To ka san shi ne?” Sai ya ce; “Ni ban san shi ba, ban ma ta~a ganin sa ba, ina dai jin labarin sa ne”. Saboda haka sai suka tafi wajen Imam Askari (AS), to a kan hanya kafin su isa, sai shi uban yake ce wa ]an nasa; “Ina ma dai a ce ya ba ni Dirhami 500 ka ga Dirhami 200 in sayi tufafi, Dirmahi 200 in biya bashi, Dirhami 100 kuma in sai kayan abinci”. Sai shi ]an a cikin ransa, wato bai fa]a wa Baban nasa ba, ya ce; “Ina ma dai ni ma ya ba ni Dirhami 300, Dirhami 100 in sayi dabbar da zan dinga hawa, Dirhami 100 kayan abinci, Dirhami 100 in sayi tufafi”.
Da suka isa gidan Imam Askari (AS) suka yi sallama da kuma bayanin matsalolinsu, lokacin da za su tafi sai Imam Askari (AS) ya ba uban Dirhami 500, ]an kum ya ba shi Dirhami 300. Wannan }issar ta nuna mana kyauta da kuma karama ta Imam Askari (AS), domin kowannansu ya samu abin da yake fata da kuma burin samu a wajen Imam Askari (AS).
Haka nan akwai wani mutum da aka yi wa haihuwa a lokacin yana cikin }unci na rayuwa, sai ya rubuta takarda ga wasu yana neman su taimaka masa, amma bai samu biyan bu}ata ba. Sai ya yi tunanin cewa bari ma ya je wajen Imam Askari (AS) wata }ila ya samu muwafa}a. Ya same shi ya shaida masa hali da yake ciki. Sai Imam Askari (AS) ya ba shi Dirhami 400 ya ce ya yi ]awainiyar haihuwar da su, ya kuma yi masa addu’a, ya ce; “Allah ya sa albarka ga abin da aka haifa.
Akwai kuma }issar wani da ya tsaya a kan hanyar da ya san Imam Askari (AS) yana bi. Lokacin da ya ga Imam Askari (AS), sai ya yi masa bayanin halin da yake ciki na bu}ata, har ma yake rantse masa ko Dirhami ]aya bai da shi, abin ma da zai ci a ranar bai da shi. Sai Imam Askari (AS) ya ce masa; “Yanzu kana rantsuwa da Allah kan }arya, alhali kana da Dirhami 200 ka ~oye su? Amma ni ba ina fa]in haka ba ne saboda kada in ba ka wani abu”. Sai ya ba shi Dirhami 100. Mu duba Akhla} na Imam Askari (AS) da kuma karamarsa.
Akwai kuma wani da ake ce wa Abu Hashim Al-Ja’afari lokacin yana tsare a kurkuku ya rubuto wa Imam Askari (AS) halin da yake ciki a kurkuku na matsaloli da kuma tsanance-tsanance, sai Imam Hasan Askari (AS) ya rubuta masa cewa; “Yau za ka yi Sallar Azahar a gidanka”. Ilai kuwa, kafin Azahar aka sake shi ya yi Sallar Azahar ]in a gidansa. Shi ne Imam Askari (AS) ya aika masa da Dirhami 100, ya ce kuma in yana da wata bu}ata kada ya ji kunya ya gabatar da ita zai samu biyan bu}ata insha Allah.
Mu duba ita ma wannan karama da kuma Akhla} na Imam Askari (AS). Akwai misalai da yawa na kyautarsa, amma ba za a iya kawo su ba saboda gudun tsawaitawa.
B. AFUWARSA: Imam Askari (AS) ya kasance mai yawan afuwa da kuma kau da kai daga masu cutar da shi. Akwai ma lokacin da yake fa]a wa wani daga cikin mabiyansa cewa idan ya ji wani mai sukar sa ko zagin sa, ya wuce kada ya amsa masa ko kula shi, ko ya nuna masa shi waye.
Akwai lokcin da Imam Askari (AS) yana tsare a kurkuku, to ]aya daga cikin ma’aikatan kurkuku ya kasance mai yawan gallazawa ga Imam Askari (AS), amma sakamakon Akhla} ]in da ya gani na Imam Askari (AS) wannan ya canza masa tunani, sai da ya kai saboda girmamawarsa ga Imam Askari (AS) da kuma jin nauyinsa bai iya ]aga ganinsa ya dubi Imam Askari (AS). Wuce nan ma, daga baya ya zama cikin mabiyansa. Mu duba yadda kyakkyawan Akla} ke canza }iyayya zuwa soyayya da kuma biyayya.
Akwai kuma lokacin da aka tsare Imam Askari (AS) a kurkuku shi da wani ]an uwansa na jini da ake ce wa Ja’afar, daga baya sai aka saki Imam Askari (AS) ban da Ja’afar ]in, shi ne Imam Askari (AS) ya ce ba inda zai je idan ba saki Ja’afar ]in ba. Ganin haka shi ma Ja’afar ]in aka sake shi. Da dai misali da yawa na Akla} ]in Imam Askari (AS) ta fuskoki daban-daban.
3. JARABAWOWIN SA: Imam Hasan Al-Askari (AS) duk da cewa ya rayu a duniya }asa da shekaru 30, amma a cikin wa]annan shekaru ya fuskanci jarabawowi daban-daban, ta kuma fuskoki daban-daban, musamman ma ta fuskacin masu tafi da iko. Domin Khalifofin Abbasawa guda uku da ya yi zamani da su babu wanda bai }untata masa ba da kuma yun}urin kashe shi, dama sa shi a kurkuku. Shi ya sa in mutum ya bibiyi tarihin Imam Askari (AS) zai ga ya yi zaman kurkuku a lokuta daban-daban, kuma ba wai kawai zaman kurkukun ba, a’a, har da umurnin cewa a gallaza masa.
Akwai ma lokacin da suka ta~a wakilta wani da ake ce wa Nahriri, ya tsare shi. Shi wannan Nahirir ]in ya kasance mutum ne maras tausayi, mai gallazawa mutane. Shi ne a lokacin matarsa take ce masa ya ji tsoron Allah dangane da Imam Hasan Askari (AS). Ta ce masa tana ji masa tsoro idan ya }untata masa wani abu zai same shi. Maimakon ya amshi wannan nasiha tata, sai ma ya da]a }aimi. Saboda bushewar zuciya, ya ce mata ai sai ya sa shi a cikin ]akin zakoki.
Wani abin mamaki da Khalifofin Umayyawa da Abbasawa suka yi a lokacin su shi ne; a kurkuku akan yi ]aki wanda ake sa zakoki a ciki, akan kuma yunwatar da su. To a cikin fursunoni wa]anda aka yanke wa hukuncin kisa akan jefa mutum cikin ]akin wa]annan zakoki a matsayin abincinsu. Mu duba irin wannan zalunci. To sai shi wannan mutumin mai suna Nahriri ya nemi izinin yin haka daga masu tafi da iko na lokacin, na a kan ya jefa Imam Askari (AS) cikin wannan ]aki na zakoki. Suka ba shi izinin yin haka.
A bayan da ya je ya aiwatar da wannan abin da ya yi nufi. Washegari sai ya zo domin ya ga abin da ya faru sai ya tarar da Imam Askari (AS) yana tsaye yana Salla, wa]annan zakoki kuma na gefensa! Allahu Akbar ! Ganin haka umurni ya zo a kan a saki Imam Askari (AS). Mu duba wannan babbar karama ta Imam Askari (AS).
Baya ga wannan jarabawa da Imam Askari (AS) ya fuskanta daga azzalumai masu tafi da iko na zamaninsa na zaman kurkuku. Akwai jarabawa da ya fuskanta na sa masa ido da kuma kange shi daga mu’amala da mutane, duk da cewa Imam Askari (AS) yana zaune ne a sansani na maya}a, amma haka bai hana sa masa ido na le}en asiri ga dukkan mu’amalolinsa ba. Wani abin mamaki ma shi ne, hatta zaman sa a cikin kurkuku, sai da aka ha]a shi da ]an le}en asiri, da sunan cewa wai shi ma fursuna ne, amma a ~oye aikinsa shi ne ya dinga tattara bayanai na zantukan Imam Askari (AS) shi da mabiyansa da suke cikin kurkukun yana aiko wa masu tafi da iko.
Imam Askari ne ya tona asirinsa ga mabiyansa. Wata rana suna zaune cikin kurkukun, sai Imam Askari (AS) ya yi ishara gare shi, ko zai ]an fita daga waje. Bayan fitar sa shi ne Imam Askari (AS) ya ce wa mabiyan nasa; “Wannan mutumin ba a cikinku yake ba, saboda haka ku yi hankali da shi. Domin duk abubuwan da kuke fa]i yana nan rubuce a takarda, takardar na nan cikin kayansa”.
Nan take cikin mabiyan Imam wani ya tashi ya duba kayansa, sai suka ga takarda }unshe da zantukansu. Wannan ma wata karama ce ta Imam Askari (AS). Shi wannan mutumin ba wai kawai ya nuna shi ]an fursuna ba ne, a’a, ma ya nuna shi mabiyin Ahlul Baiti (AS) ne, shi ya sa Imam Askari (AS) ya ce su yi hankali da shi, ba a cikinsu yake ba.
Mu duba irin wannan sa ido, har a kurkuku ba a }yale shi ba. Saboda da ma gayar sa ido da ake yi masa, akwai lokacin da Imam Askari (AS) ya bu}ata daga mabiyansa, idan suka gan shi ko suka ha]u da shi, kada su yi masa sallama, ko su nuna shi domin amintuwa ga kawukansu, kamar yadda Imam Askari (AS) ya ce. Daga nan mutum zai fahimci irin gayar ’yan le}en asiri da aka turo wa Imam Askari (AS), wa]anda suke lura da kai-komon sa, da kuma mu’amalarsa da mutane. Domin mujararradin ala}a da Imam Askari (AS) a lokacin in an ga mutum yana iya fuskantar hukuncin kisa ko zuwa kurkuku. Akwai ma lokacin da Imam Askari (AS) yake fa]a wa wani daga cikin mabiyansa ko dai ya ~oye ala}arsa da shi, ko kuma ya fuskanci kisa.
A ta}aice dai Imam Askari (AS) ya fuskanci sa ido daga masu tafi da iko fiye da sauran A’imma (AS) da suka gabace shi.
Wata jarabawa kuma da Imam Askari (AS) ya fuskanta wanda sauran A’imma (AS) ba su fuskance ta ba ita ce, na sa ido da kuma bincike ga iyalansa lokaci bayan lokaci, domin a gane wacce ce take da ciki? Saboda masaniyar da su wa]annan azzalumai masu tafi da a iko suke da ita na cewa shi ne Imam na 11, kuma shi ne zai haifi Imam na 12, wanda zai kau da zalunci da kuma azzalumai a doron }asa. A kan wannan asasi suka samo mata }wararru na sanin cikin ’ya mace wa]anda suke da ciki, da nufin su sa ido ga iyalinsa. Amma ta Allah (T) ba tasu ba. A irin wannan yanayi aka haifi Imam Mahdi (AS).
Bayan haihuwar sa ma, al’amarin haka ya ~oye gare su har ya shekara biyar a duniya gabanin wafaatin Imam Askari (AS). Wannan jarabawa ce ga Imam Askari (AS), domin da aka yi haihuwar wa]anda suka sani kawai sune wasu da suke kusa da shi sosai a cikin mabiyansa. Domin ko abin a}i}ar[dabbar da ake yankawa ta suna]  Imam Askari (AS) ya bayar a sayo a wani waje ne,wato aka yanka acan. bayan wafatinsa ma akwai wata daga cikin kuyangun sa da aka tsare kusan shekara biyu bisa tsammanin tana da ciki, sai daga baya suka sake ta.
A ta}aice Imam Askari (AS) ya fuskanci wannan jarabawa ta sa ido, fiye da kowane Imami, shi ya sa galibi ala}arsa da mabiyansa ta rubutu ne. Su rubuto, ya rubuta masu. A nan za mu kammala wannan rubutu da wata wasiyya da ya rubuta wa Shi’arsa a loakcin. Ga Wasiyyar:- “Ina maku wasiyya da jin tsoron Allah (T) da kuma tsantseni cikin addininku da kuma yin mujahada saboda neman yardar Allah (T) da gaskiya wajen magana da ba da amana ga wanda ya ba ku amana daga mutum kirki da wa]anda ba mutumin kirki ba. Da kuma tsawaita sujuda, da kyakkyawan ma}wabtaka, da wannan Manzon Allah (S) ya zo. (Sannan Imam Askari (AS) ya fa]i abubuwa hu]u domin kyautata ala}a ga wa]anda ba mabiya Ahlul-Baiti (AS) ba)”.
A ci gaban wannan wasiyyar sune; “Ku yi Salla a masallatansu, ku halarci jana’izarsu, ku je gaida mara lafiyarsu, ku ba da ha}}o}insu, domin ]ayan ku idan ya yi tsantseni a addininsa, ya zama mai gaskiya a maganarsa, mai kuma ri}on amana, ya kuma kyautata ]abi’unsa da mutane za a ce wannan ]an Shi’a ne. Wannan ko sai ya faranta min rai”.
Ya ci gaba da cewa; “Ku ji tsoron Allah ku kasance masu }awatawa, kada ku kasance masu munanawa. Ku jayo mana dukkan so. Ku tunku]e mana dukkan }i (wato mutum ya lizimci aikata abin da ya san zai jayo so ga Ahlul Baiti (AS) domin abin da aka fa]i kyakkyawa dangane da mu, to mu ma’abotansa ne. Abun da kuma aka fa]i mummuna dangane da mu, to mu ba haka muke ba. Ku yawaita ambaton Allah (T) da kuma tunanin mutuwa da karatun Al}ur’ani da kuma salati ga Manzon Allah (S). Ku kiyaye wannan wasiyya da na yi maku. Amincin Allah ya tabbata gare ku”.
Wannan ita ce wasiyyar da Imam Askari (AS) ya aiko wa mabiyansa. Kuma wannan wasiyya tasa ba ta ta}aita ga Shi’ar zamaninsa ba, a’a, har da wa]anda suka zo daga baya. Saboda haka sai mutum ya dubi wannan wasiyya kamar madubi, ya dubi kansa da ita. Abubuwan da aka ambata duka ya dabba}a su, in haka ne sai ya gode wa Allah (T) da kuma da]e tsayuwa a kan su, in ko ba haka ba ne. To sai ya yi }o}arin wajen ganin cewa ya ]abba}a su.
Bayan haka kuma akwai wata wasiyyarsa da ya rubuta wa ]aya daga cikin manya-manyan mabiyansa, wato Ibn Babawaihi Al}ummi, wanda yake shi Mahaifi ne ga Shaikh Sadu}. Ga wasiyyar; “Inai maka wasiyya da tsoron Allah da tsaida Salla da ba da Zakka, domin ba a }ar~ar Sallar wanda bai ba da Zakkah.
“Ina maka wasiyya ga yin afuwa ga laifin da aka yi maku, da ha]iye fushi da sadar da zumunci da taimaka wa ’yan uwa, da kuma sa’ayi ga bu}atocinsu a cikin tsanani da kuma sau}i da kuma ha}uri ga mai wauta, da kuma neman ilimin addini, da kuma tabbata a kan al’amarin, da kuma yawaita karatun Al}ur’ani, da kyakkyawar ]abi’a, da umurni da ma’arufi, da kuma hani ga mun}ar, da nisantar alfasha dukkan ta. Na hore ka da Sallar dare. Domin Manzon Allah (S) ya yi wasiyya ga Imam Ali (AS) ya ce masa; ‘Ya Ali! Na hore ka da Sallar dare, na hore ka da Sallar dare, na hore ka da Sallar dare, duk wanda ya wula}anta Sallar dare, to ba ya daga cikinmu’. Ka yi aiki da wannan wasiyya tawa. Kuma ka umurci duk mabiyana da su yi aiki da ita. Kuma na hore ka da dauriya da kuma jiran faraj[wato jiran Imam Mahdi]. Domin Manzon Allah (S) ya ce mafificin aikin al’ummata shi ne jiran faraj, kuma Shi’armu ba za su gushe ba cikin damuwa da ba}in ciki ba har sai ]ana ya bayyana, wanda Manzon Allah (S) ya ba da albishir da zuwan sa, cewa zai cika }asa da adalci bayan ta cika da zalunci da kuma danniya. Saboda haka ka daure ka umurci Shi’ata, su daure, }asa ta Allah ce yana gadar da ita ga bayin sa. A}iba kuma tana ga masu ta}awa. Amincin Allah ya tabbata gare ka da kuma dukkan Shi’armu”. Wannan ita ce }arshen wasiyyar. Allah (T) ya ba mu ikon aikatawa.
In Allah ya kai mu wata munasaba ta wafatinsa za a ]ora a kai, insha Allah.

No comments:

Post a Comment