Sunday 3 February 2013

Darussa 12 daga rayuwar Imam Aliy Alhadi (AS)


Kasantuwar 3 ga watan Rajab ne wafatin Imam Aliy Alhadi (AS), kamar yadda aka saba a irin wa]annan munasabobi na wafati da kuma shahadar Ma’asumai (AS), akan gabatar da Darussa a ta}aice daidai gwargwado, na tarihinsu da kuma wasu ~angarori na rayuwarsu daban-daban, da nufin su kasance madubi da za mu dubi kawukanmu da kuma rayuwarmu da su, da kuma yin mujahada daidai ikonmu.
Domin mu ga cewa mun aikata abubuwan da muka karanta, domin aikata abin da mutum ya sani, yana bu]e wa mutum }ofar ilimin da bai sani ba.
            Kamar yadda ya zo a Hadisi cewa, “duk wanda ya aikata abin da ya sani, Allah (T) zai gadar masa ilimin da bai sani.” Wannan tabbas haka ne. Mutum ya jarraba haka a rayuwarsa, ya gani. Misali duk lokacin da mutum ya ji ko ya karanta wani Hadisi ko kuma ruwaya ta Manzon Allah (S) da kuma Ahlul-Bait (AS) ya kuma aikata daidai ikonsa, sai mutum ya ga ba da jimawa ba Allah (T) ya sake ni’imta shi da sanin wa]ansu domin ya aikata. Haka nan abin yake a ayoyi na Al}ur’anin da muke karantawa. In har mutum na karanta Al}ur’ani mai girma tare da aikatawa daidai gwargwadon ikonsa, to, zai ga Allah bisa falalarsa yana sanar da shi wasu daga cikin asrar na ayoyin da yake karantawa, watau ba]ini na ayoyin. Kamar dai fa]in Allah (T) da ya ce, “ku yi ta}awa ga Allah, Allah ya sanar da ku.” Kamar yadda aka sani ]aya daga cikin fassarori na ta}awa shi ne misaltuwa da umurnin Allah (T) da kuma hanuwa da haninsa. Kuma rashin aikata abin da mutum ya sani zai kasance ne musiba ga mutum gobe }iyama, kamar yadda haka ya zo a Hadis. Domin zai kasance ke nan hujja a kan mutum. Kuma shi aikata Addini ko kuma aikata abin da mutum ya sani zai yi shi ne da ‘Ikhlasi’. Wato saboda Allah(T) da kuma neman yardarsa, ba domin a yaba masa ko samun matsayi ko kuma wani abu na duniya ba. Domin kamar yadda rashin aikata abin da mutum ya sani zai kasance musiba ga mutum gobe }iyama, to, haka ma idan ya sani kuma ya aikata, amma ba tare da ‘Ikhlasi’ ba, shi ma zai kasance musiba ga mutum gobe }iyama. 
           Ya zo a wani Hadis, mai ban tsaro da kuma ta da hankali cewa za a zo da wasu mutane gobe }iyama wa]anda suka rayu a fagage daban-daban na ba da gudummuwa ga Addini, amma daga }arshe Allah (T) zai ce a kai su wuta, saboda rashin ‘Ikhlas’ a cikin ayyukansu. Wannan ko ba }aramar hasara ba ce. A ce aiki ba mummuna ba watau na sa~o, kyakkyawa na ]a’a, amma sakamakon rashin ‘Ikhlasi’ a ciki, ya yi sanadiyyar zuwan mutum wuta. Shi ya sa in mutum ya duba kuma ya bibiya zai ga cewa Malam, watau Sayyid Zakzaky (H) a mu’utamarori daban-daban da aka gabatar, ake kuma gabatarwa, lokaci bayan lokaci a garuruwa daban-daban, yana yawan magana da kuma }arfafawa a kan ilimi, aiki da ikhlasi. Zai yi wahala ka ga a kullewar Mu’utamar, Sayyid Zakzaky bai yi magana a kansu ba, ko wani daga ciki, watau saboda gayar muhimmancinsu.
            Baya ga wa]annan matakai uku watau Ilimi, aiki da ikhlasi, sai kuma’ Khauf’, watau mutum ya zauna cikin tsoro tsakanin sa da Allah (T), ya dinga yawan tunanin cewa shi }ashin kansa da kuma ’yan ayyukan da yake aikatawa kar~a~~u ne a wajen Allah (T) ko ba kar~a~~u ba ne? Yaya a}ibarsa ko }arshensa zai kasance a Addinance a wannan gida na duniya? Kuma ya al’amarinsa zai kasance gobe }iyama? Ana son mutum ya zauna cikin tsoron wa]annan abubuwa da aka ambata da ma wa]anda ba a ambata ba; musamman ma tunanin tsoron a}iba. Domin da za a tambaya a ce, me ya fi komai muhimmanci a rayuwar ]an Adam? Amsa ita ce yadda }arshensa ya kasance a Addinance a zamansa a wannan gida na duniya. Domin a kan abin da mutum ya mutu a kai, a kansa za a tashe shi.  
         Maganin mummunar a}iba a Addini, kamar yadda Malaman ‘Irfani’ suka yi bayani yana samuwa ta hanyoyi uku: 1. Yawaita Addu’ar neman kyakkyawar A}iba daga wajen Allah (T) 2. Nisantar Zunubi, watau mutum ya yi iyakar iyawarsa wajen ganin cewa ya nisanci zunubi, watau Sa~o. Domin yadda ya zo a Hadisi cewa, duk lokacin da mutum ya yi zunubi, idan bai tuba ba, akan sa ba}in ]igo a zuciyarsa, in ya sake, a sake sa ba}i. Kama-kama in ya ci gaba a haka, har zuciyar ta zama ba}i-}irin. Domin shi zunubi illolinsa da kuma gubarsa suna da yawan gaske. Misali yana iya dabaibaye mutum daga ayyukan ]a’a. Watau ya kasance mutum ya saba yin wasu ayyuka na ibada, amma sakamakon wani zunubi da ya yi, ya samu kansa bai iya aikata komai, ko kuma ya shamakance mutum daga addu’o’insa da dai makamantansu na illolin zunubi. Shi ya sa in mutum ya duba zai ga bayin Allah (T) da ya za~a, su kasance Hujjoji ga bayinsa, dukkansu suna da wannan siffa ta ‘isma,’ wadda ]aya daga cikin ma’anoninta shi ne rashin aikata sa~o.
          3. Hanya ta uku ta maganin mummunar A}iba ita ce kyautata wa Allah (T) zato. Kamar yadda ya zo a Hadisi cewa, Allah (T) yana nan inda bawansa yake zaton sa, watau mutum ya dinga tunanin cewa, insha Allah, Allah (T) zai yi masa kyakkyawan }arshe a Addini, ba mummunan }arshe ba. Khulasar da aka ambata shi ne Ilimi, aiki ‘ikhlas da ‘khauf’,  watau tsoro na ababen da aka ambata. Kuma wa]annan abubuwan guda hu]u da aka ambata, ba za su samu ba, sai tare da yin mujahada da ‘Nafs’ ]insa (ransa) da kuma Shai]ani da kuma duniya da kuma mutane. Haka mutum zai ta fama da wa]annan ~angarori na mujahada matu}ar yana raye, hutunsa sai ran da ajalinsa ya sauka. Kamar yadda ya zo a Hadis cewa, mutuwa hutu ce ga mumini, watau daga irin wannan dama da kuma mujahada da ransa da shai]ani da dai sauransu.
            Dawowa ga wannan munasaba ta Imam Ali Alhadi (AS), Imam Aliy Alhadi kamar yadda aka sani shi ne, Imam na goma a jerin }idaya na Imamai 12. An haife shi a wani gari kusa da Madina, ana ce masa Sarya, a ran 15 ga watan Zul Hijja, shekara ta 212 bayan Hijira. Mahaifinsa kamar yadda aka sani shi ne Imam Jawad (AS). Sunan Mahaifiyarsa Sumanatu, amma an fi sanin ta da Sayyida, kuma ana yi mata kinaya da Ummi Fadhal. Kamar yadda ya zo a tarihi, ta kasance  mai yawan ibada, musamman ma ta ~angaren Azumi. Kuma ta kasance mai ta}awa da kuma zuhud, watau gudun duniya. Imam Aliy Alhadi (AS) ya kasance yana da la}ubba da yawa, amma wa]annan biyun su suka fi fice, Alhadi da kuma Anna}iy. Imam Aliy Alhadi (AS) ana yi masa kinaya da Abul Hasanis-Salis,Abul Hasanis- Sani, shi ne Imam Ridha( AS), domin a wasu littafan tarihi ko Hadisi, kinayar kawai sukan fa]i na wa]annan Imamai, ko kuwa wani lokaci a littafai mutum ya ci karo da wannan kinayar Abu Jafarul Awwal. Ana nufin Imam Ba}ir (AS) ko kuma Abu Jafarus-Sani, ana nufin Imam Jawwad (AS).
            Imam Aliy Alhadi ya rayu tare da Mahaifinsa Imam Jawwad (AS) shekaru 8, bayan wafatinsa, Imamanci ya dawo gare shi. Muddar Imamancinsa shekara 33, a wata ruwaya kuma 34. Imam Alhadi (AS) ya kasance yana da yara 5 - maza 4, mace 1. Sune: Imam Hasan Al’askari (AS), Husain, Muhammad, Jafar da kuma Aliyya. Imam Aliy Alhadi (AS) ya zauana a Madina, kusan Shekaru 22 yana Madina. Khalifan Abbasawa mai suna Mutawakkil, ya sa a zo a ]auke shi daga Madina zuwa Ira}i. Ya aiko runduna na maya}a zuwa Madina domin su tafi da Imam Hadi (AS) a cikin dare. Da suka shiga gidan, sai suka same shi zaune yana karatun Al}ur’ani mai girma, suka bincike gidan baki ]ayansa. Bayan haka suka kama hanya da shi zuwa Ira}.
            A wannan tafiya Imam Aliy Alhadi (AS) da zai fita, ya fita tare da ]ansa Imam Hasan Al’askari (AS), lokacin yana shekara hu]u da watanni. Da suka isa Ira} an kai Imam Hadi (AS) wajen Mutawakkil, a inda abubuwa marasa da]in ji da kuma karantawa suka gudana, wa]anda shi Mutawakkil ya yi ga Imam Hadi (AS). Da yake lokacin da suka isa wajen Mutawakkil ]in yana shan giya ne, watau a buge yake. Ga mai bu}atar sanin abubuwan da suka gudana, yana iya duba littafi mai suna A’immatuna Juzu’i na biyu. Haka Imam Aliy Alhadi (AS) ya zauna a Ira}i, a garin Samarra, a wata unguwa da ake kira da Askar tare da ]ansa, Imam Hasan Askari (AS). Shi ya sa daga cikin la}ubban Imam Hadi (AS) akwai Askari, saboda haka a nan ya }are sauran rayuwarsa, watau a Ira}. Ya zauna a cikinta shekaru 20. Imam Aliy Alhadi (AS) ya rayu a duniya shekaru 42. {abarinsa yanzu haka yana Samarra ne tare da }abarin ]ansa Imam Askari (AS).
            Imam Hadi (AS) ya rasu ranar Litinin 3 ga watan Rajab shekara ta 254 bayan hijira. Ya rasu ne sakamakon guba, wadda Khalifan Abbasawa mai suna Mu’utazaz ya sa masa. Imam Aliy Hadi (AS) ya yi zamani da Khalifofin Abbasawa guda shida. Su ne Mu’utassim, Wasik, Mutawakkil, Muntasir, Musta’in, Mu’utazaz. To, a cikin wa]annan guda shidan, wanda ya fi gallazawa da cutarwa ga Imam Hadi (AS) shi ne Mutawakkil (LA). Kuma cikin su shida ]in shi ya fi su tsawon shekaru a mulki, don shekararsa 14 a karagar mulki. Kuma a cikin wa]annan shekaru ya yi munanan abubuwa masu yawan gaske. Ga goma daga ciki:
            1. [auko Imam Hadi (AS) da kuma raba shi da Madina, birnin Manzon Allah (S). 2. Sa Imam Hadi (AS) da kuma mabiya ]aruruwan Ahlul-Bait (AS) a kurkuku, wanda sai bayan mutuwarsa aka saki mafi yawan su. 3. Ya sha yun}urin kashe Imam Hadi (AS) Allah (T) ya tsare. 4. Nuna }iyayya da gaba ga Imam Aliy (AS) da kuma Sayyida Fa]ima (AS). Ya zo a tarihinsa cewa saboda gayar }iyayya da gaba har zagin su yana yi. Zagin nasa ma bai ta}aita ga Imam Aliy (AS) ba, a’a har ga Sayyida Fatima (AS), wa’iyazubillah. Wannan mummunan aiki nasa na zagin wa]annan bayin Allah (T) shi ya zama sanadiyyar ajalinsa.
            Abin da ya faru shi ne, wata rana ]ansa mai suna Muntasir ya ji shi yana zagin Sayyida Fatima (AS). Abin ya ~ata masa rai matu}a, shi ne ya je ya samu wani Malami ya tambaye shi, ga munanan abin da mahaifinsa yake yi, zai iya kashe  shi? Sai Malamin ya ce masa eh. Shi ne  ya shirya, shi da wasu abokansa suka samu la’ananne a cikin gida, inda yake shaye-shayensa na giya, suka auka masa, suka kashe shi. Shi wannan ]an nasa shi ya zama Khalifan Abbasawa a bayansa.
            5. Ya sa aka rushe }abarin Imam Husain (AS) da kuma gidajen da ke kewaye. Duk wannan bai ishi Mutawakkil ba, ya sa a yi gona a wajen, wai saboda }abarin da alamominsa su ~uya ga mabiyaAhlul bait. To, ta Allah ba ta shi ba, }abarin bai ~oyu ba. 6. Kafin ba da wannan umurni nasa na a rusa }abarin Imam Husain (AS), sai da ya sa a rin}a kamawa da kuma azabtar da masu ziyarar Imam Husain (AS). Akwai ma lokacin da ya ba da umurnin cewa duk wanda aka kama yana ziyartar Imam Husain (AS) a yanke masa hannu tun daga kafa]a har ya zuwa yatsun hannu. A ta}aice dai hannun baki ]aya. In ya sake kawo ziyarar, ]aya hannun ma ai masa haka. In ya sake a zo ga }afa, ita ma baki ]aya. To, akwai wani da aka yi masa haka, saboda ziyarar Imam Husaini (AS) aka yanke masa hannaye biyu. Ya zamanto yana zuwa ziyarar a kan dabba. Aka yanke masa }afa. Ya zamanto saura }afa ]aya. Da ya sake zuwa aka ]auke shi aka kai shi har wajen Mutawakkil, shi ne yake tambayar sa, kai me ya kai ka kake wannan abu haka? Ya ba da amsa da cewa, saboda so da kuma shau}insa ga Imam Husain (AS). Ya ce kuma ko da za a yayyanka naman jikinsa, matu}ar zai iya zuwa ziyarar, sai ya je.
            7. Shi ya sa aka cire dabinnai wa]anda Manzon Allah (S) ya shuka a Fadak da hannayensa masu albarka, watau Fadak da Manzon Allah ya bai wa Sayyida Fatima (AS). Shi wanda aka sa ya yi wannan aika-aikar ta cire dabinan, daga baya jikinsa ya shanye. 8. Kamawa da kuma }wace dukiyar duk wanda ya taimaka wa Sadat, watau jikokin Manzon Allah (S). Wannan abu da ban mamaki, idan mutum ya duba littafi mai suna TATIMMATUL-MUNTAHA FI TARIKHIL KHULAFAI na Shaikh Abbas {ummy, watau marubucin Littafin Mafatihul Jinan, zai ga ya kawo abubuwa daban-daban na matsalolin da aka jefa Sadat a ciki. Ba don komai ba, saboda }iyayyarsa ga Imam Aliy (AS) da kuma Sayyida Fatima (AS).     
            [aya daga cikin matsalolin da aka jefa su da gangan ita ce ta talauci. Ya zo a kan cewa saboda rashi, ta kai ga wasu daga cikin Sadat mata, ba su da tufafin da zai rufe jiki baki ]aya a lokacin Sallah sai guda ]aya, saboda haka yadda suke yi shi ne in ]aya ta yi Sallah, in ta gama sai ta ba ]ayar. Haka Sadat suka kasance a cikin wannan yanayi har sai bayan da ya mutu, ]ansa Muntasir, ya kyautata ma Sadat. Ya kuma saki ]aruruwan mabiyan Ahlul-Bait (AS) da aka ]aure a kurkuku. 9. Daga munanan ayyukan da Mutawakkil ya sa aka yi shi ne, kashe Malamin ’ya’yansa, kisa mummuna, watau na Musla. Abin da ya faru shi ne. Wata rana Mutawakkil ya tambayi wannan Malami ’ya’yana wane da wane watau Mu’utazaz da kuma Mu’ayyid su suka fi maka ko ko Hasan da Husain? Sai Malamin ya ba da amsa da cewa, “Mai yi wa Imam Aliy (AS) hidima (watau Bawan sa) ya fi ka, ya fi ’ya’yanka”. Shi ne Mutawakkil ya fusata ya sa a yanke harshensa, a farka masa ciki; haka dai daga }arshe aka yi masa gunduwa-gunduwa. Mu duba irin wannan bushewar zuciya tasa.
            10. Daga cikin munanan ayyukan Mutawakkil akwai azabtar da mutanae da wuta, watau ya sa a }ona wasu ~angarori na jikin mutum ko kuma ya sa a jefa shi a wuta baki ]aya. A ta}aice dai rayuwar Mutawakkil baki ]ayanta rayuwa ce ta fasadi da zalunci da kuma fasi}anci, shi ya sa da wa]annan munanan ayyukan nasa suka tsananta, Imam Aliy Alhadi ya yi addu’a,akan sa. Mutawakkil ko bai kwana uku ba ya mutu. Aka huta da shi. Allahu Akbar. Saboda munanan ayyuka na Mutawakkil, shi ya sa wasu Malaman Tarihi suke kwatanta shi da Yazid (LA), a cikin Khalifofin Banu Umayya.     
            Watau shi Mutawakkil shi ne Yazid ]in Khalifofin Abbasawa. Al’amarinsa in mutum ya bincika tarihi zai ga sun yi kama da na Yazid ta fuskoki daban-daban. Alal misali, kamar yadda ]an Yazid mai suna Mu’awiyyah bai bi halinsa ba, haka shi ma ]an Mutawakkil mai suna Muntasir bai bi halinsa ba. Domin bayansa, shi ya kyautata wa AhlulBait (AS) da kuma mabiyansu. Duk Sadat da babansa ya jefa cikin talauci, haka ya dinga bi yana aika masu da ku]a]e da kuma kayayyaki. Wannan ke nan dai a ta}aice, sai kuma wasu ~angarori na rayuwar Imam Hadi (AS)
1. ILIMIN SA: Imam Aliy Alhadi (AS) a wannan fagen babu wanda ya kai shi a zamaninsa ballantana ma ya wuce shi. Hatta ma}iyansa sun tabbatar da haka. Ga wata }issa da ta faru lokacin yana shekara takwas a duniya mai ban mamaki da kuma ban dariya ga wa]anda suka shirya al’amarin. Abin da ya faru shi ne, Khalifan Abbasawa, wanda ake ce wa Mu’utassim, wanda ya yi sanadiyyar rasuwar Mahaifinsa, watau Imam Jawad (AS) bayan wafatin Imam Jawad (AS), sai shi wannan Khalifa Mu’uttasim ya yi tunanin cewa ]ansa Imam Hadi (AS) tun da shi ne Imam na  gaba, bayan Imam Jawad (AS) kuma shi a lokacin shekarunsa takwas, to, bari ya samo wani Malami wanda ya san yana gaba da kuma }iyayya ga Ahlul-Bait (AS), domin wai ya karantar da Imam Hadi (AS), kuma wai ya cusa masa }iyyayya da Ahlul-Bait (AS) (abin dariya). Ilai ko, sai sai ya aika Madina ga Gwamnansa, ga abin da yake bu}ata. Sai aka ce ai ga Malam wane, kowa ya san gabarsa da kuma }iyayyarsa ga Ahlul Bait (AS). Sai aka ha]a shi da Imam Alhadi (AS), wai ya dinga karantar da shi. Sai wannan Malami ya soma karantarwar, amma sai ya ga abubuwan da suka ba shi mamaki. Sai ya ga duk fannin da yake so ya karantar da Imam Hadi (AS), sai ya ga ya fi shi fahimtar fannin.
            Wata rana wani wanda yake da masaniyar wannan shirin, da suka ha]u, sai yana tambayar Malamin, ya yaron da kake karantarwa? Sai Malamin ya ce kai wannan ba yaro ba ne dattijo ne. Duk abubuwan da nake karantar da shi ya fi ni sanin su. Ya ba shi misali da karatun Al}ur’ani cewa wani lokaci sai ya ce ba zai tashi ba sai ya karanta sura kaza, sai ya fa]i surar da bai kai ba, amma sai ya ji ya karanta. Sai ya fahimci cewa Al}ur’anin baki ]aya ya haddace shi. Bayan kwana biyu da Malamin ya sake ha]uwa da mutumin yake tambayar sa, ya ya ga wanda yake karantarwa? Sai Malamin ya ce wa mutumin, “Wallahi a bayan }asa babu wanda ya kai shi ilimi da kuma daraja.” Ikon Allah sai wannan Malami wa]annan karamomin da kuma ayoyi da ya gani ga Imam Hadi (AS) ya zama sanadiyyar wanke }iyayya da gaba da ke zuciyarsa ta Ahlul Bait (AS) zuwa ga soyayya da kuma }auna ga Ahlul Bait (AS). A ta}aice dai tun daga lokacin ya zama ]an Shi’a, watau mabiyin Ahlul Bait (AS). Mu duba mu gani daga }arshe shi aka gyara. Allahumma salli ala Muhammad wa Aaliy Muhammad.
2. JARABAWOWIN SA: Imam Hadi (AS) ya fuskanci jarabawowi masu yawa a rayuwarsa, musamman ma ga masu tafiyar da iko. Ga misalan wasu daga ciki: Zama a kurkuku, yana ]aya daga cikin Imaman da suka yi zaman kurkuku, da kai hari a gidansa da sunan bincike, wai yana tara makamai. An kai masa irin wannan harin lokacin yana Madina da kuma Ira}i; kuma haka ya auku ba ]aya ba, ba biyu ba. Kuma duk lokacin da suka kai irin wannan harin sukan same shi yana ibada ne. Akwai lokacin da suka je suka same shi yana sallah. A wani harin kuma suka samu yana karatun {ur’ani a zaune a }asa mubasharatan, watau ba wai yana kan tabarma ba ko buzu, wannan abu ya ba su mamaki, watau su jami’an tsaro ]in da aka aiko. Wannan ke nan baki ]aya a ta}aice. Sai In Allah ya kai mu shekara mai zuwa a munasabar wafatinsa insha Allah za a ]ora.


No comments:

Post a Comment