Watan jiya,wato
watan jimada sani shine wata wanda aka haifi Imam khumaini a cikinsa,domin an
haife shine ran 20 ga watan jimada sani hijira na da shekara 1321,kuma ranar
haihuwarsa tayi muwafa}a da ranar haihuwar shugaban mataye
baki ]aya,wato
‘yar Manzon Allah [S],sayyidah fa]ima
[SA].
Dama kuma shi jikan sayyidah fa]ima[SA]]in ne,ta hanyar Imam Musa
al-kazim [AS],wanda shi yasa ake ce masa al-musawi.Kuma rasuwarsa ta kasance 3
ga watan yuni 1989,amma a }idayar
Hijiriyya 28 ga watan shawwal ne,1409.Wato yau shekaru 22 kenan cur da
rasuwarsa. To,kasantuwar
wiladarsa da kuma wafatinsa sun yi kusa da juna a wannan }idaya ta Hijiriyya da miladiyyar ya
zamanto zai yi kyau kawo wasu darussa daga rayuwar Imam Khumaini,wanda in muka
aikata su a rayuwarmu zasu kasance insha Allah masu amfani gare mu duniyarmu da
kuma lahirarmu. Koba
komai duk wanda ya bibiyi tarihi da kuma rayuwar Imam Khumaini zai fahimci cewa
lalle Imam Khumaini baiwa ce kuma kyauta ce ta musamman da Allah [T] ya bai wa
alummar musulmi ta wannan zamani,kai hatta ma wa]anda ba musulmi ba,domin da yawansu bayyanar
Imam Khumaini ya canza masu tunani dangane da yadda suke dubar addinin musulunci,wanda sakamakon haka da
yawa sun musulunta. Ashe
kenan sanin tarihi da kuma rayuwarsa wani abu ne wanda yake da gayar
muhimmanci,saboda ma muhimmancinsa za mu
ga malamai da dama da suka zauna dashi,
suka kuma rayu tare da Imam Khumaini,da ma masana daga sassan duniya
daban-daban sun yi rubuce-rubuce na littafai wasu ma mujalladat ne.Misali
littafi mai suna ‘{abasat
min hayatil Imam Khumaini’,wanda mujalladi hu]u ne.Da kuma misali littafi mai suna
‘Rajulun min ahli }um’,wanda babba ne sosai,da dai sauransu;wanda
yanzu haka a birnin }um
akwai wani babban ]akin
karatu [library],wanda duk littafan dake ciki littafai ne wa]anda suke da ala}a da Imam Khumaini,Ko littafan dashi ya
rubuta,ko kuma wa]anda ya’yansa suka rubuta,misali su sayyid mustafa da kuma sayyid Ahmad.Ko kuma
wa]anda wasu malamai suka rubuta dangane da Tarihin sa da
kuma rayuwarsa.Saboda haka
sanin tarihi da kuma rayuwar Imam Khumaini shi zai taimaka wa mutum domin yayi
koyi dashi.Kamar yadda wani malami wanda ya rayu da tare da Imam Khumaini sama
da shekaru 50,wato Ayatullah Nasiriy yake cewa, “na kasance na kan fa]a wa mutane a wasu
lokuta,in kun kasance baku sami yin karatu gaban Imam khumaini ba,to kada ku
haramta wa kanku yin koyi dashi,domin koyi da shi shima wani darasi ne wanda
yake gina mutum ya zama salihi”. Saboda
haka anan insha Allah za’a kawo wani sashen ~angaren rayuwar Imam Khumaini,ba duka
ba.Domin kewaye ~angarori
na rayuwar Imam wani abu ne wanda yake da wahala,koma ace ba zai yiwu ba,kamar
yadda Ayatullah Nasiriy yake cewa, “a iyakar sanina har yanzu wa]anda sukayi
rubuce-rubuce ko bayanai dangane da rayuwar Imam Khumaini basu kewaye duka
ba,balle ba zai ma yiwu har abada a iya kewaye duka ba.” Akan asasin haka ga wa]ansu darussa game
12,amma a ta}aice: 1.NIZAMINSA:Wato tsara alummarsa,Imam khumaini ya kasance komai nasa
a cikin nizami yake,wato lokacin sa ne,alamarin sane,yadda yake tasarrufi da
dukiya,duka a tsare suke.Kuma ya kasance ya na yawan kwa]aitar da ]alibansa muhimmancin su kiyaye nizami na lokutansu
da kuma al’amuransu na yau da kullum,saboda ma gayar nizaminsa da lokaci,ya
kasance agogo ne a gidan sa da kuma ]alibansa dama sauran jama’a,]aya daga cikin masu hidima a gidan Imam
yana cewa,awowi 24 na Imam a tsare suke,ta yadda da sunga yana wani abu sun san
}arfe
kaza kenan;ta yadda da ]ayan
su,da zai yi tafiya zuwa wani gari a tambaye shi mai Imam yake yi yanzu,in ya
duba agogonsa zai ce ya na kaza ne,watau saboda gayar yadda suka kiyaye nizamin
Imam na lokutansa. Kuma
wannan nizami na Imam na lokutan sa, bai ta}aita ga ayyukansa na ibada ko bahasinsa na
ilimi ko kuma ganawarsa da jama’a ba ,a’a hatta barcinsa da cin abincin sa a
cikin nizami suke.Yazo akan cewa,wani lokaci a cikin gida idan an gama abinci
akan zo ace masa an gama abinci akawo masa,sai ya duba agogo,yace saura minti kaza.A
ta}aice dai wa]anda suke tare da Imam khumaini,duk lokacin da suka ga yana aikata wani
abu,ibada ne,karatu ne,cin abinci ne,barci ne,ganawa da ba}i ne,sun san ko }arfe nawa ne,saboda Imam ko wane abu nasa
yana ba shi lokacinsa. Akwai ma wani abin mamaki daya ta~a faruwa lokacin ya na gudun hijira a birnin Najaf,yazo akan cewa tsawon
zaman da yayi a birnin Najaf na shekaru 15,kullum sai ya ziyarci kabarin Imam Aliy
[AS].To, ta hanyar da yake bi zuwa ziyarar,akwai wani shago,watau kanti na sai da
kaya,wanda akwai wani mutum da ya kan zo ya zauna wajen mai kantin suna hira,to
yau da gobe,har ya kiyaye lokacin da Imam yake bi ta wurin,wata rana Imam yazo
zai wuce sai shi wannan mutumin ya duba agogonsa sai yaga sa~anin yadda ya san Imam na wu cewa,sai ya
tambayi mai shagon,}arfe
nawa? Sai mai shagon yace }arfe
kaza.Sai mutumin yace,haba! Na san wannan malamin kullum yana wu cewa nan }arfe kaza,sai ya fahimci
agogonsa ne,ya samu matsala,akwai misalai da dama saboda gudun tsawaitawa,ba
zai yiwu akawo ba. A ta}aice
dai sa’a 24 na Imam a tsare suke. 2.IBADARSA:Imam Khumaini ya kasance mai
yawan ibada,duk wa]anda suka zauna tare da shi sun
tabbatar da haka.Ga misalan wasu daga cikin ibadodinsa. A-Tahajjud
]insa: watau
sallar dare.Yazo akan cewa ya kwashe shekaru saba’in, bai ta~a fashin sallar
tahajjud ba,watau a halin da yake zaune a gida da kuma halin tafiya.Kamar yadda
yazo akan cewa,lokacin da yake dawowa daga gudun hijira watau daga faransa zuwa
iran,to,a cikin jirgin sama lokacin daya saba yin Tahajjud yayi,sai aka ga
kawai yana yi .Kuma ya tsayu da ita a halin tafiya da kuma rashin lafiya.Kamar
yadda yazo,aka ce,wani lokaci an ]auke
shi a motar Asibiti daga Qum zuwa Tehran,da lokacin Tahajjud ]insa yayi sai aka
ga yana yi.Kai hatta ma jinyar da yayi ta rashin lafiyar wafatinsa,bai bar
Tahajjud ]insa
ba! Yazo akan cewa daren }arshe
na rayuwarsa, da isha-ra yayi sallar tahajjud ]insa,wato
saboda raunin da jikinsa yayi na jinya.A lokacin da yake isha-ra na salla ]in,likitocin dasu
ke kula dashi sun ]auka
ko wani abu yake bu}ata.’yar’sa
tace masu yana sallah ne. B-Karatun
Al}ur’aninsa:
Yazo akan cewa a kowane rana Imam khumaini yakan karanta izu Ashirin,wanda yake
nuna cewa a kowane kwana uku yake saukewa,Akwai ma wani a cikin masu yi masa hidima
yana cewa so da yawa mu kanje wajen Imam cikin yini,domin ko yana bu}atar wani abu na
hidima,sai mu same shi yana karatun Al}ur’ani. C-Azkar ]insa:Imam ya
kasance mai yawan zikiri,kamar yadda wanda ya zauna tare dashi mai suna Ansari
Kar-maniy ya bayyana,yace,Imam bai ta~a
gafala daga zikiri ba.Yaci gaba da cewa sau da yawa Imam Khumaini ko tafiya
yake yi zaka ga akwai tasbaha a hannunsa ya na zikiri. D-Addu’oin
sa: Imam ya kasance mai yawan addu’oi,musammam addu’oin ma’asurai,watau wa]anda aka ruwaito
daga ma’asumai [AS].Tabbas haka ne,duk wanda ya bibiyi wasu littafai da Imam ya rubuta,zai ga yana
yawan kwa]aitarwa
da kuma shajja’awa wajen karanta littafan addu’oi.Misali,Ansari kar-maniy yana cewa, “sau da yawa mukan je
wajen Imam a wasu lokuta na sashen dare,sai mu jishi yana biya addu’oi.Har ya
bada misali da Du’a’u khumail.Imam ya kasance yana yawan kwa]aitarwa,na biya
Du’a’u sha’abaniyya.ya kasance yana cewa itace addu’a,wanda baki ]aya A’imma [AS] sun
lizimce ta.Asalin addu’ar,kamar yadda yazo a ruwaya,daga Imam Aliy [AS] ne. E-AZUMINSA:Har
wala yau Imam ya kasance mai yawan azumi na nafila,watau baya ga azumin ramadan
,ya mazo akan cewa baki ]ayan
darare na watan ramadan,ya kan shagaltu da salloli da kuma addu’oi ne.Har ila
yau,yazo akan cewa idan Imam ya ]auki
azumi baya bu]e
baki har sai yayi sallar magariba da kuma isha’i da nafilfilinsu da kuma ta’a}ibat ]insu. 3.KUKANSA:Imam khumaini ya
kasance mai yawan kuka saboda tsoron Allah [T] da kuma shau}i gare shi,har ila yau mai yawan
kuka ne,saboda abubuwan da suka samu Manzon Allah [S] da kuma Ahlul-baiti [AS]
wanda ya bibiyi tarihin rayuwarsa zai ga hakan.Ga misali lokacin Imam ya na
birnin Qum,watau tun gabanin gudun hijira.Wata rana babban ]ansa watau sayyid
mustafa,sai abokinsa ya ziyarce shi,sai ya kwana a gidan.Da tsakar dare,sai shi
wannan ba}on
ya tashi a firgice, saboda yadda yaji sautin kuka na tashi a cikin gidan,yana
tunanin me nene ya faru? Sai ya ta da sayyid mustafa daga barci,domin yaje ya
bincika menene ya faru? Sai sayyid mustafa ya shaida masa cewa ai babansa ne
yake sallar tahajjud yake kuka.Haka nan Hurras dake gadin gidan,sukan fa]i makamancini hakan,cewa duk lokacin da
yake sallar tahajjud su kan ji sautin kuka.Haka nan duk lokacin munasabar zaman
makoki ta shahada ko wafatin ]aya
daga cikin ma’asumai [AS] ya kan yi kuka,kuka mai yawa,musamman zaman makoki na
wafatin Nana fatima [AS] da kuma na Ashura.Wa]anda
suka zauna tare da shi sun ba da shaida cewa,duk lokacin da aka ambaci sunan
Imam Husain [AS],idan Imam Khumain na wajen sai an ga hawaye sun gangaro masa. 4.ILIMINSA:
A wannan fage na ilimi,Imam khumaini ba ma kawai ya }ware
bane a dukkan fannoninsasss,a’a ya yi zurfi a ciki.Babban
hanyar da mutum zai san hakan itace ya bibiyi littafan da ya rubuta a fannoni
daban-daban na ilimin addini,domin Imam khumain ya rubuta littafai da dama akan
fannoni daban daban,misali fannin fiqhu Usul-fiqh Ilimul Rijal,Irfan da dai
sauransu.Akwai ma wani littafi na irfan da ya yi sharhinsa mai suna
Fususul-hikam,wanda wannan littafi ko a malaman irfan,ba kowa yake iya fahimtar
sa ba ballantana ma ya yi sharhi a kai. Ayatullah
shahid mu]ahhari
yana cewa dangane da wannan littafi na fususul hikam,a kowane zamani wa]anda suke iya
fahimtar sa [watau shi littafin] adadinsu bai wuce a }idaya su da yatsu ba.Haka nan fannin
tafsiri na Al}ur’ani,shima
akwai rubuce-rubucensa,da kuma muhadarori akai,duk da kasancewar sashen wasu
surori ne da kuma ayoyi Imam Khumain ya yi tafsirinsu,ba wai dukkan al}ur’ani ba.Da
mutum zai samu irin wa]annan
littafan da suka }unshi
tafsirin sa, ga wasu surori da kuma ayoyi,zai fahimci irin zuzzurfa ilimin da
yake dashi na tafsirin Al}ur’ani,da
kuma tunanin cewa da a ce ya rubuta tafsiri na Al}ur’ani
baki ]aya,to
da Allah [T] ne, ka ]ai
ya san adadin juzu’o’in da zai kasance. Kyakkyawan
misali anan shine mutum ya nemi littafinsa mai suna ‘Tafsirul Ayatil basmala’
na shi Imam khumain.zai ga cewa a tafsirin Bisimillah kawai sai da aka samu
shafi ]ari da
ashirin da ]aya. Haka
nan fannin Hadisi, shima Imam ya rubuta littafi akai,wanda littafi ne sananne,
kuma fitacce mai suna Al’arba’una Hadis;Hadisai 33 suna magana akan akhla},sauran 7 suna
magana akan a}ida.A
ta}aice dai Imam
ya rubuta littafai da dama,wa]anda
ko a yanzu akwai littafai a}alla
guda 45 wa]anda
an buga su,kuma ana samun su a kasuwa,banda wa]anda
ba’a buga suba,ko kuma ana kan bugawa. Haka
nan kuma wani ~angare
da yake da ala}a
da ilimin Imam shine uslubin karantarwarsa,wanda nasa uslubin yana da banbanci,in
an kwatanta dana sauran malamai,kamar yadda wasu da su kayi karatu a wajensa
suka bayyana.Ga misali guda biyu daga cikinsu.shaikh karimi yana cewa,uslubin
karantar war Imam,wani abune wanda yana da ban mamaki kuma mai }ayatarwa.Tsawon
wannan lokaci,kusan shekaru talatin da ‘yan kai,wanda na shafe ina karatu a
gaban malamai masu yawa a hauzozin Qum da najaf ,uslubinsu na karantarwa da na
Imam akwai banbanci.Imam ya kasance idan yana yi mana bayani na mas’aloli awani
fanni na ilimi,ya kan yi wanda ya tattaro duk wani abu da yake da ala}a da
mas’alar,wato bayani shamili kuma zuzzurfa,ta yadda yake,duk wanda yake zaune
yake sauraron darasin,zai wadatu ga komawa ga wasu littafai ko bayanin wasu
malamai domin }arin
bayani.Haka wani da yayi karatu a wajensa mai suna khatim yazdi yana cewa’’Shekaru
goma shabiyar da Imam yayi a najaf,na kasance tare dashi.Akwai wasu ababe da
suka janyo hankalina gare shi.Na farko uslubin karantarwar Imam.Duk da
kasancewar Imam babban malamin falsafane kuma malamin Irfani awannan
zamanin,amma tare da haka in yana yi mana bayani a darussa na fa}hu,zai mana
bayani gam sasshe,kai kace bai san kome ba in ba fi}hu
ba.’’Ya ci gaba da cewa.Domin a fahimci abin da nike nufi ga misali;Idan }wararre a fannin
ilimin falsfa,misali zai yi bayani dangane da mas’aloli na fi}hu ko kuma yayi
tafsirin wasu ayoyi na Al }ur’ani,a
guje za ka ga a cikin bayanansa ya kawo kalmomi na falsafa,amma idan Imam na
bayani dangane da falsafa,to,falsafar kawai za kaji.Haka nan irfan, to irfan ]in kawai za
kaji,haka nan fi}ihu
da dai sauransu,wanda ta}aita
kai acikin fannin ilimi lokacin bayani yana da wahala.’’A ta}aice dai uslubin
karan tarwar Imam a ko wane fanni na ilimi,za a iya siffata shi da cewa’Al
jami’I,Al mani’I,watau wanda ya tattara komai,kuma
ya hana duk wani abin da bai ciki shiga.
5. ZUHUDUNSA
Watau gudun duniyarsa; shi ma wannan wani fage ne, wanda
Imam ya kai mustawa ma]aukakiya
a ciki. Duk wa]anda
suka zauna tare da shi sun tabbatar da haka. Akwai ma fa]in ]ansa
sayyid Ahmad cewa, “ba wai zar~a~~iya
ba ce, na fa]in
wa]anda suka
zauna tare da Imam da suka siffanta da shi da cewa shi abidi ne kuma zahidi,
wato mai ibada kuma mai gudun duniya. Duk wanda ya bibiyi rayuwar Imam sanka-sanka
ta fuskoki daban-daban, zai ga cewa a kwai gudun duniya a ciki.
Akwai abubuwa da dama, idan mutum ya ji ko ya karanta zai ga
abun mamaki sosai. Misali cewa Imam khumain har ya bar duniya bai mallaki gida
da mota ba. Hatta gidan da ya bar duniya
a cikin sa, gida ne wanda ya ke haya a cikinsa, duk da cewa lokacin da aka kama
hayar gidan, masu gidan sun zo wajen Imam,
suka nuna murnarsu da kuma jin da]insu
da kuma godiya ga Allah (T) da ya yi masu wannan babbar ni’ima, suka nuna shi
wannan gida sun bar wa Imam khomain har abada. Imam yace masu, abun da ya ke so
a gurin su shi ne haya, in ko ba haka ba zai sa a bincika a wani waje. Kuma
idan Allah (T) ya azurta mutum da ziyartar gidan, ba wai gida ne wanda ya kai
ya kawo ba, a’a gida ne }arami
wanda da yawa da suka ziyarci gidan, sai da suka zubar da hawaye, saboda yadda
suka ga gidan da kuma kayan da ke ciki. Saboda gudun tsawaitawa, da an kawo
rayuwar Imam sanka-sanka misali abincinsa, tufafinsa, da sauransu.
6. GWAGWARMAYARSA: Abin da ya shafi gwagwarmaya, baki ]aya masoya da ma}iya sun san Imam
khomain a wannan fage na gwagwarmaya da zalunci da azzalumai da tsayawa wajen
kafa hukuma islamiyya da kuma tsayawa wajen kare ta bayan kafuwarta. Kuma akan
haka ya fuskanci jarabobi daban-daban a rayuwarsa, kama tun daga tsangwama ta
fatar baki har zuwa ga ]aurewa
a kurkuku zuwa ga yanke masa hukuncin kisa, da yake wannan sunna ce ilahiyya.
Daga }arshe,
da kashe shi bai yiwu ba, aka kore shi daga }asar,
ya tafi gudun hijira }asan
turkiyya. Da ga nan kuma zuwa ira},
da ga nan kuma zuwa kuwait, wanda su ko kwana ]aya
basu yarda yayi a kuwait ba. Da kuwait ta }i
yarda ya shiga }asar,
ya wuce faransa. Kama-kama dai har Allah (T) ya hukunta dawowar sa }asar iran, hukuma
islamiyya ta kafu }ar}ashin
jagorancin sa. Bayan kafuwar hukuma islamiyya, matsaloli sabbi daban-daban suka taso. Haka Imam ya
kasance cikin gwagwarmaya da matsaloi daban-daban har zuwa rasuwar sa. A ta}aice dai duk wanda
ya bibiyi tarihi da rayuwar Imam
zai ga cewa baki ]aya
rayuwarsa, tun daga farkonta har }arshen
ta, ta gudana ne kan ginshi}ai
guda uku.
1. Neman ilimi da
ilimantarwa.
2. Ibada domin
kusanci zuwa ga Allah (T).
3. Gwagwarmaya
domin kafa hukuma islamiyya da kuma kariya gare ta bayan kafata.
7. YUN{URINSA WAJEN HA[A KAN AL’UMMAR MUSULMI
Ha]a
kan al’ummar musulmi yana daga cikin manya-manyan abunda Imam Khumain ya dinga kwa]aitarwa da kuma }arfafan musulmi a
kai tsawon rayuwarsa, musamman bayan juyin islama da aka yi a Iran. Kan haka ne ma ya ba da
umarnin }ir}iro
da makon ha]in
kai a watan maulidi, wato Rabi’ul- awwal, wanda ake yinsa ko wace shekara daga
12 ga watan zuwa 17 gare shi. Akan gayyato malamai daga sassan duniya
daban-daban, da kuma mabiya mazhabobi daban-daban, wato ahlus-sunna da kuma
shi’a, domin gabatar da jawabai a mako ]in, da nufin
fahimtar da juna da kusantar juna. Har ila yau idan mutum ya bibiyi jawaban
Imam, musamman wa]anda
yake aika wa lokacin aikin hajji, zai ga ya na }arfafa
magana ne akan ha]in
kan al’ummar musulmi da kuma nisantar rarraba.
8. MUJAHADAR SA
Wato fa]a
da zuciyarsa da kuma shai]an
domin samun sul]a,
wato iko akan su, Imam ya kasance mai yawan mujahada. Kuma duk wanda ya bibiyi
tarihinsa da kuma rayuwarsa, zai ga cewa lallai Imam khumain ya samu sul]a akan nafs ]insa da kuma shai]an. Wato shi
yake juya nafs ]insa
da kuma shai]an,
ba su suke juya shi ba, kuma wannan shine babban hadafin mujahada, wato mutum
ya kai matsayin da shi ya ke iko da zuciyarsa da kuma shai]an, ba su suke iko da shi ba, dama
a ce mutum zai nemi littafinsa na
hadisai arba’in, ko ya duba in yana da shi, zai ga hadisi na farko da ya fara
kawowa, shine hadisi wanda yake magana akan jihadin-nafs (ya}ar zuciya). In
mutum ya duba zai ga yadda yayi dogon sharahi kan hadisin, wato bayani
sanka-sanka kan mujahadar nafs. Domin samun iko akan zuciya da shai]an wani abu ne
da yake da gayar mahimmanci, kuma yake da faidoji masu yawa, daga cikin
faidojin, baya ga mutum zai kai matsayi na ubudiyya. Wato ya zama bawa na Allah
(T) ba ya zama bawa na nafs ]insa
ba ko shai]an.Haka
nan kuma zai taimakawa mutum wajen samun iko a tunanin sa, a
lokacin ibadodi, wato ta yadda idan kana sallah, ko karatun al}ur’ani ko ka na
biya addu’o’i ko ziyarori da dai sauran su, tunaninka ba zai je ko ina ba. Dama
wa]annan
tunani-tunanin sukan zo ne ta wajen nafs
da kuma shai]an.
9. AKHLA{ [IN SA
Wato ]abi’o’in
sa. Imam khomain ya kasance mai
kyawawan ]abi’u
ta ko wace fuska. Duk wa]anda suka zauna tare da shi sun tabbatar da haka. Ga misali:
a-
Ha}urinsa, Imam ya
kasance mai yawan ha}uri.
An cutar da shi ta fuskoki daban-daban, a kuma lokuta daban-daban a
rayuwarsa, amma matakin da ya ]auka
shine ha}uri.
Har ma sau da yawa ya kan cewa ]alibansa,
ko da sun ji wani na sukan sa, ko yana aibata shi, to, bai ce su ]auki wani mataki
akai ba na musgunawa ko na ramawa ba.
b-
Tausayinsa, Imam ya kasance mai yawan tausayi ga mutane. Har
ma yazo a kan cewa sau da yawa idan yana kallon talabijin (tv) aka nuna mutane
suna cikin wahala da kuma halin }a}a-ni-ka-yi
na talauci, ciwo ko rashin kwanciyar hankali, sai a ga yana zubar da hawaye
akan haka.
c- Tawali’unsa,Imam ya
kasance mai yawan }as}antar da kai, saboda ma
gayar }as}antar da kai, sau da yawa shi yake yima kansa hidima. Kuma a jawaban sa,
ya kan siffanta kansa a matsayin ]alibi
ko mai hidima. Ya ma zo akan cewa sau da yawa ya kan taimakawa iyalinsa a wasu
ayyuka na cikin gida.
d-
Kyautarsa,
Imam ya kasance mai yawan kyauta da kuma share wa mutane hawaye akan
matsalolin su, idan sun kawo masa, shi ma wannan akwai misali da dama, amma ga
guda ]aya,
lokacin Imam yana najaf, akwai wani da ya samu Imam, ya kawo bu}atar wani da bai
da lafiya, bayan haka kuma yana cikin matsala ta rayuwa. Da Imam ya ji sai ya
kira ]aya daga
cikin ]alibansa
ya shaida masa cewa, in Allah ya kai mu gobe ya zo ya kar~i sa}o
wajansa, ya kai ma mutumin. Wannan abu ya auku da daddare ne bayan sallar
isha’i. Ikon Allah washegari sai labari shahadar babban ]ansa, wato sayyid Mustapha ya zo. Shi
wannan da Imam yace ya zo ya amshi sa}o
da safe, ko da ya doso gidan Imam da safe, sai ya ga cincirindon jama’a. Tun
kafin ya iso sai ya tambaya lafiya?. Sai aka ce masa; Sayyid Mustapha ne ya
rasu. Sai ya ce, “nan take na ]imauta,
gwiwoyina suka yi sanyi, na isa gidan har aka yi jana’izar sayyid Mustapha.
Bayan an dawo Imam na amsar ta’aziyya daga jama’a. Can misalin }arfe tara da minti
goma, sai na ga Imam na kallo na, can sai ya ce min ya maganar jiya? Sai na tsaya
ina tunani, saboda halin ka]uwa
da juyayi da na ke ciki. sai Imam ya ce maganar da na ce ka zo ka amshi sa}o ka kai wa mutumin.
Sai Imam ya shiga ya ]auko sa}o na ku]i da wasu abubuwa ya
ce in kai masa. A cikin wannan abu akwai darussa da dama, ]aya daga ciki shin ne yadda yake Allah (T)
yayi ma babban ]ansa
rasuwa. Amma bai manta da al}awari ba.
10. ALA{ARSA DA ALLAH (T)
Imam khomain ya
kasance yana da gayar ala}antuwa da kuma ]amfaruwa
da Allah (T). Akwai ma lokacin da aka bu}aci ]ansa, wato sayyid Ahmad, da ya yi bayani akan ala}ar Imam da Allah (T).
Shine ya ke cewa, “lallai wannan wani abu ne wanda ba zan iya siffanta shi
ba”. Ya ci gaba da cewa, “ha}i}a
na yi iyaka }o}arina,
na sa du da abokan mahaifina, kuma na tambayi mahaifiyata, dangane da wannan
abu. Dukkan su sunyi ijma’I akan cewa lallai Imam yana da ala}a ta musamman da
Allah (T), kuma yayi fana’i gare shi”. Ya ci gaba da cewa, sau da yawa masu
gudanar da al-amura sukan zo wajen su lokacin matsaloli, ya kan ce masu, kada
suji tsoro Allah (T)na tare da mu. Imam ya kasance mai gayar tawakkali ga Allah
(T), mai gayar ya}ini da kuma si}}a ga Allah (T), mai gayar ikhlasi
da kuma ta’azimi ga Allah, mai gayar so da kuma shau}i
ga Allah (T). A ta}aice
dai ala}ar Imam
da Allah wani abu ne wanda ba za a iya bayani ba, kamar yadda ]ansa sayyid Ahmad
ya fa]a.
11. ALA{ARSA DA MANZON ALLAH[S] DA KUMA AHLUL-BAYT (AS)
Shima
wannan wani faga ne,wanda bayanin sa nada wahala.Baya ga ]abi’antuwa da kuma
siffata da Imam Khumaini yayi,da ]abi’o’i na Manzon Allah da kuma Ahlul-bayt[AS] ya kasance mai kiyaye munasabobi na ranakun
haihuwar su da kuma wafatin su.ya mazo akan cewa,hatta lokacin da yake gudun
hijira a }asar
faransa,ranar da wafatin sayyida Fa]ima[AS] ya
zagayo,sai da ya gabatar da zaman makoki a gidan da ya zauna tare da wa]anda ke zaune dashi a
lokacin.kuma yazo akan cewa tsawon shekaru 15 da yayi a birnin Najaf, lokacin
yana gudun hijira a can,to kullum sai ya ziyarci }abarin Imam Ali[AS].a Akwai ma lokacin da sojoji sukayi
juyin mulki a }asar,watau
a Ira},sai suka sa dokanar hana fita,ga kuma Imam ya saba kullum sai ya ziyarci
Imam Ali[AS] Babban ]ansa wato Sayyid
Mustafa,yana ta tunanin yadda babansa zaiyi a ranar,to lokacin da Imam ya saba
zuwa wannan ziyara,sai yaje ]akinsa bai gan shi ba,da kuma wasu ]akuna na
gidan.Abin mamaki da Sayyid Mustafa ya ]aga kansa sama,sai yaga Imam Khumaini
akan dakin ]in ]akinsa yana tsaye ya fuskanci }abarin Imam Ali[AS]yana biya ziyarar sa.Haka nan kuma Imam
Khumaini ya kasance mai yawan kuka da juyayi na abubuwan da suka samu Ahlul
bayt, musammam ma Imam Husain [AS]domin yazo a tarihin sa cewa duk lokacin da
aka ambaci Imam Husain[AS] a gabansa to sai ya zubar da hawaye.A ta}aice dai Imam Khumain ya
kasance yana da gayar ala}a a zahirance da kuma a ba]inance da Manzon Allah[S] da kuma Ahlul bayt[AS].
12. KARAMOMINSA
Da dama wa]anda
suka zauna tare da Imam khumain, sun yi bayani dangane da karamomi daban-daban
da suka gani wajen Imam. Har ma akwai fa]in
Ayatullahi sadu} da yake cewa, akwai
lokacin da suka yi tafiya da Imam zuwa mash-had. To, a kan hanyarsu ta dawowa,
jami’an tsaron da suke bincike akan hanyar su ka tsaida su, domin yin bincike.
Ya ce, da yake wajen tsakar dare ne, sai ya kasance lokacin sallar tahajjud ]in Imam yayi, ya na
so y yi alwala, amma babu ruwan alwala, saboda sahara ne. ya ce, kawai sai muka
ga gefen mu, ga idon ruwa ya na ~u~~ugowa,
sai Imam yayi alwala. Ayatullahi sadu}
ya ci gaba da cewa bai sani ba, bayan sun bar wurin ruwan ya ci gaba da ~u~~ugowa ko ya
tsaya. Mai bu}atar
ganin haka yana iya duba littafi mai suna “Al-imam }udwa”; watau littafi ne da ya }unshi bayani
daban-daban daga wa]anda
suka zauna tare da Imam khomain. Daga cikin karamomin sa hatta rasuwar sa da
kwanaki gabaninta, Imam ya shaida wa iyalansa, ‘yan’uwansa na jini da wasu da
suke kusa da shi, wannan jinya ba zai tashi ba, zai koma ga Allah (T) ne.
Wannan kenan a ta}aice.
Da fatan wa]annan darussan da aka kawo su amfanar da mu.
Allah (T) ya bamu ikon aiki da su.
No comments:
Post a Comment