Saturday 9 February 2013

Gudummawar mata a wa}i’ar Karbala.


Kasantuwar wannan wata da muke ciki wato Muharram,wata ne na zaman makoki wanda akan tunatar da juna dangane wannan wa}i’a ta karbala,misali abubuwan da suka auku gabanin Ashura da abubuwan da suka auku ranar Ashura,da kuma abubuwan da suka biyo bayan Ashura da kuma darussan da zamu koya daga wannan wa}i’ar ta Ashura dadai sauran ~angarori dake da ala}a da wannan al’amarin na Ashura,
wanda akan tunatar da juna a kai,baya ga wannan akwai wani janibi mai muhimmancin gaske dake da ala}a da wannan wa}i’ar ta Ashura.Wannan janibi kuwa shine GUDUMMAWAR MATA A WA{I’AR ASHURA.Idan mutum ya bibiyi tarihin wannan wa}i’ar ta Ashura,tun daga farkon  ta har }arshen ta zai ga cewa mata sun bada gudummawa mai yawan gaske a ciki.Kuma wannan gudummawa tasu ta wanzu har ya zuwa wannan zamanin namu kuma zata ci gaba da wanzuwa.Alal misali,zaman makoki wanda ya zama wata zaunanniyar sunna tun bayan shahadar su Imam Husain [AS] wa]anda suka soma yin wannan zaman makoki sune matan da sukayi musharaka cikin wannan wa}i’ar ta Ashura,wato su sayyida Zainab [AS] sun soma yin haka a sham da kuma bayan isarsu madina kamar yadda zamu ga haka a nan gaba Insha Allah.
Haka nan sa ba}a}en kaya a irin wannan zama na makoki su suka soma yi.Wannan ya auku a madina har ma yazo akan cewa idan suna zaman makoki Imam Zainul Abidin yakan sa a yi abinci a kai masu,kuma daga nan malaman Imamiyyah suka tafi akan sunnah ]in sa ba}a}en kaya a lokacin makoki,domin kamar yadda aka sani sunnah itace fa]in ma’asum ko aikinsa ko kuma tabbatarwarsa,wato Imam Zainul Abidin [AS] ya gansu a wannan shiga ta ba}a}en kaya baki ]ayan su,wato abinda ake so a fitar a nan shine;wannan sunna ta shiga babin tabbatarwa.            Haka nan baya ga wannan daga cikin gidunmawar da mata suka bayar,shine Tablig ]in ita wa}i’ar.wato isar da ita ga wa]anda basu kasance a wajen ba.Domin baki ]aya duk bayanan da akeyi dangane da wannan wa}i’a  ta karbala ko rubuce-rubuce da akeyi akai,to asalin shi daga wa]annan bayin Allah mata aka jishi,domin a wa}i’ai kamar yadda aka sani duk wani namiji an kashe  shi,sai Imam Zainul Abidin ko shima dun yana kwance bai da lafiya.Wannan yana ]aya daga cikin asrar da kuma hikima ilahiyya da yasa Imam Husain[AS] ya tafi da mata da kuma yara  zuwa karbala,saboda bayan wa}i’ar ,su isar da ita ga mutanen zamaninsu da kuma wa]anda zasu zo daga baya, na abubuwan da idonsu ya gani,kuma kunnuwansu suka ji,da kuma abubuwan da suka fuskanta bayan shahadarsu, a nan karbala ,kufa da kuma sham.kuma  akan wannan asasi na tablig ]in wannan wa}i’a ta karbala,wanda Sayyida Zainab[AS] ta dun ga yi bayan komawarta madina,yasa Gwamnan madina na lokacin ya aikawa Yazidu cewa,in yana bu}atar madina to ya kori Zainab daga cikinta.wato saboda bayanan da take yin a wa}i’ar karbala yana tasiri a zukatan mutane,wanda wannan tasiri ya kai ga hatta magoya bayan Bani umayya,suka canza tunani,suka yi masu tawaye. A ta}aice dai Yazidu ya aika da umarni cewa a kore ta daga cikin madina.shi yasa in muka duba zamu ga }abarinta ba a madina ba yake.                                  Daga cikin gudummawar da mata suka bayar a wannan wa}i’a ta karbala.Akwai kula da kuma bada magani ga wa]anda suka samu raunuka,wanda  zainab [AS] ta bada gudummawa babba a wannan fage.A kan asasin haka ne ma a jamhuriyar musulunci ta Iran aka baiwa ranar da aka haifi zainab [AS] sunan ‘Ranar masu kula da majinyata’,don tunawa da girmama irin gudummawar data bayar wajen jinyar wa]anda suka samu raunuka a karbala.Daga cikin gudummawar da mata suka bayar a cikin wannan waki’ar ta karbala itace }arfafa mazajensu da kuma ‘ya’yansu wajen taimaka wa Imam Husain [AS].Ga misali matar Zuhair kamar yadda yazo a tarihi zuhair a farkon al’amarin yaso ya kasance basu ha]u da Imam Husain [AS] ba,sai Imam Husain ya aika yana kiransa, Lokacin da wannan sa}o yazo ga zuhair sai yayi ]an nauyin jiki ga amsa wannan kiran,sai matarsa ta }arfafa shi akan ya tafi ya amsa kiran Imam Husain [AS] yaji menene,bayan ya tafi ya dawo,ikon Allah sai ya dawo da canjin tunani da kuma yankewa cewa ai shiga cikin rundunar Imam Husain [AS],shine matarsa tace masa; “Allah [T] yayi maka za~i.Ina ro}on ka,ka tuna dani wajen kakan Husain [AS] ranar }iyama”.Haka nan zainab ta bada gudummawa mai yawa wajen }arfafa zukatan wa]anda sukayi musharaka  a cikin wannan waki’ar ta karbala,musamman ma mataye da yara a bayan shahadar su Imam Husain [AS].
Daga cikin gudummawar da mata suka bayar a wannan waki’ar ta karbala akwai niyya da kuma azama wajen sadaukar da kai domin taimaka wa Imam Husain [AS].Idan mutum ya bibiyi tarihin wannan waki’ar,zai ga akwai matayen da suka yi yun}urin fafatawa da ma}iya,Imam Husain [AS] yace su koma.Misali wata mata mai suna Ummi wahab,lokacin da mijinta ya fito yana fafatawa da ma}iya itama ta yun}uro domin ta shiga fagen faman a fafata da ita,sai Imam Husain [AS] yace ta koma hema.Yace mata Allah ya saka da alheri.Bayan shahadan mijin nata ta shigo filin daga tana share masa jini,tana ce masa ; “Albishirinka da Aljanna,ina ro}on Allah da ya azurta ka da shahada ya sani danshinka mu tafi tare”.Tana cikin fa]in haka sai Shimr ya bada umarnin a rotsa mata kai,aka ko aiwatar da umarninsa na rotsa kanta.Nan take Allah yayi mata rasuwa.Saboda haka itace farkon matar da aka kashe a cikin wannan waki’ar ta karbala.Shine bayan da mahaifiyar wannan shahidi taga ]anta an kashe,ga matarsa an kashe,ta ]auki makami ta yun}uro domin ta shiga fagen fama ta fafata da ma}iya.Imam Husain [AS] yace mata ta koma.Shine ta koma tana cewa ya Allah kada ka yanke fatana,wato na samun shahada.Sai Imam Husain [AS] yace; “Allah ba zai yanke maki fata ba”.Da dai misalai irin wannan da yawa,wanda ba za’a kawo ba saboda gudun tsawaitawa,wato irin wannan gudummawar da mata suka bayar wa]anda aka ambata dama wa]anda ba’a ambata ba.                                                                              Akwai kuma dauriya da dakewa da sukayi na fuskantar wahalhalu daban daban ta kuma fuskoki daban daban tun daga ranar Ashura har bayan shahadar su Imam Husain [AS] har ya zuwa dawowar su madina.Ga kulasar matsalolin da suka fuskanta tun daga ranar Ashura har zuwa dawowar su madina,sai dai abubuwan suna da sosa rai da kuma ta da hankali.Bayan da aka kashe dukkan sahabban Imam Husain [AS] da kuma Bani Hashim,ya zama yanzu babu wani namiji babba daya rage face Imam zainul Abidin [AS],shi kuma bai da lafiya,da kuma mata da yara,sai Imam Husain [AS] ya tafi domin yayi bankwana dasu.Abu na }arshe daya fa]a wa Imam zainul Abidin [AS] da yayi bankwana dashi shine yace masa; “Ya kai ]ana! Ka isar da sallamata ga shi’ata [wato mabiyana] kace masu,babana an kashe shi yana ba}o.saboda haka kuyi juyayi,kuyi kuka”.Bayan nan ya tafi hema wato tanti nasu zainab [AS] domin yayi bankwana dasu.Ya kira sunansu ]aya bayan ]aya; “Ya Sukaina! Ya Fa]ima! Ya Zainab! Ya Ummul kulsum!” Haka ya kira su dukkan su yace masu “Amincin Allah ya tabbata a gare ku,wannan itace }arshen ha]uwa ta daku”.Wato a wannan gida na duniya.Jin haka nan take dukkan su suka fashe da kuka.Yace masu; “kuyi shirin fuskantar jarabawowi.Amma ku sani Allah [T] zai kiyaye ku,zai kuma kiyaye mutuncinku,kuma zai tseratar daku daga sharrorin na ma}iyanku”.                                     Kuma in muka duba mutum zai ga cewa wannan abin ya tabbata,wato duk da yadda suka kasance a hannun ma}iya masu busassun zukata da kuma yun}urin da Ibn Ziyad yayi na ya kashe zainab [AS],da kuma wanda yazid yayi na ya kashe Imam Sajjad [AS],duk Allah ya kiyaye su, dama yun}urin da wani mutumin sham yayi a fadar yazid na cewa a bashi Fatima ‘yar Husain [AS],shima Allah ya kiyaye.Wahalhalu kam sun sha na yunwa da }ishin ruwa da duka na tafiyarsu daga karbala zuwa sham.Amma kisa da ta~a mutunci,Allah [T] ya tsare kamar yadda Imam Husain ya shaida masu.                                                                                                             }arshen abinda Imam Husain [AS] yace wa zainab [AS] a wannan bankwana shine yace mata; “Ya ‘yar uwata kada kimanta ni a sallar dare [wato sashi cikin addu’a] domin yazo a tarihi cewa Zainab [AS] hatta ranar Ashura da daddare bata bar sallar tahajjud ]inta ba,duk da ko gashi a daren Ashura sun kwana suna ibada,a ranar Ashura kuma ga abubuwan da suka faru,amma duk da haka,haka tayi sallar dare amma a zaune saboda gajiya da yunwa da }ishi.Shine har Imam zainul Abidin [AS] yake tambayar ta dalilin sallar a zaune tace masa; “wallahi }afafuwana basu iya ]auka ta”.Bayan haka Imam Husain [AS] ya fito zai wuce ya duba dama ya duba hagu ba kowa yace; “wa zai kawo min doki na?” Da Zainab [AS] taji haka,ta fito taje ta zo masa da dokinsa [AS],ya hau ya tafi fagen fama.                                                                                  Abubuwan da suka faru ,suka faru marasa da]in ji da karantawada kuma rubutawa,wato na abubuwan da shimr [LA] yayi masa.Can bayan wani lokaci sai ga doki ya dawo zuwa tantin su zainab [AS] ba Imam Husain [AS],wanda abin da yake alamta an kashe Imam Husain [AS].Wannan dokin ainihinsa dokin manzon Allah [S] ne,amma ikon Allah yayi masa tsawon rai har zuwa lokacin, wato bayan shekaru 50 da rasuwar manzon Allah [S] yana raye.Bayan wa]annan la’anannun sun kashe wa]annan bayin Allah sai suka bisu suna ]a]]ebe masu tufafin jikinsu suna rabawa tsakanin su.Haka suka barsu ba tufafi a jikinsu.ya mazo akan cewa kasantuwar Imam Husain [AS] yasan haka zata auku,da zai fita bayan yayi bankwana dasu     Zainab [AS] ya samu tsofaffin tufafi wanda mutum ma ba zai yi sha’awarsu ba yasa.Saboda wannan mummunan aikin da zasu yi.Haka bai ishe su ba,sai suka bi su suka sassare kawukansu daga jikunansu,shima suka raba kawukan tsakanin su.Daga }arshe wanda ya jagoranci ya}in baki ]aya ya basu umarnin dasu hau dawakansu suyi sukuwa akan jikkunan wa]annan bayin Allah!! Haka ko suka aikata wannan mummunan aikin.                                                         Bayan haka sai suka tafi hemomi na mata da yara da suka rage suka kwashe masu kayayyakin su !! Kai hatta ]an kunne na mata da ababen hannu irinsu warwaro basu bari ba.      Wani ma da yaje hemar da Imam Sajjad [AS] yake ciki yana jinya,shimfi]ar da Imam Sajjad [AS] yake kai,ya fisge ya jefar da Imam Sajjad [AS] a }asa.Ana cikin haka sai ga shimr ya zare takobi zai sara wa Imam Sajjad [AS],sai Zainab [AS] ta fa]a kan Imam Sajjad [AS] tace sai dai akashe ta kafin a kashe shi.Nan dai wasu suka bada baki cewa a }yale shi,shine shimr [LA] yace masu ai kun san abinda Ibn Ziyad ya bada umarni akan cewa akashe duk ‘ya’yan Husain [AS].Allah [T] bisa ikonsa ya tsare.                                                                                                                      Bayan sun gama wannan aika aika na kwashe kayayyakin wa]annan matan da kuma yara,sai suka cinna wa tantunan wuta.Shine Zainab [AS] ta samu Imam Sajjad [AS] ta shaida masa  ga abinda mutanen nan sukayi nasa wa hemomi wuta.Meye abinyi ? Imam Sajjad [AS] yace su fita daga cikin hemomin su gudu.Bayan da suka gama wannan aika aika na }one tantuna,Zainab [AS] ta sake tattara wa]annan bayin Allah [T] da yara a waje ]aya.A cikin wannan yanayin ne aka samu yara biyu suka rasu ‘ya’yan khadija ‘yar Imam Ali [AS],sakamakon yunwa da }ishi da kuma firgitar da yara da sukayi.Haka wa]annan bayin Allah suka kasance a filin Allah [T] har wayewar gari.Haka Zainab [AS] ta kasance lokaci bayan lokaci tana bi tana dudduba su.Saboda a wannan rana ta Ashura bayan shahadar su Imam Husain [AS] mafi yawan wahalhalun da wa]annan bayin Allah suka fuskanta,Sayyida Zainab[AS] ce tafi kowa shan wahala a cikinsu,saboda yazo akan cewa sun dake ta ba ka]an ba,don ko duka za’a kaiwa wani cikin mata da yara ita take karewa da jikinta.Haka suka kwana a daren 11  ba abinci,ba ruwa,ba kayansu da suke amfani dashi yau da kullum,duk an }wace.                                                                                                                                                                                                   Bayan haka washegari, wato 11 ga wata bayan zawal na ranar suka sa wa wa]annan bayin Allah sar}o}i suka tasa su gaba zuwa Kufa tare da kawukan Shuhada tsire a masu!! Suka bar jikkunan wa]annan bayin Allah da suka kashe a fili a nan Karbala. A wata ruwaya an ce kwanansu uku a wannan filin, sannan wasu bayin Allah (T) suka zo suka yi jana’izarsu.
ISAR SU ZAINAB KUFA: Lokacin da labari ya iso ga Ibn Ziyad cewa an iso da wa]annan bayin Allah Kufa, sai ya ba da umurnin cewa kawukan Shuhada da Ibn Sa’ad ya aika da su a soke su a masu a ]aga a kuma zagaya da su a kan tituna da kasuwar Kufa tare da wa]annan mata da yara domin mutane su gani.
Bayan an gama kewayawa da su aka kawo su fada wurin Ibn Ziyad maganganu marasa da]in ji da izgili suka gudana daga wurinsa, Zainab (AS) ta mayar masa, shi ne ya fusata wai zai kashe ta. Shi ne wasu na fadar suka ce masa "haba! Ba ka ganin mace ce?" A nan Zainab ta yi jawabi mai tsawo, wanda yake cike da balaga da kuma fasaha.
Bayan wani lokaci aka kama hanya da su zuwa Sham. Haka suka kama hanya da su daga }auye zuwa }auye, birni zuwa birni, har suka isa Sham. A kowane }auye ko birni da suka isa sai a yi yekuwa ga mutane, domin su zo su gan su. Kazalika duk wata ko wani yaro da ya yi kuka sai su dake shi. Abinci kuwa sau ]aya suke ba su a yini a cikin wannan tafiya tasu. Ya zo a kan cewa Zainab (AS) wani lokaci nata abincin takan }ara wa yaran, ita kuma ta ha}ura. Haka suka rika yi masu a hanya har suka isa Sham.
Ya zo a kan cewa sun isa Sham ranar farko ga watan Safar, dubi adadin kwanakin da ke tsakanin ranar Ashura da 1 ga watan Safar? Za ka ga kwanaki 20 ke tsakaninsu. Sa'annan mutum ya yi tunanin matsalolin da wa]annan bayin Allah (S) suka fuskanta a cikin wa]annan kwanakin. Da suka iso Sham sun iske mutane a yanayi na murna da bukuwa na wannan abin da ya faru. Abin nufi a nan shi ne su mutanen Sham suna da bambanci da mutanen Kufa. Mutanen Sham suna da bambancin tunani da kuma asasin abin da suka ginu a kai da mutanen Kufa. Misali mutanen Sham ba su san su waye Ahlul-Baiti (AS) ba, ballantana su san matsayinsu, sa~anin mutanen Kufa su sun san su waye Ahlul Baiti (AS), sun kuma san matsayinsu. Domin Imam Ali (AS) a nan ya zauna har ya zuwa shahadarsa, sa~anin mutanen Sham, Mu’awiyya (LA) ne ya zauna da su, har ya zuwa mutuwarsa. Shi ya sa idan mutum ya yi nazarin jawabai da hu]ubobi wa]anda Zainab, Ummu Khulsum, Fatima ’yar Imam Husain (AS) tare da Imam Zainul Abidin (AS) suka yi a Kufa, zai ga akwai bambanci da wa]anda suka yi a Sham. Kuma ma in mutum ya duba zai ga cewa lokacin da aka shigar da wa]annan bayin Allah (T) garin Kufa, galibin matan, wa]anda suka yi wannan aika-aikan sun fito suna kuka ne sa~anin ko Sham sun samu mutane suna ki]e-}i]e da raye-raye na murna da farin ciki.
Da suka iso Sham abubuwa da yawa munana sun faru gare su, wato tun daga isar su garin har ya zuwa isar su fadar Yazidu. Amma daga baya abubuwa sun canza sakamakon abubuwan da matar Yazid ta yi da kuma bayyana matsayinta kan wannan aika-aika da aka yi, wanda wannan ‘mau}if’ ]in nata ya sa ala dole Yazid ya canza usulubin fuskantar wannan al’amarin. Wannan abin yana da ban mamaki ta wata fuskar, ta wata fuskar kuma babu mamaki. Wato na mau}if ]in matar Yazid. Ya zo a tarihi cewa ita wannan mata ta Yazid sunanta Hindu ’yar Abdullahi ]an Amir, lokacin da aka kashe Babanta sai ta dawo gidan Imam Ali (AS) da zama tana hidima a gidan. Bayan shahadar Imam Ali (AS) sai ta koma gidan Imam Hasan (AS) da zama, kuma ta ci gaba da hidima a gidan. Kamar yadda ya zo a tarihinta takasance ma’abociyar kyau, a kan asasin haka ne Mu’awiyya ya nemi aurenta ga ]ansa Yazidu, aka ba shi. Bayan da aka yi auren ta koma Sham da zama tare da Yazidu. Amma duk da haka lokaci bayan lokaci idan ta ji wasu sun zo daga Madina takan bincika domin ta ji labarin su Imam Hasan da kuma Imam Husain (AS). Lokacin da aka kashe Imam Husain (AS) ba ta da labari. Bayan da aka kawo su Zainab Sham, sai wata mata ta same ta ta ce mata lallai an zo da wasu ribattatun ya}i ko za ta bincika ta ji daga ina aka kawo su. Amma akwai }ishin-}ishin asalin su daga Madina suka fito.
Jin haka matar Yazidu ta ]aukar wa kanta ta je ta bincika da kanta. Ta shirya domin ta tafi sai ta shaida wa Yazidu ga inda za ta je. Jin haka Yazidu hankalinsa ya soma tashi, saboda ya san mau}if ]in matarsa dangane da Ahlul Baiti (AS) don ta zauna gidan. Amma kasantuwar tana da sul]a a kansa, wato bai tsallake maganarta ko kuma abin da take so kamar yadda ya zo a tarihin zamantakewarsu. Saboda haka sai ya }yale ta ta tafi. Saboda haka ta fita tare da ’yan rakiya da masu yi mata hidima. Lokacin da suka kusa isowa inda su Zainab suke, Zainab ta hango ta ta gane ta, Ummi Khulsum na kusa da ita, ta ce mata kin gane waccen matar da take zuwa? Ta ce ba ta gane ta ba. Ta ce; “Hind ’yar Abdullah ce mai yi mana hidima”. Jin haka sai Ummi Khulsum ta sunkuyar da kanta. Haka nan ita ma Zainab ta sunkuyar da kanta. Lokacin da ta iso sai aka aje mata kujera kusa da Zainab take cewa; “Zainab ya na ga kin sunkuyar da kai?” Sai Zainab ba ta amsa mata ba. Sai ta sake tambayar ta cewa; “Daga wane gari aka kawo ku? Zainab ta ce daga Madina. Jin cewa daga Madina. Sai nan take Hind ]in ta sauko daga kujerarta, ta zauna a }asa. Shi ne har Zainab take tambayar ta na ga kin sauko }asa Hind? Ta ce saboda girmama ma’abocin Madina (wato Manzon Allah(S)). Sai Hind ta ce wa Zainab; “Ina so in tambaye ki wani gida a Madina?” Zainab ta ce; “Tambayi abin da kike so”. Ta ce; “Ina tambaya dangane da gidan Ali [an Abi [alib”. Sai Zainab ta ce mata; “Ina kika san gidan Ali?” Jin haka sai Hind ta fashe da kuka ta ce; “Na yi hidima a gidan”. Sai Zainab ta ce mata; “Wa kike tambaya a gidan?” Ta ce; “Ina tambaya dangane da Husain da ’yan uwansa da ’ya’yansa da dai sauran ’ya’yan Ali. Haka nan ina tambayar ki Shugaba ta Zainab da ’yar uwarta Ummi Khulsum”.
Jin haka sai Zainab ta yi kuka, kuka mai yawa. Sai ta ba ta amsa da cewa; “Tambayarki dangane da Husain (AS) ga kansa can gaban Yazid. Dangane da Zainab kuwa ni ce Zainab, wannan kuma ita ce Ummi Khulsum”. Lokacin da matar Yazid ta ji haka, sai ta fashe da kuka tana fa]in “Wa Imamah! Wa Sayyidah!! Wa Husainah!!” Ta ce kaico! Da a ce na makance, gabanin wannan ranar ban ga ’ya’yan Fatima a irin wannan halin ba." Aka ce haka ta dinga dukan kanta har sai da ta suma. Lokacin da ta farfa]o Zainab ta ce mata; “Ki koma gida. Ina ji maki tsaron mijinki Yazid”. Hind ta ce ai ba zan koma gida ba sai tare da ku. Daga nan ta kama hanya kai tsaye sai zuwa wajen Yazid, ta ce masa "yanzu kai ka ba da umurnin a yi wa Hasan haka, kuma a yi masu irin wannan cin mutunci? Shi ne ya yi waje yana ce mata; “Ai Ibn Ziyad duk shi ya aukar da wannan abu na kashe shi, Allah ya tsine masa”, in ji Yazid. Wato don ya kwantar mata da hankali. Shi ne matar tasa ta ce; “To ka sani wallahi ba zan shiga gidanka ba sai tare da su. Jin haka sai Yazid ]in ya ce to, shi ke nan, tana iya shiga da su. Aka shiga da su Zainab gidan aka aje su a sashin aje ba}i. Aka ce a nan suka yi zaman makoki na kwana uku. Daga baya Yazid ya fahimci zaman su hatsari ne a wajensa domin mutanen gidansa da kuma mutanen gari sun soma samun canjin tunani sakamakon bayanin da suka ji daga su Zainab da kuma Imam Zainul Abidin (AS). Shi ne wani na kusa da shi ya ba shi shawarar cewa mafita gare shi ya mai da su Madina. Shi ne ya shirya a mai da su Madina. Saboda wauta irin ta Yazid, da za su tafi sai ya ]auko ku]i mai yawa ya ba su, wai ga wannan kan abubuwan da aka yi maku. Shi ne Ummu Khulsum ta dube shi ta ce lallai Yazid ba ka da kunya, kuma ka cika mai tsaurin ido, ka kashe ]an uwana da Ahlil Baiti ]ina, wai ka ba mu wannan makwafin haka? Suka watsar masa da ku]insa, ba su ]auki komai ba.
Bayan kuma haka aka kama hanya da su zuwa Madina. Da suka iso Madina, inda Zainab ta fara zuwa shi ne Masallacin Manzon Allah (S). Da ta iso Masallacin ta dafa }ofar Masallacin ta ce; “Ya Kakana! Ina yi maka ta’aziyyar ]an uwana Husain. Sannan ta fashe da kuka. Bayan haka ta wuce gida.
Wani tambihi a nan shi ne mutum ya auna ya yi tunani lokacin da su Zainab suka bar Madina tare da Husain (AS) da wane da wane, amma yau ga shi sun dawo Madina birnin Manzon Allah (S), ba Imam Husain (AS), ba wane ba wane. Hatta ita Zainab ’ya’yanta biyu aka kashe. Mutum ya duba ya gani, ya tunanin wa]annan bayin Allah zai kasance lokacin da suka iso Madina suka wuce zuwa gidajensu. Bayan isar ta gida matayen Madina suka cika gidanta. Shi ne Zainab ta yi masu bayani sanka-sankan abubuwan da suka faru a Karbala a Kufa da kuma Sham, matayen suka yi ta kuka. Da suka koma gidajensu suka fa]a wa mazajensu abubuwan da suka faru, wato kamar yadda Zainab ta yi masu bayani, ]an lokaci ka]an labari ya cika Madina, da yawa suka yi wa Yazid tawaye. Shi Gwamnansa na Madina ya aika masa cewa in yana da bu}atar Madina, to ya kori Zainab daga cikinta. Shi ne ya aiko da sa}o a fitar da ita daga cikin Madina. Zainab ta ce ba inda za ta je. Shi ne wasu daga cikin mataye na Bani Hashim suka same ta suka ba ta shawara a kan ta bar Madina. Suka ce Yazid zai iya yin komai, a kan haka yana iya maimaita wata Karbala a nan. Kuma su ba za su yarda a ce za a zo a fitar da ita da }arfi ba suna gani su }yale sai dai duk abin da zai faru ya faru. Jin haka sai Zainab (AS) ta yanke shawarar ta bar Madina zuwa Misira.
Wannan ke nan a ta}aice. Ga mai bu}atar ganin wannan, musamman ma na al’amarin matar Yazid da aka kawo na mau}if ]inta ya duba littafi mai suna Zainabul Kubra minal mahdi ila lahdi na Sayyid Mahammaf Kazim.
Daga }arshe babu abin cewa face “Amincin Allah ya tabbata a gare ki ya Zainab, ranar da aka haife ki, ranar da kika yi wafati da kuma ranar da za a tashe ki.”


No comments:

Post a Comment