A darasin daya gabata,an ]anyi
bayani a ta}aice, kuma a dun}ule dangane da ilimin irfani da kuma cewa Akhla}, ~angare ne na shi wannan ilimin irfani,da kuma muhimmancin Akhla} da yadda kyakkyawan Akhla},
yake iya canza ma}iyi ya zama masoyi,kamar yadda aka bada misalai daga Manzon Allah [S] da
kuma Aimma na Ahlul Bait [AS]
,wanda anan ne aka kwana.Sai dai wani ]an
tambihi, a nan shine lokaci bayan lokaci za a ri}a
samun yankewar shi darasin,saboda rubutu na wafati ko shahadar Aimma na Ahlul
Bait [AS] daya kasance, a kowane wata daga cikin wa]annan watannin 12 na musulunci,wanda akan kawo da, unwani ]in ‘ Darussa 12’,alal misali,wata da muke fita na zul}i’idah akwai wafatin Imam Ridah [AS],da
kuma wannan watan na zulhijja,akwai wafatin Imam Ba}ir
[AS],watan gobe kuma wato Muharram akwai
shahadar Imam Husain [AS] da kuma wafatin Imam Zainul Abidin [AS],da dai sauran
watanni, akan asasin wafatin ma’asumai ]in [AS].Saboda haka koda wani lokaci ba’a ga cigaban darasin shi Akhla} ]in ba biye da juna to wannan shine dalilin.
Dawowa ga shi darasin
Akhla},da yake har yanzu ana cikin shimfi]a da kuma
gabatarwa na shi ilimin irfani da kuma muhimmancin Akhlak ne,akwai wata mas’ala
muhimmiya da take da ala}a da ilimin irfani,wannan mas’ala kuwa itace,menene hukuncin yin Ta}lid a cikinsa? Shin wajibi ne ko
kuma bai halatta ba? Kamar yadda aka sani,a fannin ilimin fi}hu,idan mutum shi ba mujtahidi bane,ba kuma muhta]i ba,to wajibi ne ya zamo yana ta}lid da wani daga cikin
mujtahidai.Amma a fannin ilimin A}a’id,wato a}idah,bai halatta yin ta}lidi a ciki ba,to
shifa ilimin irfani,meye matsayin ta}lid
a cikinsa? Wajibi
ne ko bai halatta ba?A wata ma’ana ta daban,yadda za’a iya fahimtar abin da ake
so a fitar a nan,a Madrasah ]in Ahlus Sunna a ~angaren fannin Tasawwuf,malaman Tasawwuf ]in
sun tafi akan cewa dole ne mutum ya zama yana da shaihi ko malami domin
sulukinsa zuwa ga Allah[T].To a Tasawwuf na imamiyyah,mene ne matsayin
haka?dolene sai ya samu shaihi ko malami a sulukinsa zuwa ga Allah [T]? To
wannan shi ake nufi da abinda aka ambata a baya na cewa wajibi ne yin Ta}lidi, a ilimin irfani ko ma bai halatta ba? Amsa anan itace malaman irfan a
madrasah ]in imamiyyah akan wannan mas’ala sun kasu kashi biyu,wasu sun tafi akan
cewa dole ne,wasu kuma sun tafi akan cewa ba dole bane.Daga cikin wadanda suka
tafi akan cewa ba dole bane akwai
Ayyatullah Bahjati,wanda kamar yadda aka sani yana daga cikin manya-manyan
malaman Irfan a madrasah ]in
imamiyyah a wannan zamanin,shekaru kusan uku da suka wuce Allah [T] yayi masa
rasuwa.To,an sha tambayar sa dangane da wannan mas’alar, ga amsar da yake
bayarwa.Ga misalin tambayar da aka yi masa; shin suluki zuwa ga Allah [T] yana bu}atuwa zuwa ga malami,in kuma ba malamin,to,menene abin da mutum zai yi? Ga
amsar daya bayar, “Da sunan Allah ma]aukaki,malaminka shine iliminka,kayi aiki da abin da ka sani,zai isar maka
daga abinda baka sani ba”.Akwai wani daya tambaye shi yake cewa;’nayi niyyar
yin suluki zuwa ga Allah [T],ina son irshadi akan haka,shin wannan aiki yana bu}atuwa zuwa ga malami ko a’a? ga amsar daya bayar, “Da sunan Allah ma]aukaki,malaminka shine iliminka,ka aikata abin da ka sani da kuma lizimtar
haka,zai kasance ya wadatar,domin duk wanda ya aikata abin da ya sani,to,Allah
[T] zai gadar masa a bin da bai sani ba.”Wata tambayar kuma itace,Ni ina son
suluki zuwa ga Allah [T],to wace hanya ce zan bi? Ga amsar, “Da sunan Allah ma]aukaki,in dai mutum da gaske yake yi,to barin sa~o
[zunubi] ya wadatar dashi,a duk tsawon rayuwarsa,ko da kuwa zai rayu shekara dubu ne”.A ta}aice dai wa]annan amsoshi da Ayatullah Bahjati ya bayar yana nuna cewa,idan mutum ya san
ilimin irfani,ya kuma aikata ilimin,ya kuma nisanci zunubi,to wannan zai wadatar
masa.
Sai kuma wa]anda suka tafi
akan muhimmancin samun malami da mutum zai yi ta}lidi da shi a wannan fagen na irfan,misalin
su shine Ayatullah Sayyid Ali Al-}adiy,wanda shima babban malamin irfani ne,ya fitar da urafa’u da yawa a
madrasah ]insa,ga abin da yake cewa,mafi muhimmancin abinda mutum yake bu}ata ga sulukinsa zuwa ga Allah [T]
shine ya samu malami }wararre a ilimin irfan,kuma kamili a sulukinsa da kuma ]abi’unsa’.A wani waje kuma yana
cewa,idan mutum ya }are rabin rayuwarsa wajen neman irin wannan malami kamili na irfan,to
bai yi hasara ba’.A ta}aice dai kuma a dun}ule a fagen ilimin irfan, a madrasah ]in
imamiyyah mutum na da za~i,ko dai ya wadatu da karanta littafan irfan tare da aikatawa,ko kuma il-tizami
da malaman irfani ko kuma ha]a duka biyun,wato domin sulukinsa
zuwa ga Allah [T].A nan ga sunayen wasu daga cikin littafan Akhla} da kuma suluki, da sashen malamai na imamiyyah suka rubuta;1-jami’u-ssa’adat,na
shaikh Muhammad Mahdi Annara}y. 2-Durusun fil Akhla},na Ayatullah Mish-kini. 3-Tazkiyatun-Nafs,na Ayatullah kazim Ha’iriy.
4-Assuluki-ilallahi,na sayyid Abdullahi shubbar.5-Sairu-ilallahi,na ustaz
sayyid Hasan. 6-Tahzibin-Nafs,na shaikh Muhammad kazim.7-kitabun- fil- Akhla}i- wal irfan. 8-A]]ari}u-i
lallahi Ta’ala,na
shaikh Husain Bahraniy. 9-Adabul-Arif,na shaikh ibrahim surar. 10-Al-}isasul irfaniyya,na Ridah Muhammad. 11-Risalatu-li}a’allah,na Ayatullah mirza jawad Attab-riziy.Da dai sauran littafai masu yawa wa]anda malaman imamiyyah suka rubuta a wannan fagen na ilimin irfani,wa]anda ba za a iya kawo su ba saboda
gudun tsawaitawa.
Kamar yadda aka
bayyana a darasin da ya gabata cewa ilimin irfan yana da manyan ~angarori guda
biyu,Akla} da kuma ma’arifa,wato sanin Allah,to ko wanne daga cikin wa]annan ~angarori biyu, akwai hadisai masu yawa da suka zo daga manzon Allah [S]
da kuma Aimma [AS] da suke nuni dangane da matsayi da kuma falalarsa.Alal
misali,ga wasu hadisai da suka zo dangane da muhimmancin Akhla} da kuma matsayinsa a addinin musulunci;. 1-wani mutum yazo wajen
manzon Allah [S] ya zauna gaba gareshi,yace ya Manzon Allah [S] me nene addini? Manzon Allah [S] yace masa kyakkyawan
Akhla}, sai mutumin ya dawo ta hagun Manzon Allah [S] yace,mene ne addini?
Manzon Allah [S] yace masa kyakkyawan Akhla},sai
kuma mutumin ya dawo bayan Manzon Allah [S] ya sake wannan tambayar, me nene addini? Manzon Allah [S]
ya dube shi yace,shin baka fahimta ba,shine kada kayi fushi’. 2-An tambayi Manzon Allah[S] wane aiki
ne yafi falala,yace kyawawan Akhla}. 3-Haka nan an samo hadisi daga Manzon Allah (s) ya ce “Babu
wani abu da ya fi nauyi a mizanin mutum (ma’auni) ranar }iyama fiye da kyekkyawan akhla}.
4. Manzon Allah (S) ya ce; “mafi yawan abin da zai shigar da al’ummata
aljannah , shine ta}’wa da kyakkyawan akhla}.
5. Manzon Allah (S) ya ce; “Mafi soyiwar ku
zuwa gare ni da kuma wa]anda su ka fi kusa da ni a majalisina ranar }iyama, sune wa]anda suka fi kyakkyawar akhla}”.
6. Manzon Allah (S) ya ce; Na hore ku da
kyakkyawan akhla}, domin mai kyakkyawan akhla}, ]an
aljannah ne ba makawa”.
7. Manzon Allah (S) ya ce; “Mai kyakkyawan
akhla} yana da lada irin na mai azumi mai kuma }iyamullaili”.wato
sallar dare
8. Manzon Allah (S) ya ce ; “Allah (T) yana son
mai kyakkyawan akhla}, yana kuma }in mai mummunan akhla}.
9. Manzon Allah (S) ya ce; “Ba za ku iya
yalwatar da mutane da dukiyoyin ku ba, ku yalwatar da su da akhla} ]in ku.
10. Daga Imam sadiq (AS) ya ce; “Mumini bai
gabata ga Allah (T) da wani aiki da yafi soyuwa gare shi, baya ga wanda ya wajabta masa ba, fiye da ya yalwaci
mutane da akhla}
din sa.
11. Haka nan daga Imam sadiq (AS) ya ce; “Duk
wanda ya ke son Allah (T) ya shigar da shi cikin rahamarsa, ya kuma sa shi a aljannarsa,
to ya kyautata akhla} ]in sa.
12. An samo daga Imam Ali (AS) ya ce; “ko da
ba mu }aunar aljannah, bamu kuma tsoron wuta, ba mu fatan samun lada, da kuma
gudun u}uba, duk da haka da ya kama ce mu mu siffantu da kyakkyawan akhla}”.
Da dai
sauran hadisai masu yawa wa]anda aka samo daga Manzon Allah (S) da kuma Aimma na Ahlul bait (AS), wa]anda ba za a iya kawowa ba saboda gudun tsawaitawa.
Sai kuma hadisan da suka zo na akasin
kyakkyawan akhla},wato mummunan akhla}, su ma ga wasu hadisai da suka zo akan
haka da kuma illolin mummnan akhla}.
1.
Manzon Allah (S)ya ce; “Mummunan akhla} yana ~a ta aiki, kamar yadda
kunu ya ke ~ata zuma.
2.
Manzon Allah (S) ya ce;
“kashedinku da mummunan akhla}, domin mummunan akhla}
na kai mutum zuwa
wuta.
3.
An samo daga Imam sadiq ya ce; “Mummunan
akhla}
yana ~ata imani kamar yadda kunu ke ~ata zuma.
4.
Daga Imam sadiq (AS) ya ce; “Duk
wanda ya munana akhla} ]in sa, to, zai azabatar da kansa.
Misali mai yin hassada, in mutum ya duba zai ga cewa ko da wani lokaci zai
kasance ne hali na damuwa da kuma ba}in ciki ga wanda ya ke yiwa hassadar”.
5.
An tambayi Imam Ali (AS) a cikin
mutane wanene ya fi dawwama cikin ba}in ciki, sai ya ce, “wanda ya fisu munin akhla}”.
6.
Haka nan wani hadisi ya zo akan
cewa wanda ya munana akhla} ]in sa, iyalinsa za su }osa da shi. Misali ya zama mai yawan fushi ko rashin ha}uri da kuma kau da kai da dai sauransu. Wannan ke nan, shima a ta}aice, wato hadisan da suke magana dangane da mummunan akhla}.
Bayan haka nan akwai
tambayoyi guda uku.
1.
Yaya za ayi mutum ya san aibobin
nafs ]insa?. Wato ya san ko yana da mummunar akhla} ko
bai da shi.
2.
Wa]anne hanyoyi mutum zai bi domin ya ku~uta, wato ya tsarkaka
daga mummunan akhla}?
3.
Yaya za ayi ya samu ko ya siffanta
da kyawawan akhla}?
Amsoshin wa]annan tambayoyin guda uku sune: tambaya ta farko wato yadda mutum zai san aibin
nafs ]in sa a nan shine, malaman akhla} sun kawo hanyoyi da yawa
da mutum zai bi domin ya san aibin nafs ]in sa, amma ga hanyoyi uku:-
1.
Mutum shi }ashin
kansa ya zauna yayi tunani , ya binciki kansa da kansa, wato muhasaba, ya ga
wane mummunan akhla} yake da shi ko wani aibi na nafs yake da shi.
Misali ya soma da zuciyarsa, shin yana da cututtuka na zuciya, kamar hassad,
riya, ujub ko su’uzzann (mummunan zato) ga juna da dai sauran cututtuka na
zuciya da zai binciki kansa.
Bayan haka sai ya dawo ga ga~o~insa na zahiri kamar harshensa ya binciki kansa yana giba, ko fa]in }arya, ko anna-mimanci (wato ]aukar maganar wannan ya
kai ma wannan), ko kuma suka da aibanta juna. Haka nan kunnansa yana yin
abubuwa da suke haramun ko makaruhi da shi.
Haka nan idanuwansa, yana ganin abubuwan da suke haramun ko makaruhi da
shi. Da dai sauran aibobi na nafs kamar yawan fushi ko rowa da dai makamantansu.
2.
Hanya ta biyu ita ce hanyar
mutane, wato duk wani mummnan akhla} da ka gani ga wani ko
wasu, sai ka tambayi kanka kana da wannan mummnan akhla} ]in ko ba ka da su? Ko kuma abin da ya fito na suka da aibantawa daga ma}iyanka, domin shi ]abi’ar ma}iyi
a kullum shine ya
nemi aibin mutum, domin ya aibanta shi da shi, wato ya soki shi, to mutum shi
sai yayi amfani da wannan damar ya ga aibin, in yana da shi sai yayi }o}ari ya tsarkaka daga aibin. ko kuma ta hanyar masoyin sa, kamar mutum ya ke~an ce ka ya nuna maka aibobinka da kuma matsalolinka, wato dai da nufin
nasiha. To anan sai mutum ya anshi irin wannan nasiha da farin ciki,da ma
godiya ga wanda yayi masa, domin ya taimake ka ne. Misali kamar kai ne,kana cikin jama’a sai wani ya ga tasono ko wata ‘yar
majina a hancin ka, ko wani datti a bayan rigarka, sai ya ]an ke~anceka, yace maka ai ko hancinka akwai
kaza da kaza, ko kuma bayan rigar ka, akwai kaza da kaza, ka duba sai ka ga
haka ne, yadda mutumin ya fa]i. Ka ga ai murna za ka yi,kai masa godiya sannan ka gyara. Ka ga ke nan ya taimake ka.
[an tambihi a nan shine, sau da yawa za ka ga haka zai iya samun mutum,
misali yana da wani aibi da ya ke yi wanda bai dace ba,ko kuma wata mummunar ]abi’a, ai masa nasiha akai, mai makon ya ji da]in
haka a zuciyarsa, akasin haka sai ya
zama bai ji da]i ba. Ko kuma ya dage akan abin
da bai dace ]in ba, wato ya}i
gyara wa, alhali }in gyara aibin nafs ]in, ya fi muni akan wancan misalin da aka bayar na kaza da kaza a hanci,
da kuma datti a taguwarsa, domin da zai mutu, nan take illarsa a wannan gida na
duniya ne kawai. Sa~anin ko aibin nafs ko mummunar akhla}, idan mutum ya mutu bai
gyara ba, to illar haka za ta bishi har lahira, ba wai za ta tsaya a
gidan duniya ba.
Hanya ta uku da mutum zai bi domin ya san
aibobin nafs ]insa, it ace hanyar malami masanin irfan, da kuma baiwa ta kashafi na akhla} ]in mutane. Wato ba wai kawai masani ga akhla} ba,
a’a Allah (T) ya yi masa baiwa da ganin mutane a ruhinsu, wato a ba]inin su, wanda in ya ganka ba sai ka fa]a masa aibin nafs ]in ka ba, zai fa]a maka aibin da kuma matakan da za ka bi na mujahada domin magance
aibin. To, samun irin wannan arifi, shi ya ke da wahala a wannan zamani namu,
ba wai ba a Samuba ba, sam sam.Kuma in
mutum ya bibiyi tarihi na malaman Tasawwuf ,na Ahlus sunna da kuma malaman Irfan na shia,zai ci karo da irin wa]annan bayin Allah, da Allah [T] yayi musu wannan bai wa ta kashafi,misalin
irin wa]annan
bayin Allah masu kashafi na imamiyya a wannan zamani namu, akwai Ayatullahi
Bahajati,wa]anda suka zauna dashi sun tabbatar da haka. Insha Allah a darasi na gaba
za’a kawo amsoshin sauran wa]ancan tambayoyi guda biyu.
No comments:
Post a Comment