Ranar arba’in ]in
Imam Husain [AS] rana ce wadda take da muhimmanci,musamman ma ga mabiya Ahlul bayt [AS],kuma kiyaye ranar
yana daga cikin alamomin mumini,kamar yadda haka yazo daga Imam Hassan Al-askari
[AS],in da yace, “Alamomin mumini [wato ]an shi’a] guda
biyar ne.
1.Yin salla raka’a 51 ko wace rana. 2.Ziyarar arba’in.3.Sa zobe a dama. 4.Sa goshi a }asa [ta’afir]. 5.Bayyana karatun bismillah
a sallah.” Amma
kafin bayani dangane da wannan hadisi da kuma
ranar arba’in ]in,zai yi kyau a ]an yi bayani a ta}aice dangane da matsayin adadin arba’in a addinin musulunci.Adadin arba’in yana da
wani asrar gaibiyya a wajen Allah [T] da kuma tarkizi na musamman a wasu ayoyi
na Al-}ur’ani
mai girma,da kuma wasu hadisai da aka samo daga Manzon Allah [S] da kuma Ahlul bayt
[AS],ga misalin wasu daga cikin wa]annan hadisai,an samo daga Imam Sadi} [AS] yace, “Idan mumini ya rasu,mutane 40
daga muminai suka halarci jana’izarsa,[cikin addu’ar da sukayi masa] suka ce
‘ya ubangiji! Bamu san komi dangane dashi ba sai alheri,kai ka fimu saninsa, Allah [T] zai ce na zartar da
shaidarku,na gafarta masa na abin da na sani da abunda ku baku sani
ba.”. Haka
nan kuma daga Imam Sadi} [AS] yace, “Babu wasu jama’a 40 da zasu ha]u suyi addu’a
a kan wata bu}ata tasu face Allah [T] ya kar~a musu”.har ila yau daga Imam Sadik [AS]
yace, “Duk wanda ya gabatar da muminai 40 gabanin addu’arsa,bayan haka ya
gabatar da addu’a ta bu}atarsa,to Allah[T] zai kar~a masa”kuma wannan wani abu ne wanda yake
da gayar muhimmanci da falala,na kowannenmu ya sabawa kansa da yin haka,wato na addu’oi ga muminai guda 40,in son sa mune a kowane dare a }unut na witri,ko kuma bayan ya gama sallar
tahajjud ]insa,in
ba zai iyayi ko wane dare ba to a}alla duk daren juma’a mutum ya lizimci hakan,domin yin hakan ya na da
fa’idodi masu yawan gaske,kuma sunna ce daga cikin sunnonin ma’asumai [AS],alal
misali yazo akan cewa sayyida fatima [AS] in ta gama sallar tahajjud ]inta, takan yi addu’oi ga muminai na kusa da na nesa,shine har Imam
Hasan [AS] yake ce mata “Na kan ji ki kan yi addu’oi ga mutane,amma ban ji kina addu’a gare
kiba”.shine tace masa, “ma}wabci gabanin gida”. Haka
nan kuma akwai hadisi da aka samo daga Manzon Allah [S] yace, “Duk wanda ya kiyaye
wa al’ummata hadisai 40 da suka shafi al’amarin addininsu,baya nufin komai face yardar Allah [T] da kuma gidan lahira,to Allah
zai tashe shi ranar }iyama a matsayin fa}ihi kuma Malami” wannan hadisin yasa da yawa daga cikin malaman madrasah ]in Ahlul bayt [AS] da kuma ta Ahlus sunna, suka rubuta littafai na hadisai 40 domin samun falalar wannan hadisi,misali anan shine littafin hadisi 40 na Imam khumaini da kuma
littafin hadisi 40 na Imam Nawawi,in mutum ya duba littafin hadisi 40 na Imam
khumaini, zai ga cewa a wajen gabatarwa na littafin yana cewa ya tattara wannan
hadisai ne da fatan ya samu shiga cikin hadisin Manzon Allah [S] da yazo akan cewa “wanda ya kiyaye wa al’ummata
hadisai 40 da suke amfana dasu,to Allah
zai ta da shi ranar al }iyama a
matsayin fa}ihi
kuma Malami”.da dai hadisai da dama da suka zo akan
Tarkizi kan 40,wanda ba za a iya kawo su ba saboda gudun tsawaitawa.Dawowa ga wannan hadisi da aka samo daga Imam Askari [AS] na alamomin mumini guda
biyar,alama ta farko,kamar yadda yazo a hadisin,shine yin Raka’a 51 ko wace rana,wannan raka’a 51 ya
ha]a
da sallolin wajibi da nafilfilinsu da kuma sallar tahajjud tare da shafa’i da witri,a warware ga lissafin adadin raka’oin na sallolin
wajibi,wato daga sallar Asuba zuwa sallar Isha’i, in mutum ya ha]a zai ga 17 ne,sai nafilfilinsu,sune raka’a 2 gabanin
Asuba,raka’a 8 gabanin sallar zuhur,raka’a 8 gabanin sallar
Asar,raka’a 4 bayan sallar maghrib,raka’a 2 a zaune bayan isha’i [watira].amma
biyun nan yana matsayin raka’a ]aya ne,sallar tahajjud raka’a 8,shafa’i 2
witri 1,in mutum ya ha]a zai ga
lissafin ya tashi 34,wato na raka’oi na nafilfilin,in mutum ya hada da wa]ancan raka’oi na wajibi 17, zai ga ya tashi
akan 51,To,wa]annan
raka’oi 51 sune ake so kowane mumini,wato mabiyin Ahlul bayt [AS]
ya tsayu da yinsu kowace rana ba tare da yin fashi ba.ko da zata kai ace mutum bai
samu yin su nafilfilin ba, saboda wani uzuri,to yazo akan cewa ana son mutum ya
rama su.misali ace bai samu yin nafilfilin zuhur da asar ba,ya na iya ramka su acikin
yini ]in,ko
kuma da daddare.in kuma bai samu yin nafilfilin dare ba, wato kamar maghrib ko
isha’i,ko kuma sallar tahajjud ]insa,to ya na iya ramka su a daren,ko kuma
washe gari cikin yini.wato ya tsayu akan yin haka kowa ce rana ba tare da fashi
ba.A in da kawai wa]annan nafilfilin suka fa]i shine a halin tafiya,a nan nafilfilin zuhr da
asar sun fa]i,amma sauran nafilfilin na sallar maghrib
da isha’I da asuba,da kuma tahajjud,shafa’i da witri,su basu fa]i ba.Wato dai a halin tafiya nafilflin
sallolin rana ne suka fa]i,amma nafilflin dare basu fa]i ba. kuma wa]annan raka’oi 51 mutum ya kwatanta su da raka’a dubu ]aya da Imam Aliy [AS],Imam Husain [AS],Imam
zainul Abidin [AS] da kuma Imam Ridah [AS] suke yi ko wace rana ,zai ga ]aya bisa 20 ne.kuma su wa]annan raka’oi 51,su ake cewa salloli na yaumiyyah.Akwai kuma salloli na usbu-iyyah,wato na mako,suma an ruwaito
sune daga Manzon Allah [S] da kuma Aimma na Ahlul bayt [AS],wato wa]annan kwanaki bakwai na mako,misali daga juma’a
zuwa Asabar to kowace rana da kuma dare na wa]annan kwanaki na da nata sallolin,littafai da
dama sun kawo wa]annan
sallolin,misali littafin Diya’us
Salihin.ga wanda bai da wannan littafin ko Daren juma’a raka’a 2,ko wace raka’a mutum zai karanta }ul-huwallahu 70.wannan an samo daga Manzon
Allah ne.sai kuma ranar juma’a raka’a 8,ko wace raka’a }ul-huwallahu 1.Daren Asabar raka’a
4,kowace raka’a bayan fatiha,sai kul-huwallahu
7,sai kuma ranar asabar raka’a 4,kowace raka’a bayan fatiha,}ul-ya Ayyuhal- kafirun sau 3 bayan sallama
ta raka’a 4,sai mutum ya karanta Ayyatul -kursiyu sau ]aya,sai daren lahadi raka’a 6,ko wace raka’a bayan fatiha,}ul-huwallahu sau 7,sai ranar lahadi raka’a
2,raka’a ta farko bayan fatiha,Inna -A’a]aina sau 3,raka’a ta biyu bayan fatiha }ul-huwallahu sau 3,sai daren litinin
raka’a 2,kowace raka’a bayan fatiha,Ayatul kursiyu,}ulhuwallahu,sai suratul fala}i da nasi,dukkansu sau ]aya,bayan sallama sai istigfari sau 10.sai ranan litinin raka’a
4,raka’a ta farko bayan fatiha Ayatul kursiyu ]aya,raka’a ta biyu bayan fatiha,}ul-huwallahu ]aya,raka’a ta uku bayan fatiha,suratul fala}i,raka’a ta hu]u bayan fatiha suratu Nasi,Daren talata
raka’a 2,raka’a ta farko bayan fatiha,inna- Anzal-nahu sau 1,raka’a ta biyu
bayan fatiha }uhuwallahu
7.Ranar talata raka’a 2,kowace raka’a bayan fatiha,wattini,}ul-huwallahu,fala}i da nasi,dukkansu sau ]aya.Daren laraba raka’a 2,bayan
fatiha,kowace raka’a Ayatul kursiyu,inna Anzal nahu,iza-ja’a sau ]ai-]ai,sai kuma }ulhuwallahu sau 3,Ranar laraba raka’a
2,kowace raka’a bayan fatiha,iza-zul sau 1,sai kuma }ulhuwallahu sau 3.Daren Alhamis raka’a
6,kowace raka’a bayan fatiha }ul-ya Ayyuhal kafirun sau ]aya,sai }ulhuwallahu sau 3,bayan sallamewa duka,wato raka’a 6 ]in,sai mutum ya karanta Ayyatul kursiyu
sau 3,sai ranar alhamis raka’a 2,bayan fatiha kowace raka’a iza-ja’a da kuma
inna -A’a]aina
ko wace sau 5. To,irin wa]annan salloli su ake cewa sallolin
usbu’iyyah,wato na mako.in mutum ya duba cikin littafin jamalul-usbu’i,na
sayyid Ibn [awus
da kuma littafin mir’atul kamal,zai ga duk sun kawo su.Su ma wannan ya na da
kyau kowannen mu ya tsayu dasu,wato baya ga wancan raka’a 51 na yaumiyyah. Sai kuma sallah ta shahariyya,wato ta
wata;ita kuma yadda take shine;idan ka yi ta a daren farko na ko wane wata,sai
kuma wani sabon wata a daren farko,haka nan in ka yi a ranar farko na wata,sai kuma wani
wata a ranar farko.shine ake ce mata
shahariyya.mutum na iya duba sallolin a littafin Mafatihul Jinan babi na 2
fasali na 11.Ga wanda bai da imkaniyyar dubawa ga yadda sallolin suke.Daren
farko na kowane wata raka’a 2,kowace raka’a bayan fatiha,sai ya karanta suratul
An’am,idan mutum bai haddace ba yana iya amfani da Al’}ur’ani domin karanta suratul An’am ]in.sai kuma ranar farko ta ko wane
wata,shima raka’a 2,raka’ar farko bayan fatiha,}ul-huwallahu 30,sai raka’a ta biyu bayan
fatiha,Inna -Anzal nahu 30.Suma wa]annan sallolin an samo ne daga A’imma na Ahlul bayt
[AS],suma wa]annan
salloli na wata-wata ana son mutum ya tsayu dasu,wato ko wane wata daren
farkonsa da kuma ranar farkonsa ya zamo mutum na yi ba tare da fashi ba,sai in
da wani uzuri. Sai kuma
salloli na sanawiyya,wato shekara- shekara,su kuma yadda suke,in ka yi su
misali yau,to sai kuma wata shekara zaka sake yinsu.Irin wa]annan salloli sun zo ne jefi-jefi a cikin
kwanuka na shekara,wato ba kullum ake
yinsu ba.misalin irin wa]annan salloli
na sanawiyya sune kamar sallar ranar }arshe ta shekara,ko kuma sallar daren Ashura,to
ire-iren wa]annan
salloli sune ake cewa salloli na shekara.misali sallolin da suka zo na daren
Ashura,yanzu mutum ba zai sake yinsu ba,sai kuma shekara mai zuwa in Allah [T]
ya kai mu wani daren Ashurar na shekara mai zuwa.Yanzu sallah ta sanawiyya dake
gabanmu itace ta 17 ga watan Rabi’ul Awwal,wato ranar maulidin Manzon Allah
[S],in mutum ya duba mafatihul jinan zai ga sallah ]in,kuma wa]annan watanni 12 na musulunci,in mutum ya bisu ]aya bayan ]aya zai ga ba wani wata wanda babu sallar
sanawiyya a cikinsa.Shima wannan wato
sallah na shekara-shekara ya na da kyau
kowannen mu ya tsayu dasu. Saboda
haka in muka duba a wannan nizami,wato
tsari zamu ga akwai salloli na yaumiyya,Usbu’iyya,shahariyya,da kuma
sanawiyya,kuma duk wa]annan salloli an ruwaito sune daga Ma’asumai
[AS].Saboda haka ya na da muhimmanci yin wa]annan salloli domin koyi dasu,kuma kamar yadda
muka ga wannan nizami guda hu]u na salloli,to haka nan ma addu’oi na da nizami
wato tsari na yaumiyya,usbu’iyya,shahariyya,da kuma sanawiyya. Haka nan ma shi
Azumi yana da wannan nizamin guda hu]u,haka nan surori na Al}ur’ani suma suna da wannan nizami guda hu]u,wato akwai surorin da ake son karantawa
yaumiyya,akwai usbu’iyya,shahariyya da kuma surori na sanawiyya.insha Allah
dukkansu za’a yi bayanin su a muhallinsu. Wannan
shine bayani a ta}aice
dangane da
alamar mumini na farko.Sai kuma alama ta biyu kamar yadda yazo a hadisin,wato
ziyarar Arba’in ]in
Imam Husain [AS] a 20 ga watan safar,wato kwanaki 40 bayan shahadarsa [AS],ya na
daga cikin alamomin mumini wato mabiyin Ahlul Bayt [AS].Kuma ita wannan ziyarar,
imma ta kasance daga kusa ne ko daga nesa,wato in mutum ya na da iko da kuma
damar zuwa karbala domin ziyara ko kuma yin ziyarar daga garin da yake.A kan wannan
asasin ne zamu ga mabiya Ahlulbaiti [AS] daga sassan duniya daban
-daban da suke da ikon zuwa karbala,musamman ma wa]anda suke cikin kasar ira}i,suke tururuwa zuwa karbala domin wannan
ziyarar ta Arba’in,wanda mutum zai iya dukan }irji a wannan zamanin namu, yace babu wani
taro da yake tara mutane a doron }asa kamar wannan ziyarar ta Arba’in a karbala. Ta
yi wu mutum yayi tunanin taron aikin hajji.To,duk shekara taron bai kai
wa miliyan biyar,galibi miliyan biyu ne zuwa uku.To,amma mu duba taron jama’a
na ziyarar arba’in ]in Imam Husain [AS] a karbala na shekarun bayan nan da suka wuce, akan samu jama’a sama da
miliyan 15,kuma ko wace shekara
adadin }aruwa ya ke yi,wannan aya ce
babba ga masu tunani.Kuma wani abin lura
shine wasu dake cikin }asar Ira}i sukan tako ne da }afa daga garuruwansu,har ya zuwa karbala
domin wannan ziyarar.Za ka gansu maza da mata yara da manya da ma dattijai.kuma
a irin wa]annan
hanyoyi na zuwa karbala zaka ga
akwai bayin Allah [T] daban daban da suke gabatar da hidima ta fuskoki daban
daban ga wa]annan
matafiyan zuwa karbala,kuma dukkan wa]annan hidimomin kyauta suke gabatar dasu.Akwai
masu bada abinci a hanyoyin,akwai masu bada masaukai,misali mutum ya yo tafiyan
kwanaki daga garinsu,ya na son ya huta
kafin ya cigaba da tafiya,to, ga masauki fisabilillah.Akwai likitoci,ga masu
gyaran takalmi,ga masu hanyoyi na sadarwa,wato tarho shima duk kyauta
ga wa]annan
matafiya zuwa karbala, da dai abubuwa da yawa daba a ambata ba na hidimomi, da
wasu bayin Allah ke gabatarwa fisabilillah. Ita ziyarar Imam Husain [AS] ta kasu kashi
biyu,akwai ziyara mu] la}a,wato itace ziyara wadda bata ke ~anta da wani zamani ayyananne ba.Akwai kuma ziyara
mak susa,wato ta ke ~anta da wani zamani ayyananne .To,ziyarar Arba’in
ta na daga cikin ziyara mak susa.A wata ma’ana ziyara mak susa, ana ce mata ziyara sanawiyya,wato ta shekara-shekara.Domin idan
kayi ta sai kuma wata shekara.Misali wannan ziyara ta Arba’in.Ziyarar Imam
Husain [AS] mak susa,kuma sanawiyya guda 10 ne sune:
1.Ziyarar
Ashura,wato 10 ga muharram. 2.Ziyarar Arba’in,wato 20 ga
watan safar. 3.Ziyarar
ranar farko, ta watan Rajab. 4.Ziyarar
15 ga watan Rajab. 5.Ziyarar
3 ga watan sha’aban,wato ranar haihuwar Imam Husain [AS]. 6.Ziyarar
daren 15 ga watan sha’aban. 7.Ziyarar
daren lailatul }adr 19,21,23 na
watan ramadan. 8.Ziyarar
daren idi }arama da kuma daren idi babba. 9.Ziyarar rana
kun idi }arama da babba. 10.Ziyarar ranar Arfa,wato 9 ga
zul hijja.To dukkan wa]annan kwanaki da
aka ambata, mustabbine ya ziyarci Imam Husaini [AS]a cikin su daga kusa ko
nesa. Ba yaga wannan ziyara ta shekara ta Imam
Hussain[as]Akwai kuma ziyar usbu’iyya
wato mako mako.Itace duk ranar litinin.Ga mai bu}atar
ganin wannan ziyara dama sauran ziyarori na Manzon Allah[s]da kuma Ahlul
bait[as]na mako,ya duba cikin littafin mafatihu, babi na ]aya
fasali na biyar.Baya ga wa]annan ziyarori
mustahabbi ne yin ziyara a rana kun wilada da kuma wafati na Ma’asumai
[AS],wato Manzon Allah [S] da kuma Ahlul bayt [AS],musamman ma rana kun wafatinsu,wato ya na da kyau mutum
ya sunnanta ma kansa wannan sunna ]in,ya kasance duk
ranar wilada ko wafati na ]aya daga cikin
ma’asumai, mutum ya kasance ya ziyarce shi ziyara ta kusa ko ta nesa.Domin yin
haka yana ]aya daga cikin hanyoyin kyautata ala}a
da Manzon Allah [S] da kuma Ahlul bayt
[AS] da kuma dan faruwa dasu }al-
biyyan,wato a zuci.A ta}aice dai kiyaye wa]annan
rana ku na wilada da wafati na ma’asumai [AS] a matsayi na ]ai-]ai
ku da kuma jama’a,yana da gayar muhimmanci.Ga wata da kuma ranar wafatin ko wanne
daga cikin ma’asumai [AS]:1.Manzon Allah [S] 28 ga watan safar. 2.Sayyida fatima [AS] 3 ga
watan jimada-sani. 3.Imam
Aliy [AS] 21 ga watan ramadan. 4.Imam
Hasan [AS] 7 ko 28[a wata ruwayar] ga watan safar. 5.Imam
Husain [AS] 10 ga watan muharram. 6.Imam
zainul Abidin [AS] 25 [a wata ruwaya] 12 ga watan muharram. 7.Imam
Ba}ir
[AS] 7 ga watan zulhijjah. 8.Imam Sadi}
[AS] 25 ga watan shawwal. 9.Imam
Kazim [AS] 25 ga watan Rajab. 10.Imam
Ridha [AS] 23 ga watan zul}idah [a wata
ruwaya] a watan safar. 11.Imam
Jawad [AS] }arshen watan zul}idah. 12.Imam
Hadi [AS] 3 ga watan Rajab. 13.Imam Askari
[AS] 8 ga watan Rabi’ul Awwal. Wa]annan
sune rana ku na wafatin su,wato rasuwarsu. Sai
kuma na wiladar su,wato haihuwar su kamar haka: 1.Manzon
Allah [S] 17 ga Rabi’ul Awwal. 2.Sayyida
fatima [AS] 20 ga watan jimada sani. 3.Imam
Aliy [AS] 13 ga watan Rajab. 4.Imam
Hasan [AS] 15 ga watan Ramadan. 5.Imam Husain [AS] 3 ga watan
sha’aban. 6.Imam
Zainul Abidin [AS] 5 ga watan sha’aban. 7.Imam
Ba}ir
[AS] 1 ga watan Rajab [a wata ruwaya 3 ga watan safar]. 8.Imam
Sadi}
[AS] 17 ga watan Rabi’ul Awwal. 9.Imam
Kazim [AS] 7 ga watan safar. 10.Imam
Ridha [AS] 11 ga watan zul}idah. 11.Imam Jawad [AS] 10 ga watan
Rajab. 12.Imam
Hadi [AS] 2 ga watan Rajab. 13.Imam
Askari [AS] 10 ga watan Rabi’us sani. 14.Imam
Mahdi [AS] 15 ga watan sha’aban. Haka
nan baya ga ziyara a wa]annan kwanaki na wafati ko wilada na ko wannensu,akwai
yin juyayi, in na wafati ne,da kuma yin murna, in na wilada ne,da kuma mi}a
ta’aziyya ga Manzon Allah [S] da kuma Ahlulbayt [AS]in na wafati ne,in kuma na
wiladar ma’asumai ne,sai ya mi}a
murnarsa ga Manzon Allah [S] da kuma
Ahlul bayt [AS] duk sai bayan mutum yayi musu sallama. Insha Allah
sauran alamomin mu’umini sai wata munasabar za’a ]ora.
No comments:
Post a Comment