Saturday 9 February 2013

Ruhin Azumi da kuma ayyukan watan Ramadan


Azumi kamar sauran ibadodi yana da ~angarori guda biyu,~angaren ruhi,wanda shine ba]ininsa,da kuma ~angaren jiki,wanda shine zahirinsa.Malaman irfani ko tasawwuf sunyi rubuce-rubuce da kuma bayanai dangane da ruhin azumi kamar yadda malaman fi}hu sukayi rubuce-rubuce da bayanai dangane da zahirinsa.Misali,sharu]]an azumi,abubuwan dake inganta shi,ko kuma abubuwan dake ~ata shi,da dai sauransu.
                                                                                                                                                                   Wannan janibi na ruhin azumi,janibi ne wanda yake da gayar muhimmanci wajen saninsa da kuma kiyaye shi,domin yin haka shi zai ba mutum kamalar azumi da kuma samun amsuwarsa wajen Allah [T].Da kuma samun abinda yake shine ma ma}asudin wajabta mana azumin,wato ta}awa,kamar yadda Allah [T] a cikin Alkur’ani mai girma a suratu ba}ara aya ta 183 yake cewa, “Ya ku wa]anda suka yi imani! An wajabta maku azumi,kamar yadda aka wajabta shi ga wa]anda suke gabaninku,domin ku samu ta}awa.” Kuma wannan kiyaye ruhi bai ta}aita  ga azumi ba kawai,a’a,dukkan ayyuka na ibadodi da ayyuka na ]a’a,kai hatta ma ayyuka na mubahat,kamar cin abinci da yin barci,duk ana bu}ata mutum ya kiyaye ruhinsu wajen aikata su.Kamar mutum yaci abinci ko yayi barci da niyyar ya samu }arfin bauta ga Allah [T].Ko kuma a ibadodi,misali halartar da zuciya,khushu’I,ta’azimin Allah [T] a ciki,ko kuma misali a ayyukan ]a’a,kamar Halartar da niyya da kuma iklasi a ciki,da dai sauransu na ruhin wa]annan ayyuka.Ma’anar azumi a lugga ana nufin kamewa,amma a is]ilahi malaman fi}ihu suna cewa kamewa daga wasu abubuwa ayyanannu tun daga ketowar alfijir zuwa fa]uwar rana.Sai dai saboda samun kamalar azumi da kuma tsayuwa da ruhinsa,bai ta}aita ga wannan kamewa ba.Wuce nan,ana son mutum ya kame ga~o~insa  baki ]aya daga sa~a wa Allah [T],wato mutum misali,ya tsare harshensa,idanuwansa,kunnuwansa,hannayensa,}afafuwansa,da dai sauran ga~o~insa  daga abubuwan da suke haram ko makruhi.                                                                                                                                                                 A kan asasin haka ne,malaman irfan ko tasawwuf suka kasa azumi zuwa gida uku.Na farko,akwai azumin awwam,wato na Aamawa.Na biyu,akwai azumi na khusus,wato na za~a~~un bayin Allah [T].Na uku,akwai azumi na khususul-khusus,wato azumin za~a~~un  za~a~~un  bayin Allah [T].                                                                         Na farko shine Azumin kamewa daga abubuwan da aka haramta,kamar ci da sha da makamantansu.Na biyu shine Azumin ga~o~i,wato ga~o~insa na zahiri kamar harshensa,idanuwansa,kunnuwansa da dai sauransu ya kame su daga sa~o.Na uku shine Azumin zuciya,wato mutum ya kame tunaninsa daga tunanin komai in ba Allah [T] ba.Akwai hadisai da dama da aka samo daga Manzon Allah [S] da kuma Ahlulbayt [AS] da suke bayani,suke kuma }arfafa wannan Azumin na ba]ini [wato na ga~o~i da kuma zuciya],wanda yana ]aya daga cikin ruhin Azumi.                                                                  Ga misali na hadisan.An samo daga Imam Sadi} [AS] yace, “Idan kayi azumi,to jinka,ganinka [da wasu ga~o~i daya ambata] suma suyi azumi,kada ranar azuminka ta zama kamar ranar da baka azumi.”Akwai kuma hadisi da aka samo daga Manzon Allah [S] yana cewa, “Wanda ya azumci watan Ramadan bisa imani da kiyayewa,ya kame jinsa,ganinsa,da harshensa daga mutane,to Allah ya kar~i azuminsa,ya kuma gafarta masa abin da ya gabatar na zunubansa da abinda ya jinkirtar.”                                                                A wani hadisi kuma Manzon Allah [S] yana cewa; “Abubuwa biyar na ~ata azumi,}arya,yi da mutum [giba],ha]a husuma,rantsuwar }arya,da kallo na sha’awa”.Amma anan a lura,Azumin da suke ~atawa shine azumin  ~oye ba na bayyane ba.Manzon Allah [S] ya ta~a jin wata mata tana zagin kuyangarta alhali kuma tana azumi,sai Manzon Allah [S] yasa aka kawo abinci,sai yace mata, “ci!”.Sai tace, “Ai ina Azumi”.Sai Manzon Allah [S] yace; “yaya zaki zama mai Azumi alhali kin zagi kuyangarki?”Don haka Azumi ba kawai kamewa daga abinci da abin sha bane.                                                                                A wata hu]uba mai tsawo da Manzon Allah [S] yayi,yayin kamawar watan Ramadan,to a }arshen hu]ubar sai Amirul Mu’uminin Ali [AS] ya mi}e yace, “Ya Manzon Allah [S] mene ne mafificin ayyuka a wannan watan?”Sai Manzon Allah [S] ya amsa dacewa: “ya kai baban hasan! Mafificin ayyuka a wannan watan shine tsantseni [kame kai] daga abubuwa da Allah ya haramta”.Mu duba wannan amsan da Manzon Allah [S] ya bayar,na cewa mafificin aiki a watan Ramadan shine kamewa daga ma’asi,wato sa~o.Ta nan mutum zai fahimci muhimmancin samun tsarkaka na Nafs a zahirance da kuma ba]inance,wato ga~o~i na bayyane da kuma na ~oye,tun gabanin shigar watan Ramadan.Wanda yin haka zai taimaka masa in ya shiga watan Ramadan wajen tsayuwa da ruhin azumi da kuma  samun fa’idodi na ma’anawiyya da zau}i  da halawa da akan samu a cikin watan Azumi.                                                                         Saboda haka idan watan Ramadan ya kama,mutum yayi iyakar ayawarsa tun daga farkon watan har ya zuwa }arshensa, yaga cewa bai sa~a wa Allah [T]ba  da ]aya daga cikin ga~o~insa,Harshensa ya tsare shi daga giba,}arya,da aibanta mutane.Idonsa ya tsare shi daga duk abubuwa da aka haramta masa ya gani,haka nan jinsa,ya tsare shi daga abubuwan da aka haramta masa ji,da dai sauransu.Haka nan ma zuciyarsa ya tsare ta daga dukkan sa~o na zuciya,misali munanan zato ga juna,hassada,riya,ujub da dai sauransu.                                                                                                                                       To,haka ake so mutum ya kiyaye dukkan ga~o~insa.Domin kiyaye ga~o~i shi zai taimaka wa mutum wajen tsayuwa da ayyuka na ibadodi a cikin watan,domin aikata sa~o yana da baibaye mutum daga aikata ayyukan ]a’a,kamar yadda wani yaje ya samu Imam Aliy [AS] yace masa kullum ya kan kwanta da nufin tashi yayi sallar tahajjud,amma bai samun tashi,sai Imam Aliy [AS] yace masa, “Zunubi ne suka da baibaye ka”.Haka nan akwai hadisi da aka samo daga Imam Sadi} [AS] yana cewa, “Lalle mutum zai iya yin }arya guda daya,sanadiyyar haka a haramta masa sallar Tahajjud”.                                              Shi zunubi yana da illoli masu yawan gaske ga mutum idan ya aikata.Daga cikin illolin yana hana amsar addu’ar bawa.Ga shi kuma wannan wata ne na addu’oi,kamar yadda aka samo daga Imam Ba}ir [AS] yana cewa, “Bawa zai iya ro}on Allah Ta’ala wata bu}ata,kuma Allah ya hukunta masa biyan bu}atar,sai bawan ya aikata wani zunubi,sakamakon haka,sai Allah yace wa mala’ika kada ka biya masa bu}ata.” Wato a ta}aice dai zunubi yana sa shamaki na addu’ar bawa ga biyan bu}atarsa.                                Haka nan daga cikin illolin zunubi yakan gusar da ni’imar da Allah [T] yayi wa mutum ta duniya ko ta addini,kamar yadda haka yazo daga Imam Sadi} [AS] cewa, “Allah [T] bai yi wata ni’ima ga bawa ba,sannan ya }wace ta, face sai  saboda zunubi da bawan ya aikata”.                                                                                          A ta}aice shi zunubi guba ce mai kisa ga ruhin ]an Adam.Saboda haka tsare ga~o~i a cikin wannan wata, yana ]aya daga cikin ruhin Azumi,a kasin haka ko,wato rashin tsarewa ]in yana iya janyo ma mutum,wa’iyazu Billahi,ya kasance rabon mutum a azumi ]in shine yunwa da kuma }ishi.kamar yadda haka yazo a wani hadisi cewa,da yawa wani mai azumi rabonsa a ciki shine yunwa da kuma }ishi.Allah ya kiyaye mu.                                                                                                                                                                       Haka nan daga cikin ruhin azumi idan mutum yayi bu]e baki ya kasance a hali na khauf da kuma raja’a.Wato yana tsoron ko Allah [T] ya amshi azuminsa,da kuma fatan Allah [T] ya amsa.Wato hali na tsoro da kuma fata.Haka nan daga cikin ruhin azumi akwai mura}aba,wato shu’urin bawa [jin]cewa Allah [T] yana ganinsa,yana jinsa,ya kuma san abinda ke zuciyarsa.Wannan shu’urin ana son mutum yasa shi a dukkan fagage na rayuwarsa.Ba wai a fagen azumi ba kawai.Da dai sauran abubuwa wa]an]a malaman suluki suka kawo a matsayin ruhin azumi,wanda ba za’a iya kawo su ba saboda gudun tsawaitawa.Amma ga mai bu}atar }arin bayani yana iya duba littafin JAMI’US -SA’ADAT,ko littafin MAHAJJATUL BAIDA’A na faibul-kashaniy.Duka a babin Azumi.                                                                                                                                                                MUHIMMANCIN WATAN RAMADAN
                Sai kuma ~angare na biyu,wato ayyukan da ake aikatawa a watan Ramadan;da farko falalar watan.Wannan wata,wata ne mai yawan falala da kuma albarka.Wata ne wanda a cikinsa Allah [T] yake ‘yanta bayinsa daga wuta fiye da yadda yake ‘yantawa a sauran watannin.Wata ne wanda Allah [T] ke nunnunka ladan ayyukan bayinsa a ciki.Wata ne a cikinsa ake bu]e  }ofofin Aljannah,ake kuma kulle }ofofin wuta.Wata ne wanda a cikinsa ake ]aure shai]anu.Wata ne wanda a cikinsa Allah [T] ke gafarta zunuban bayinsa baki ]aya.Wata ne wanda a cikinsa Allah [T] ke ]aukaka darajojin bayinsa.Wata ne wanda a cikinsa akwai wani dare wanda ibada a cikinsa yafi ibadar  wata dubu.wato daren lailatul }adari.Wata ne wanda a cikinsa Allah [T] yake tsarkake bayinsa yake kusanta su gare shi.Wata ne na samun Ta}awa.Wata ne  wanda yake shine shugaban watanni.A ta}aice  dai wata ne wanda yake cike da alherai da kuma albarkoki,wa]anda ba za’a iya lissafa su ba.                                                                                                                                       AYYUKAN CIKIN WATAN RAMADAN
Sai kuma abinda ya shafi ayyuka a wannan watan na Ramadan.wata ne wanda yake da ayyuka na ibadodi masu yawan gaske,wanda a duk watanni 12 ba watan da ya kai shi ayyuka na ibada.kuma wa]annan  ayyuka da ake aikatawa a cikin shi  wannan watan sun kasu kashi biyu.Na ]aya akwai ayyuka na ‘Aam’,wato wa]anda ake son aikata su tun daga farkon watan har ya zuwa }arshensa.Akwai kuma ayyuka na ‘Khaas’,wato wa]anda ake aikatawa a muhimman ranaku na daren 13,14,15 da daren 19,21,23 na watan.Ga mai bu}atar ganin wa]annan ayyuka na ‘aam’ da kuma ‘khaas’ yana iya komawa ga littafin I}bal na sayyid ibn Dawus,ko zadul ma’ad na Allama majlisi,ko misbahul mutahajjid na shaikh [usy.Ko kuma littafin mafatihul jinan.Saboda haka ana so mutum ya yawaita salloli,karatun Alkur’ani,Azkar,Addu’oi,biya  ziyarori na ma’asumai [AS] da ciyarwa da dai sauransu.                                                               Haka nan kuma ana son mutum ya }ara }aimi wajen ibada,infa}i da kuma mujahada a goman }arshe na watan.Ta yadda mutum yayi wa kansa tarbiyya wajen tsayawa da ire-iren wa]annan ayyuka,bayan watan ramadan ya ]ore a haka har ya zuwa wani watan na ramadan,in Allah [T] ya raya shi,saboda haka ake son kowannenmu ]an uwa ko ‘yar uwa ya kasance yana da wani tsari na ayyukan ibadodi da zasu dinga kusanta shi ga Allah [T],wanda zai tsaya akai yana aikatawa.Daga cikin fa’idodin yin haka shine ko da mutum bai da lafiya ko kuma yayi tafiya, to za’a cigaba da rubuta masa lada kamar ya aikata,sa~anin idan mutum sai jefi-jefi yake yi,wato bai tsaya akai ba.                                                                                 Wa]annan ayyuka malaman Irfani sun kasa su kashi hu]u sune:                                                                                    1.Yaumiyyah [na kullum]                                                                                                                                                             2.Usbu’iyyah [na mako]                                                                                                                                                                               3.Shahariyyah [na wata]                                                                                                                                                             4.Sanawiyyah [na shekara]                                                                                                                                                        Kamar shi wannan watan na Ramadan,Alhamdulillah,a wannan madrasah ta Ahlulbayt [AS]an samu malamai magabata da kuma na yanzu da suka fitar da wa]annan  ayyuka sanka-sanka a cikin littafan.Kyakkyawan misali anan shine Sayyid Ibn [awus.A ayyuka na yaumiyyah yayi littafi mai suna falahus sa’il,a ayyuka na usbu’iyyah yayi littafi mai suna jamalul- usbu’I,a ayyuka na shahariyya yayi littafi mai suna Duru’ul-wa}iya,a  ayyuka na sanawiyyah yayi littafi mai suna I}bal.Sauran littafin na A’amal kamar misbahul mutahajjid,misbah na khaf’amiy, Baladul amin,Dhiya’us Salihin,wa]anda suka rubuta su, sun tattara wa]annan  ~angarori guda hu]u,tare da }arfafa wani akan wa Misali mai misbahul mutahajjid ya }arfafa ne akan ayyukan yaumiyya da kuma na usbu’iyya,mai dhiyaus salihin ya }arfafa ne akan ayyuka na shahriyya,domin ya kawo addu’a wadda aka samo daga Imam Aliy [AS] ana biya ta tun daga farkon kowane wata har ya zuwa }arshensa.Wanda littafan da aka ambata basu kawo ba,sai kuma littafin mafatihul jinan na shaikh Abbas Al-}ummy,wanda yayi kulasar duk wa]annan littafan da aka ambata a sama.In mutum ya bibiyi littafin mafatihul jinan zai ga yana yawan ambaton wa]annan littafan.Wani lokaci ma idan addu’a ta nada tsawo sai yace ka duba littafi kaza,wato cikin wa]anda aka ambata a sama da wasunsu.Ma}asudin  kawo wannan shine sanin yadda littafan suke da kuma abinda kowannensu ya }arfafa,misali shi mai zadul ma’ad baki ]aya  ayyukan sanawiyya ya kawo.                      To,irin wannan ake son ma kowannenmu ya tsara wa kansa wa]annan ayyuka,wato ya tsara wa kansa ayyuka na yaumiyya,usbu’iyya,shahriyya,da kuma sanawiyya.Ya kuma tsayu akai har ya koma ga Allah [T].                                                                                                                                                                                                         Daga }arshe muna ro}on Allah [T] ya kar~a mana ayyukan mu da kuma addu’oinmu,ya kuma sa mu cikin ajin bayinsa da yake ‘yantawa a cikin wannan wata,ya kuma azurta mu da fita wannan watan na Ramadan da ta}awa.Amin.

No comments:

Post a Comment