Sunday 3 February 2013

Hanyoyin samun kyawawan ]abi’u da kuma tsarkaka daga munanan ]abi’u.


Kamar yadda ya gabata a darasi na Akhla}  na  biyu, da yake an samu lokaci mai tsawo ba’a gabatar da wannan darasi na Akhla}  ba,dalili ko shine,kamar yadda aka ce a baya,lokaci  bayan  lokaci za’a ri}a samun yankewar darasin,
saboda rubutu na wafati ko shahadar Aimma na Ahlul Bayt [AS] wanda akan kawo da unwanin  Darussa 12.Alal misali,watan muharram da safar daya gabata,akwai shahadar Imam Husain[AS],wafatin Imam zainul Abidin [AS],wafatin Imam Hasan [AS],da kuma wafatin Manzon Allah [S],a ta}aice dai rubutu kan wa]annan ~angarori daya gabata, shine  dalilin da yasa aka samu kusufi na wani lokaci ba’a gabatar da wannan darasi na Akhla} ba.                                                                                         Idan ba’a manta ba,a darasin daya gabata an tsaya ne akan wasu tambayoyi guda uku sune,1.yaya za’ayi mutum yasan aibobin Nafs ]insa? Wato ya san ko yana da munanan Akhla}  ko bai dasu.2.wa]anne hanyoyi ne mutum zai bi domin ya ku~uta? Wato ya tsarkaka daga munanan Akhla}. 3.yaya za’ayi mutum ya samu ko ya siffanta da kyawawan Akhla}?                                                                          A darasin daya gabata,an bada amsar tambaya ta farko,bayan haka aka ce insha Allah a darasi na gaba za’a kawo amsoshin sauran wa]ancan  tambayoyi  guda biyu.                                                                                             Dangane da tambaya ta biyu na wa]anne hanyoyi mutum zai bi domin ya tsarkaka daga munanan Akhla},idan mutum ya bibiyi littafan Akha}, kamar  littafin Akhla}u  Ahlul Bayt [AS],ko kuma littafi mai suna, Ilajul –Amradu- Akhla-}iyyah;zai ga an kawo hanyoyi da matakai da mutum zai bi domin tsarkakuwa ko wankuwa daga munanan Akhla}.Anan za’a kawo guda uku daga ciki saboda gudun tsawaitawa.                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                   1.Sanin illolin munanan ]abi’u,domin su munanan ]abi’u  sukan nisanta mutum daga Allah [T],sukan nisanta mutum daga mutane,sukan kuma nisanta mutum daga Aljannah.Ga kuma illoli da suke yiwa mutum,a addininsa da duniyarsa da kuma lahirarsa.Domin ita mummunar ]abi’a,ba wai ga mutum ]an uwanka ba,a’a ko dabba mutum ya munana wa,zata iya kasancewa sanadiyyar shiga wuta ga mutum,alal misali,}issar wata mata mai mage da ta ]aure ta,ba ta bata abinci,bata kuma bari taje ta nema ba,wanda hakan yayi sanadiyyar zuwanta wuta,insha Allah idan an yi nisa a cikin wannan darasi na Akhla},za’a kawo illolin da munanan ]abi’u  suke yi a addinin mutum da duniyarsa da kuma lahirarsa,sanka- sanka.                                                                                                                                                                                          2.Mujahada:Daga cikin hanyoyin da mutum zai bi domin tsarkaka daga munanan ]abi’u  shine mujahada,wato mutum ya ya}i Nafs ]insa [ransa] da kuma shai]an,domin yaga ya tsarkaka daga wata mummunar ]abi’a da yake tare da ita.Misali,mummunar ]abi’a ta riya,ko ujub,ko hassada, ko rowa,da dai makamantansu.To,anan mutum zaiyi mujahada wajen ganin cewa ya tsarkaka daga riya,ko ujub,ko hassada,ko kuma rowa.Shima  wannan insha Allah nan gaba za’ayi bayanin yadda mutum zai yi wannan mujahada,domin tsarkakuwa daga wadannan cututtuka na zuciya da aka ambata,dama wa]anda ba’a ambata ba.                                                                                                                                                                                                   3.Mura}aba:Daga cikin hanyoyin da mutum zai bi domin tsarkaka daga munanan ]abi’oi,akwai hanyar mura}aba,wato shine mutum ya  zamo yana  shu’urin [jin]cewa Allah [T] yana ganinsa,yana jinsa,ya san tunanin zuciyarsa,yana kuma tare da shi,idan mutum ya kasance ko da wane lokaci,tunaninsa ya ginu akan wannan shu’urin na mura}aba,to ha}i}a ya samu hanya babba ta tsarkakuwa daga munanan  ]abi’u, kuma wadda tafi tasiri fiye da biyun da aka ambata.Shima wannan,wato yadda mutum zai gina shu’urin mura}aba  a zuciyarsa,bayaninsa  zai zo nan gaba.Wannan ke nan a ta}aice dangane da amsar  tambaya ta biyu.                                                                                                                          Sai kuma amsar tambaya ta uku.Ta yaya za’ayi mutum ya siffantu,ko ya samu kyawawan ]abi’u? shima wannan malamam Akhla}  sunyi  bayani na hanyoyi da matakai da mutum zai bi,daga cikin hanyoyin:
1.Sanin fa’idodi da kuma sakamako na kyawawan ]abi’u,domin sanin zai taimaka wa mutum wajen ganin cewa ya siffanta da kyawawan ]abi’u. saboda kyawawan ]abi’u  sukan  kusanta mutum ga Allah [T],sukan kusanta shi da mutane,sukan kuma kusanta shi ga Aljannah.Banda kuma fa’idodi masu yawan gaske da mutum zai samu a addininsa da duniyarsa da kuma lahiyarsa sakamakon siffantuwa da kyawawan ]abi’u.Domin kyakkyawar ]abi’a,ba wai ga mutum ]an uwanka ba,ko dabba mutum ya kyautata wa,haka na iya zama sanadiyyar shigarsa Aljannah.Misali  anan }issar wani mutumi da yaji }ishi yaje ya samu wata rijiya ya sha ruwa,bayan ya sha ya juya zai tafi sai ga wani kare,yazo bakin rijiyar yana jin }ishi,ganin haka sai mutumin ya ]ebo ruwan a rijiya ya ba karen,to sai Allah[T] yayi wahayi ga Annabin zamanin,da ya shaida ma mutumin,Allah zai shigar dashi aljanna sakamakon wannan aiki nasa.Mu duba mu gani yadda kyautatawa ga dabba zai iya sanadiyyar shigar mutum aljanna ko kuma munana mata,yana iya sanadiyyar shigar mutum wuta.To ina ga kyautata ma mutum ]an’uwanka ko munana masa.Hanyoyi da mutum zai bi a addini wajen siffanta da kyawawan ]abi’u shine,ta hanyar mujahada,wato mutum yayi fa]a da Nafs ]insa wajen ganin cewa ya siffanta da kyakkyawar siffa,kuma wannan mujahada mutum zai yi tane ta fuskoki guda ukku:Na farko,mutum yayi mujahada wajen ‘Iktisabin’ wato samun kyawawan ]abi’a.Na biyu,mujahada wajen Ba}a’a’ wato wanzuwa da  kuma  isti}ama akan kyawawan ]abi’a.Na uku,mujahada wajen ‘Numuw’ wato cigaba wajen da]a kyautatuwa ga wa]annan kyawawan ]abi’u daya samu.                                                                                                Domin su kyawawan ]abi’u,kamar yadda malaman Akhla} sukayi bayani,ana samun su ko mallakar sune ta hanyoyi guda biyu: Hanya ta farko itace,ta ‘JuduL-lLahiy’ wato baiwa daga ubangiji,wani zaka ga tun tashinsa yana yaro, yana da ha}uri da kyauta,ko dai wasu kyawawan siffofi,wato yana da su ba tare da yayi wata mujahada ba wajen samun su,To,wannan shine abinda malaman Akhla}, suke cewa ]abi’oi  na ‘Judul-ILahiy’,Hanya  ta biyu ta mallakar kyawawan ]abi’u, itace ta hanyar ‘Iktisabi’,wato mutum shi zai yi mujahada wajen samun su kyawawan ]abi’un.Misali  yayi mujahada idan shi bai da ha}uri,ya zama mai ha}uri,idan shi mai yawan fushi ne,ya zama mai ha]iye fushi,idan shi marowaci ne,ya zama mai kyauta,da dai sauran kyawawan ]abi’oi, da ba’a ambata ba.Shima wannan nan gaba insha Allah in an zo kan bayani dangane da kyawawan ]abi’u, za’a yi bayani a warware, na irin mujahadar da kowanne  yake bu}ata,domin siffanta da siffar kamar yadda malaman Akhla}  suka  bayyana.              
3.Mushahada da kuma Mura}aba:Daga cikin hanyoyin da mutum zai bi domin samun kyawawan ]abi’u shine,hanyar mushahada da kuma mura}aba na Allah [T].Mushahada shine,mutum ya zaman to koda wane lokacin yana shu’urin [jin] Allah [T],kamar  yana  ganin Allah [T],domin in shi bai ganinsa to Allah [T] yana  ganinsa,wanda  wannan shu’rin na cewa Allah [T] yana ganinsa shine mura}aba,kamar yadda aka yi ]an  bayani a baya.Domin idan mutum ya kasance koda wane lokaci yana cikin wannan shu’irin na mushahada da kuma mura}aba,to zai zamo hanya babba a gare shi da zai taimaka masa wajen siffanta da kyawawan siffofi.Misali,tun da yasan Allah [T] yana jinsa,to duk abinda zai fa]i zai ga cewa ya fa]i gaskiya kuma tun da ya san Allah [T] yana ganinsa,to zai ga cewa ya kasance mai ri}on amana,kuma tun da ya san cewa Allah [T] yasan abinda ke cikin zuciyarsa,to zai ga cewa ya kyautata tunaninsa,ba zai yi tunanin da bai dace ba.Kuma irin wannan shu’uri na mura}aba da kuma mushahada,idan mutum ya same shi,zai taimaka masa wajen ganin cewa, ko da wane lokaci, yayi iya iyawarsa wajen ganin yayi wa Allah [T] ]a’a,da kuma  kasancewa bai sa~a masa ba. Ta }issar wani malamin irfani dana  karanta, shi da Almajiransa. Wata rana sai shi malamin ya ba almajiransa  wani  aiki, amma ya ce yana son kowa yayi in da ba a ganin sa. Dukkan su  sai suka tafi, kowa yaje in da mutane ba su ganinsa ya aiwatar da aikin, sai guda ]aya daga cikin almjiran ne bai aiwatar ba. Sai  malamin ya tambaye shi, kai ya aka yi kowa ya aiwatar  kai  baka  aiwatar  ba? Shine ya bada  amsa  cewa, ai duk  in da ya je, Allah (T) yana ganinsa, shi yasa bai yi ba. Shine  malamin  yace masa  dama na yi maku jarabawa ne, in ga wanda ya kai ma}am (matsayi) na mura}aba da kuma mushahada na Allah (T).
4. Samun so da kuma kusanci zuwa ga Manzon Allah (S), kamar yadda ya zo a hadisi, Manzon Allah (S) ya ce; “Wanda na fi so daga cikin ku, wanda ya fi kusa dani gobe }iyama, shine wanda ya fiku kyawawan ]abi’u”. ginuwa  akan wannan tunani na samun son Manzon Allah (S) da kuma kusanci gare shi, yana daga cikin hanyoyin da za su taimakawa mutum wajen samun kyawawan ]abi’u. Saboda haka, ma’auni na yadda mutum yake a wajen Manzon Allah (S) shine kyawawan ]abi’u, dai dai kyawawan ]abi’un mutum, dai dai son Manzon Allah (S) gare shi da kuma kusanci da shi gobe  }iyama. Kuma kyawawan ]abi’u, koda ba domin fa’idodinsu da kuma amfanoninsu masu yawan gaske ga mutum ba, a addininsa da kuma lahiransa,to ko da a duniyan ce,ya kamata mutum ya siffata dasu. kamar yadda ya zo daga Imam Ali (AS) ya ce; “ko da bamu }aunar aljannah, ba mu kuma tsoron wuta, ba mu fatan samun lada  da kuma gudn u}uba, duk da haka ya kamace mu, mu siffantu da kyawawan akhla}.”
5. Daga cikin hanyoyin da za su taimaka wa mutum wajen samun kyawawan ]abi’u, shine sanin cewa, jarabawa daga wajen mutane wani abune  wanda  ba  makawa  ga mutum  matu}ar yana raye.Shi yasa Yazo a hadisi cewa: Mutuwa hutu ne ga mumini. Saboda haka, samun jarabawa daga wajen mutane ta fuskoki daban-daban sunna ce  ilahiyya wadda ba makawa, hadisai masu yawa sun yi nuni ga haka, ga wasu daga ciki, akwai lokacin da Imam Zainul abidin (AS) yake cewa wani daga cikin mabiyansa: mutane in ka barsu ba za su barka ba, In ka watsar da su ba za su watsar da kai ba, sai yace wa Imam zainul abidin (AS); ‘to ya zan yi?’ sai ya amsa da cewa: “ka basu daga mutuncin ka,  saboda gobe  }iyama”. Wato mutum yayi ha}uri daga cutarwar mutane, saboda  sakamakon da zai samu gobe }iyama.
An  samo daga Imam sadi} (AS) ya ce; “Bai kasance  a da ba, bai kasance a yanzu ba, kuma ba zai kasance nan gaba, har zuwa tashin }iyama, Annabi ne ko mumini, face sai an samu wani yana cutar da shi. A wani hadisi makamancin wannan da aka samo daga Manzon Allah (S) ya ce; “Bai kasance a da ba, ko a yanzu, ko nan gaba, har zuwa tashin }iyama, ga Annabi ko mumini, face an samu wani ]an uwan sa na jini da ya ke cutar da shi”.
An samo daga Imam Ali (AS) ya ce; Manzon Allah (S) ya ce; “Da a ce mumini zai shiga wani rami (wato saboda  gujewa  cutarwar  mutane) da Allah (T) ya salla]o masa wanda zai cutar da shi”.
A wata ruwayar da aka samo daga Imam sadi} (AS) ya ce; “Da mumini zai je ya hau tsororuwar dutse ya zauna (wato  saboda  gujewa matsalar mutane) da Allah (T) ya salla]o masa wanda zai cutar da shi”.
A kuma wani hadisi da aka samo daga Imam Ba}ir (AS) ya ce; “Fari ya samu mutanan Annabi Hudu (AS), sai suka tafi wajen sa domin yayi addu’ar Allah (T) ya saukar da ruwa. Suka je gidansa ba su same shi ba, sai matarsa da ta fito, sai ta yi masu fa]a da hayaniya. Su ka ce, ‘to yana ina?’ ta ce, ya tafi  gona. Sai suka samu Annabi Hudu (AS) a gona. Da suka isa sai suka ga duk idan ya yi kunya guda ]aya na shuka sai ya yi nafila raka’a biyu. Ya dube su ya ce, ‘me nene bu}atar ku?’ su ka ce; ‘munzo wajen ka ne domin wata bu}ata’, sai mu kaga abin da ya bamu mamaki’ sai ya tambaye su, me ya baku mamaki? Suka ce; ‘Mun ga wata mata ta fito daga gidan ka, tana mana fa]a da haniya’. Sai Annabi hud (AS) ya ce masu; ‘Ai matata ce, kuma duk da wa]annan ]abi’u nata, ina son ci gaba da zama da ita?’ Sai ya ce masu, babu wani mumini face an samu wani da yake cutar da shi. Ni ina  godiya ga Allah(T) da ya sanya mai cutar da ni, yana }ar}ashin iko na ne, ba domin  haka ba  da Allah (T)ya salla]o min da wanda ya fita cutarwa”.
 Akwai hadisai masu yawa ire-iren wa]annan masu nuni da cewa cutarwar mutane  ga mutum, wani abune  wanda  yake  ba  makawa. Amma  saboda gudun tsawaitawa, ba za a iya ci gaba da kawosu ba. Sai dai mai bu}atar }arin ganin wa]annan hadisai, yana iya duba littafi mai suna ‘mishkatil anwar fi guraril  akhbar ‘, na Abul-Fadhal  at-tabrisiy. Shi ]a ne ga wanda yayi littafin ‘Makarimul  akhla}’ wato ta~-rasiy.
Tun da cutarwar mutane ga mutum, wani abu ne lazim, matu}ar ya na raye, ashe ke nan siffantuwa da kyawawan ]abi’u, irin su ha}uri, kau da kai, ha]iye fushi, afuwa, kyawtatawa akan munanawa, da dai sauran kyawawan ]abi’o’I, wani abu ne wanda yake da muhimmancin gaske, musamman ga wanda yake ma’abocin addini, domin babbar hanya ce ta da’awa. Kuma wa]annan kyawawan ]abi’u, mutum zai yi su ne saboda Allah (T) da kuma neman yardarsa, ba domin mutane su yarda da mutum ba, ko su yaba maka.Domin mutane suna iya yaba maka yau, gobe su soke ka. To, a nan mutum zai fahimci hikma da asrar na ikhlasi ga dukkan ayyuka.
Misali, kana kyautata wa mutum saboda Allah (T), sai wata matsala ta shiga tsakaninka da shi. To, idan mu’amalar ka da shi, akan asasin ikhlasi ne, to baza ka damu ba wajen ci gaba da kyautata masa, sa~anin ko idan mu’amalar ba akan ikhlasi ba ne, da an samu sa~ani shi ke nan,  sai kyautatawar ta yanke. Ya ma zo a hadisi cewa, mutum ya sadar ga wanda ya yanke masa. Ya bai wa wanda ya hana masa. Ya yi afuwa ga wanda ya zalunce shi, kuma ma in mutum ya dubi wasu kyawawan ]abi’u  da  Manzon Allah (S) ya samu mutanen jahiliyya a kai, kamar fa]ar gaskiya, ri}on amana, cika al}awari, sadar da zumunci, da dai sauransu, musulunci ya tabbatar da wa]annan ]abi’un, abin da ya }ara a ciki shine ikhlasi. Wato wannan fa]in gaskiyar, da ri}on amana, da cika al}awari, da sadar da zumunci, da dai sauransu, to mutum yayi su saboda Allah (T), ba domin kada a soke shi a ce ma}aryaci, mai cin amana, mai sa~a alkawari, ko bai da zumunci ba.
Kuma in mutm ya dubi Ayoyin da suka sauka a makkah, baya ga maganar a}ida da suke yi, wato tauhid, nubuwwah da kuma ma’ad, da kuma }issoshi na annabawa, zai ga suna magana kan akhla}  ne, wanda kuma  an  ga tasirin  akhla}  ]in,a lokacin da Manzon Allah (S) ya koma Madinah, a al’amarin ha]a ‘yan –uwan-taka  tsakanin  muhajirin da kuma  ansar. Kuma }arfin juriyar mutum a bisa cutarwar mutane gare shi, yana nuna  ikon sa, akan  nafs ]in sa da kuma shai]an. Saboda haka, mujahada  wajen samun sul ]a (iko) a kan nafs da kuma shai]an, wani abu ne wanda ya ke da gayar muhimmanci, kuma mafi }arancin kyautatawa da mutum zai yi ga mutane ‘yan uwansa, musamman ma ‘yan uwansa muminai, shine ya zamanto bai cutar da su ba da zuciyarsa ko harshensa ko hannunsa. In kuma su suka cutar da shi, ya daure, ta wata mahangar, ni’ima ce gareshi saboda gobe }iyama, Allah (T) zai ba shi sakamako akan wannan cutarwa da aka yi masa da kuma juriyar da yayi akai. Domin sakamakon da Allah (T) zai ba bayinsa gobe  }iyama, sun kasu kashi uku:
1.       Sakamako da  zai bayar na taklif  da ya aza wa bayinsa, wato umurce-umurce da kuma hane-hane, wato sakamako akan yadda kowa ya tsayu da wannan taklif.
2.       Sakamako akan jarabobin da ya jarabta bayinsa da su,wannan jarabawa tana da fuskoki daban-daban; ]aya daga ciki shine: jarabawa na tsakanin mutum da mutane ‘yan uwansa.
3.       Sakamako na judiL-lLahi[wato bai wa daga wajen Allah] wanda irin wannan sakamako ba kowa ke samun sa ba, wasu daga cikin bayin Allah (T) ne yakan za~a, yayi masu sakamako na musamman daga wajensa, saboda yadda suka tsayu da kuma  kai wa  gaya wajen tsayuwa da taklif, da kuma cin jarabobin da suka yi, wanda Allah (T) yayi masu a wannan gida na duniya. Saboda haka cutarwar mutane a zahirance mutum zai ga matsala ne, amma a ba]inance alheri ne.
Wannan ke nan dai a ta}aice dangane da hanyoyin da mutum zai bi domin ya tsarkaka daga munanan ]abi’u,  da  kuma hanyoyin da zai bi domin siffanta da kyawawan siffofi.

No comments:

Post a Comment